Category: Latest News

  • Majalisar CPPCC Ta Kasar Sin Ta Kammala Taronta Na Shekara

    [ad_1]

    Da safiyar yau Laraba aka rufe taro na 4 na majalisar bayar da shawara kan harkokin siyasa ta kasar Sin (CPPCC).

    Shugaban kasar Sin Xi Jinping da sauran shugabannin kasar da na Jam’iyyar Kwaminis ta Sin, sun halarci taron da ya gudana a babban dakin taron jama’a dake birnin Beijing.

    Kuma yayin taron, an amince da kuduri kan rahoton aiki na kwamitin dindindin na majalisar CPPCC da kuduri kan rahoto game da yadda aka tafiyar da shawarwarin siyasa da aka bayar tun bayan taron majalisar da ya gabata, da rahoto kan nazarin sabbin shawarwari da kuma kudurin siyasa kan taron na 4 na majalisar CPPCC na 14.

    Kana shugaban majalisar CPPCC Wang Huning, ya gabatar da jawabi yayin taron. (FMM)

    [ad_2]

    Source link

  • Ramadan: Lokutan Buda-Baki Da Sahur Na Azumi Na 22

    [ad_1]

    Mota Sahur (Fajr/Imsak) Iftar (Maghrib)
    Abuja 05:12 AM 06:59 PM
    Idan 05:07 AM 06:53 PM
    Kano 05:08 na safe 06:58 PM
    Kaduna 05:12 AM 07:01 PM
    Legas 05:26 AM 07:18 PM
    Maiduguri 05:03 AM 06:38 PM
    Sokoto 05:25 AM 07:11 PM
    Fatakwal 05:17 AM 07:00 PM

    [ad_2]

    Source link

  • NDLEA Ta Kama Mutane 56 A Wuraren Hada-hadar Miyagun Ƙwayoyi A Kano

    [ad_1]

    Hukumar hana sha da fataucin miyagun ƙwayoyi ta ƙasa, NDLEA, reshen Kano, ta kai samame a wurare da dama da ake sayar da miyagun ƙwayoyi a Jihar Kano, inda ta kama mutane akalla 56, ciki har da wani da ake zargi da hannu a kisan kai da aka yi shekaru biyar da suka gabata.

    A cewar hukumar, an samu nasarar kama mutanen ne bayan wani samame na kwanaki uku a jere, wanda aka gudanar mai taken “Operation Ramadan Mubarak” da ake ci gaba da yi.

    Jami’in Hulɗa da Jama’a na rundunar, Sadiq Muhammad Maigatari, ne ya tabbatar da kama waɗanda ake zargin a cikin wata sanarwa da ya fitar ranar Laraba.

    Ya ce, “Hukumar NDLEA ta kai samame wurare da dama da ake hada-hadar miyagun ƙwayoyi a faɗin Jihar Kano, tare da kama mutane 56, ciki har da wani da ake zargi da hannu a wani kisan kai da ya faru shekaru biyar da suka gabata, bayan gudanar da aiki na tsawon kwanaki uku a jere a ƙarƙashin shirin ‘Operation Ramadan Mubarak’.”

    [ad_2]

    Source link

  • Kotu ta yanke wa wani hukuncin kisa kan kashe tsohuwar matarsa a Gombe

    [ad_1]



    Babbar Kotun Jihar Gombe, ta yanke wa wani matashi mai shekaru 25, Hassan Mohammed, hukuncin kisa ta hanyar rataya bayan ta same shi da laifin kashe tsohuwar matarsa, Halima Sadiya Adamu.

    Hassan Mohammed ɗan asalin ƙauyen Falangaya ne, da ke Ƙaramar Hukumar Dukku a Jihar Gombe.

    Mai shari’a Abdulhamid Mohammed Yakubu na Babbar Kotun Jihar Gombe mai lamba ta biyu ne, ya yanke hukuncin bayan kotun ta tabbatar da laifin kisan.

