Category: Latest News

  • Cinikin Kasar Sin a Watanni 2 Na Farkon Bana Ya Karu Da 18.3% Idan Aka Kwatanta Da Na Shekarar Da Ta Gabata

    [ad_1]

    Tun farkon wannan shekara, cinikin shige da fice na kasar Sin ya ci gaba da tafiya ba tare da tangarda ba tare da samun ci gaba, kuma karfin juriya da kuzarinsa ya kara bayyana.

    A yau Talata hukumar kwastam ta kasar Sin ta bayyana alkaluman cinikin, inda ta nuna cewa, a watanni 2 na farkon wannan shekara, sassa da hukumomi daban-daban sun dauki matakai da himma, kuma kamfanonin masu jarin waje da dama sun yi kokarin tabbatar da samar da kaya, da kuma fadada kasuwanni, yayin da cinikayyar shige da fice ta kasar Sin ta karu da kashi 18.3%, idan aka kwatanta da shekarar da ta gabata, wanda ke nuna kyakkyawan yanayi na shiga wannan shekara.

    Masana sun bayyana cewa, samun “kyakkyawan mafari a bangaren ciniki” a kasar Sin a shekarar 2026, ya samo asali ne sakamakon hadakar dalilai guda 4: Wato farfadowar bukatu a duniya, da bayyanar fa’idodin manufofi a fili, da bayyanar fifikon masana’antu, da kuma karuwar kuzarin kananan hukumomi da daidaikun mutane.

    A lokaci guda kuma, ya kamata a lura da cewa, har yanzu ana fuskantar rashin tabbaci da sauye-sauye, musamman ma karuwar tashe-tashen hankula na yanki a kwanan nan, wanda ke kawo babbar matsala ga tsarin samar da kayayyaki a duniya. Ya kamata a baiwa ciniki tabbaci, ta dogaro da kara inganta kirkire-kirkire, da kuma kokarin tabbatar da kwanciyar hankali a yanayin ciniki da inganta tsarinsa. (Amina Xu)

    [ad_2]

    Source link

  • Ministan Wajen Kasar Sin: Ya Zama Wajibi A Yi Adawa Da Duk Wasu Hare-hare Kan Fararen Hula Da Wuraren Da Ba Na Soji Ba

    [ad_1]

    Ministan harkokin wajen kasar Sin Wang Yi, ya ce ya wajaba a martaba ikon mulkin kai, da tsaro da hurumin yankunan dukkanin kasashen duniya, kuma dole ne a yi adawa da duk wasu hare-hare kan fararen hula, da wuraren da ba na soji ba.

    Wang ya bayyana hakan ne a jiya Litinin, yayin tattaunawa ta wayar tarho da takwaran aikinsa na kasar Bahrain Abdullatif bin Rashid Al Zayani. Inda ya ce abubuwan dake kan gaba, su ne gaggauta dakatar da dauki ba dadi tsakanin rundunonin soji, domin dakile bazuwar tashin hankalin da ake ciki.

    Wang Yi ya kara da cewa, jakadan musamman na gwamnatin kasar Sin dangane da batun gabas ta tsakiya, ya fara ziyartar sassan kasashe masu ruwa da tsaki a yakin, inda nan gaba zai ziyarci Bahrain, kana kasar Sin za ta ci gaba da taka rawar gani wajen kare zaman lafiya da daidaito a yankin Gulf.

    Kazalika, yayin zantawarsa da takwaran aikinsa na kasar Kuwait, Jarrah Jaber Al-Ahmad Al-Sabah duk dai a jiyan, Wang, ya ce babban burin da aka sanya gaba a yanzu, shi ne cimma nasarar dakatar da bude wuta cikin sauri. Ya ce kasar Sin ta gamsu da kiraye-kirayen da kasashen Gulf ke yi, na a komawa teburin shawarwari da tattaunawa. (Saminu Alhassan)

    [ad_2]

    Source link

  • Kotu Ta Ɗage Shari’ar Zargin Ta’addanci Da Mallakar Makamai Kan Malami Da Ɗansa Zuwa Afrilu

    [ad_1]

    Kotun Tarayya da ke Abuja ta ɗage sauraron ƙarar zargin tallafa wa ayyukan ta’addanci da kuma mallakar makamai ba bisa ƙa’ida ba da ake yi wa tsohon Babban Lauyan Tarayya, Abubakar Malami, tare da ɗansa Abdulaziz Malami, zuwa ranar 15 da 16 ga Afrilu.

    Dukkan waɗanda ake ƙara sun halarci kotun lokacin da shari’ar ta zo gaban Mai shari’a Joyce Abdulmalik.

    • Kamfanonin Sin Sun Gudanar Da Taron Bayar Da Tallafi A Masar
    • APC Na Da Gwamnoni 31 Bayan Sauya Sheƙar Gwamnan Zamfara

    A yayin zaman kotun, lauya mai kare gwamnati, Mista Akinlolu Kehinde, SAN, ya sanar da kotun cewa, a ranar Litinin ne aka ba shi umarnin ya karɓi jagorancin shigar da ƙarar, don haka yana buƙatar lokaci domin ya gana da shaidun da za su ba da shaida.