    Kotun ta ce laifin ya saɓa da sashe na 221 na Dokar Penal Code.

    A cewar ɓangaren gwamnati, lamarin ya faru ne a ranar 25 ga watan Maris, 2025, da misalin ƙarfe 1 na rana.

    An zargi Hassan da kai wa tsohuwar matarsa hari da wuƙa tare da yanka a wuya, bayan ta ƙi amincewa ta sake aurensa.

    Daraktan shari’a na gwamnati (DPP), Barrista Abubakar Jungudo, wanda ya jagoranci ɓangaren masu gabatar da ƙara a madadin gwamnatin jihar, ya ce laifin ya saɓa wa Sashe na 221 na Dokar Penal Code.

    Lokacin da aka karanta masa tuhume-tuhumen da ake masa, wanda ake zargin ya musanta aikata laifin.

    A yayin shari’ar, ɓangaren gwamnati sun gabatar da shaidu shida da suka bayar da shaida kan abin da suka gani lokacin da lamarin ya faru.

    Haka kuma kotu ta karbi wukar da ake zargin an yi amfani da ita wajen aikata laifin a matsayin hujja.

    Lauyan wanda ake tuhuma, Barrista Habib Alkali, ya yi wa shaidun gwamnati tambayoyi domin tantance shaidarsu.

    Daga bisani ɓangaren kariya ya gabatar da wanda ake tuhuma a matsayin shaidarsa ɗaya tilo, inda ya sake musanta aikata laifin.

    Sai dai ɓangaren gwamnati sun sake yi masa tambayoyi.

    A hukuncin da ya yanke, Mai shari’a Yakubu, ya ce ɓangaren gwamnati sun tabbatar da laifin kisan kai a kan wanda ake tuhuma ba tare da wata shakka ba.

    Saboda haka kotun ta same shi da laifin kashe tsohuwar matarsa ta hanyar yanka mata wuya da wuƙa.

    Sannan ta yanke masa hukuncin kisa ta hanyar rataya kamar yadda Sashe na 221 na Dokar Penal Code ya tanada.


    [ad_2]

    Source link

  • Ɗan majalisar Kano ya fice daga NNPP zuwa APC

    [ad_1]



    Ɗan Majalisar Wakilai mai wakiltar mazaɓar Dala a Jihar Kano, Aliyu Sani Madakin Gini, ya fice daga jam’iyyar NNPP tare da komawa APC.

    Madakin Gini, wanda shi ne Mataimakin Shugaban Marasa Rinjaye a majalisar wakilai, ya sanar da hakan cikin wata wasiƙa mai ɗauke da kwanan wata 10 ga watan Maris, 2026.

    Ya aike wasiƙar ga shugaban jam’iyyar NNPP na Unguwar Yalwa da ke Ƙaramar Hukumar Dala ta Jihar Kano.

    A cikin wasiƙar, ɗan majalisar ya ce ya ɗauki wannan mataki ne bayan tuntuɓar abokan siyasarsa da magoya bayansa a faɗin Kano, musamman a gundumomi 12 da ke mazaɓar Dala.

    Ya ce matakin cikin bai zo masa da sauƙi ba, la’akari da irin sadaukarwar da ya yi wa jam’iyyar da kuma tafiyar siyasar Kwankwasiyya.

    Sai dai ya ce rikice-rikicen cikin gida a jam’iyyar ne suka sa ya yanke shawarar ficewa.

    A cewarsa, jam’iyyar ta rabu gida biyu, inda ɓangare ɗaya ke goyon bayan Boniface Aniebonam, yayin da wani ɓangaren kuma ke goyon bayan tsohon gwamnan Jihar Kano, Rabiu Musa Kwankwaso.

    Madakin Gini, ya ce wannan dalili ne ya sa ya yanke shawarar ficewa daga jam’iyyar shi da magoya bayansa.

    Ya ce: “Ina so na sanar da ku a hukumance cewa daga wannan lokaci ni da magoya bayana kun fice daga jam’iyyar NNPP.”