    Ya ce: “Na samu umarnin karɓar jagorancin shigar da ƙarar ne a ranar Litinin, don haka ina buƙatar lokaci domin na tattauna da shaidun. Ina roƙon kotu cikin girmamawa da ta ba mu wani sabon lokaci.”

    Lauyan da ke kare waɗanda ake ƙara, Mista Shuaibu Arua, SAN, bai yi jayayya da buƙatar ɗage shari’ar ba.

    Daga nan sai Mai shari’a Abdulmalik ta amince da buƙatar, tare da ɗage shari’ar zuwa ranar 15 da 16 ga Afrilu domin ci gaba da sauraron shari’ar.

    [ad_2]

    Source link

  • Kafafen Yada Labarai Na Kasashen Waje: Taron Npc Da Cppcc Na Sin Za Su Samar Da Sababbin Damammaki Ga Duniya

    [ad_1]

    Kafafen yada labarai na kasashen waje sun ci gaba da bibiyar yadda taron majalisar wakilan jama’ar Sin NPC da taron majalisar ba da shawara kan harkokin siyasa ta CPPCC ke gudana, kuma suna jinjinawa matakan da Sin ta dauka a fagagen kirkire-kirkire da fadada bude kofa ga ketare, inda suke ganin hakan zai samar da sababbin damammaki ga duniya.

    Gidan rediyon kasa na Kenya ya wallafa wani labari a shafukansa na yanar gizo ya nuna cewa, a bana wadannan manyan taruka 2 sun fitar da wata alama a fili, wato kasuwar Sin a bude take. A ganin Kenya, ta hanyar yin hadin gwiwa da Sin, za ta iya inganta ababen more rayuwa, da kara ingancin kayayyaki da kuma kara kimar kayayyakin a duniya. Lamarin da zai kawo karin guraben ayyukan yi ga al’ummar Kenya, da karin kudaden shiga da kuma kwanciyar hankali.

    Tashar Afirka ta gidan talabijin na BRICS na kasar Afirka ta Kudu ta ci gaba da watsa labarai kan ayyuka da dama na manyan taruka 2 na kasar Sin kai tsaye, inda take taimakawa masu kallo fahimtar yanayin ci gaban hadin gwiwar Sin da kasashe masu tasowa. (Amina Xu)

    [ad_2]

    Source link

  • Tinubu Da Shettima Sun Yi Buɗa-Baki Da Sarakuna Da Malaman Addini A Villa

    [ad_1]

    Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu tare da Mataimakinsa Kashim Shettima sun yi buɗa-bakin azumin watan Ramadan tare da sarakuna da kuma shugabannin addinai a Banquet Hall na Fadar Shugaban Ƙasa da ke Villa, Abuja.

    Taron buɗa-bakin wanda ya gudana a ranar Litinin ya haɗa manyan shugabannin gargajiya da malaman addini daga sassa daban-daban na ƙasar, inda suka taru domin yin addu’o’i da kuma ƙarfafa haɗin kai a tsakanin al’umma.

    Wannan taro na daga cikin al’adun da fadar shugaban ƙasa ke yi a watan Ramadan, inda ake haɗa shugabanni da masu ruwa da tsaki domin tattauna muhimman batutuwa da suka shafi zaman lafiya da ci gaban ƙasa.

    [ad_2]

    Source link

  • Kamfanonin Sin Sun Gudanar Da Taron Bayar Da Tallafi A Masar

    [ad_1]

    Kungiyar ‘yan kasuwan kasar Sin da ke Masar da kungiyar Orman ta Masar sun gudanar da wani taron ba da tallafi cikin hadin gwiwa a jihar Giza jiya Litinin, don taimaka wa iyalai mabukata a kasar ta Masar.

    A cewar Zhang Yaqiang, babban jami’i kuma mataimakin jakada a ofishin jakadancin kasar Sin da ke kasar Masar, gangamin tallafin da aka yi na bana ya samar da kudin Masar fam miliyan 3, kwatankwacin dalar Amurka 56,800, don tallafa wa iyalai mabukata a kasar, kana daga fara shirya taron zuwa yanzu, an taimaka wa dubun dubatan iyalai a fadin kasar..

    Taron ba da tallafin ya zama wani muhimmin dandali na sada zumunci, da tuntubar juna, da kuma hadin gwiwa tsakanin Sin da Masar, kamar yadda Zhang ya bayyana. (Mai fassara: Abdulrazaq Yahuza Jere)

    [ad_2]

    Source link

  • Da dumidumi-  Barayin Daji Sun Auka wa Jikamshi Da Maraicen Nan

    [ad_1]



    Da dumidumi-  Barayin Daji Sun Auka wa Jikamshi Da Maraicen Yau

    Yanzu haka Barayin Daji na cin karensu ba babbaka a garin Jikamshi hedikwatar Karamar Hukumar Jikamshi ta Jihar Katsina.

    Wata majiya mai tushe daga garin na Jikamshi ta tabbatar da cewa, Barayin da suka shigo garin tun wajen karfe 6 na yamma dauke da muggan makamai har ya zuwa yanzu suna cikin garin suna harbin duk wanda suka ci karo da shi a waje.

    Majiyar ta tabbatar da cewa, sun harbi mutane da dama wadanda kuma aka kasa kai su asibiti saboda kowa gudun ransa.

    Labarin da ya sa kowa ya koma cikin gida ya boye. Wanda ta kai har ya zuwa yanzu da yawan mutanen garin basu yi buda bakin azumin da ke a bakinsu ba.

    Majiyar ta tabbatar da cewa, har ya zuwa yanzu dai babu alamun wani dauki daga hukumomin tsaro.


    [ad_2]

    Source link

  • Dimokuradiyyar Dake Shafar Kowa a Sin Ingantaccen Karfi Ne Na Ingiza Shirin Raya Ci Gaban Sin Da Zamantakewar Al’umma Na Shekaru Biyar-Biyar Karo Na 15

    [ad_1]

    Taron shekara-shekara na NPC da na CPPCC na Sin, muhimmiyar taga ce ta fahimtar yadda ake zamanintar da al’ummar Sinawa, da aiwatar da dimokuradiyya mai shafar kowa da kowa. Ta hanyar wannan muhimmin dandalin, wakilai da ‘yan majalisar bayar da shawara suna gabatar da shawarwari masu kyau, suna sa karin ra’ayoyi daga jama’a su kai ga shugabanni masu yanke shawara kai tsaye, sannan sun zama manyan manufofin kasar, wanda ke nuna karfin dimokuradiyyar irin ta Sin dake shafar kowa da kowa.

    Ma’aunin Edelman Trust Barometer da aka buga ya nuna cewa, amincewar jama’ar Sin da gwamnati, da kamfanoni da sauransu ya ci gaba da zama na farko a cikin kasashen da aka yi nazari a kai, kuma kyakkyawan fatansu game da nan gaba ya tsaya a matsayin na farko a duniya. Masana na ganin cewa, nasarar aiwatar da dimokuradiyya irinta kasar Sin, ba wai kawai ya ba da kariya a bangaren tsare-tsare ga aikin zamanintar da jama’a ba, har ma ya samar da misali mai amfani ga yawancin kasashe masu tasowa, don bullo da tsari irin nasu na dimokuradiyya, da ya dace da yanayin kasarsu, ya kuma wadatar da yanayin siyasar bil’adama.

    Shirin raya ci gaban Sin da zamantakewar al’ummar na shekaru biyar-biyar karo na 15 ya fara aiki a wannan shekara da muke ciki, kuma Sin ta shiga sabon tafarki na zamanintar da al’umma. Tsarin aiwatar da dimokuradiyyar dake shafar kowa da kowa zai ta kara kuzari a cikin aikin zamanintar da al’umma, kuma zai kawo karin haske da damammaki ga duniya. (Amina Xu)

    [ad_2]

    Source link

  • Dukiyar Elon Musk ta kai dala biliyan 839 — Forbes

    [ad_1]



    Fitaccen attajirin duniya, Elon Musk, ya zama mutum mafi arziki da aka taɓa samu a tarihi, yayin da dukiyarsa ta kai kimanin dala biliyan 839, kamar yadda mujallar Forbes ta bayyana a sabuwar ƙididdiga ta jerin attajiran duniya da ta fitar.

    Rahoton ya ce Musk ne ya sake zama lamba daya karo na biyu a jere a jerin Forbes World’s Billionaires, bayan da dukiyarsa ta ƙaru da kusan dala biliyan 500 cikin watanni 12 da suka gabata.

    An ce hauhawar darajar kamfanoninsa na Tesla da SpaceX, wadda ke shirin shiga kasuwar hada-hadar hannayen jari a 2026, ne suka taimaka wajen ƙaruwar dukiyarsa.

    Forbes ta ce Musk shi ne mutum na farko a tarihi da dukiyarsa ta haura dala biliyan 800, kuma yana kan hanya ta zama mutum na farko da dukiyarsa za ta kai dala tiriliyan guda.

    Rahoton ya kuma nuna cewa yawan attajirai a duniya ya kai mutum 3,428, yayin da jimillar dukiyarsu ta kai dala tiriliyan 20.1 — mafi girma da aka taɓa samu.


    [ad_2]

    Source link

  • Matatar Man Fetur Ta Dangote Ta Rage Farashin Man Fetur Da Dizal

    [ad_1]

    Matatar Man Fetur ta Dangote ta rage farashin man fetur da gas (AGO), wanda hakan ke nuna raguwar farashi na farko bayan karuwar farashi da aka samu a ‘yan kwanakin nan.

    A cewar sabon rahoton farashin matatar da aka fitar a ranar 10 ga Maris, 2026, an rage farashin mai da N100 inda ya dawo N1,075 a kowace lita, wanda yake a baya akan N1,175 a kowace lita.

    Bugu da ƙari, an rage farashin dizal zuwa N1,430 a kowace lita, wanda ke nuna cewa, an samu ragowar N190 daga farashin farko na N1,620 a kowace lita.

    [ad_2]

    Source link