    Ya kuma ƙara da cewa ya koma jam’iyyar APC tare da magoya bayansa a faɗin Jihar Kano.

    Idan ba a manta ba, Madakin Gini ya jima da nesanta kansa daga tafiyar Kwankwasiyya, lamarin da ya kai ya daina sanya jan hula wadda ita ce alamar ƙungiyar.


    [ad_2]

    Source link

  • Aminu Ado ya sanar da ’yan sanda shirin gudanar da hawan salla a Kano

    [ad_1]



    Fadar Sarkin Kano na 15, Aminu Ado Bayero, ta sanar da rundunar ’Yan Sandan Jihar Kano, cewa ta fara shirye-shiryen gudanar da bukukuwan Hawan Salla idan an kammala azumin watan Ramadan.

    Wannan na cikin wata wasiƙa mai ɗauke da kwanan wata 7 ga watan Maris, 2026, wadda aka aike wa Kwamishinan ’Yan Sandan jihar, Ibrahim Adamu Bakori.

    Fadar ta ce za a gudanar da bukukuwan hawan sallar daga fadar sarkin da ke unguwar Nassarawa a Kano.

    Sakataren Sarkin, Abdullahi Haruna Kwaru ne, ya sanya wa wasiƙar hannu, inda ya ce Sarkin da mambobin majalisar masarautar sun amince da shirye-shiryen bukukuwan.

    A cewar fadar, bukukuwan sallar za su haɗa da hawan hawan salla, hawan Daushe, hawan Nassarawa, da hawan Fanisau

    Fadar ta ce an tura wa jami’an tsaro cikakken bayanai game da ranakun gudanarwa, lokaci da wuraren da za a yi hawan.

    Ta kuma ce Sarkin da majalisar masarautar suna godiya ga jami’an tsaro kan haɗin gwiwar da suke bayarwa wajen tabbatar da zaman lafiya da tsaro a Jihar Kano.

    Fadar ta kuma yi addu’ar samun zaman lafiya da nasarar gudanar da bukukuwan salla a faɗin jihar.


    [ad_2]

    Source link

  • Ana Ganin Yanayi Na Tabbas Wajen Tarukan Majalisun Kasar Sin

    [ad_1]

    Bisa wani rahoton da aka gabatar da shi wajen dandalin tattaunawar tattalin arziki na duniya, an ce yanayin rashin tabbas daya ne daga cikin manyan abubuwan da suke haifar da barazana ga al’ummun kasashe daban daban a shekarar 2026 da muke ciki. Sai dai a nata bangare, kasar Sin tana samar da cikakken yanayi na tabbas, da ake iya ganin alamarsa wajen tarukan shekara-shekara na majalisun NPC da CPPCC, wato hukumar koli ta kafa dokoki da hukumar ba da shawara kan harkokin siyasa na kasar, dake gudana a birnin Beijing yanzu.

    Yanayin tabbas da aka ga alamarsa a tarukan majalisun, da farko dai ya shafi ci gaban tattalin arzikin kasar Sin mai inganci.

    A yanzu haka, ’yan majalisun NPC da CPPCC na kasar Sin suna tantance daftarin shirin raya kasar na shekaru 5 masu zuwa, wato tsakanin shekarar 2026 da ta 2030, wanda ya shafi zamanantar da tsarin masana’antu, da inganta kayayyakin more rayuwar jama’a, da raya kimiyya da fasaha, da kirkiro sabbin fasahohi, gami da sauya zuwa salon raya tattalin arziki mai kare muhallin halittu. Wannan shiri ya sa ake hasashen kyakkyawar makomar kasar, musamman ma ta la’akari da kwarewarta ta fuskar aiwatar da shirin da ta tsara, wadda ta tabbatar da karuwar tattalin arzikin kasar ta kaso 5.4% cikin wa’adin shirinta na raya kasa na 2021-2025.

    Na biyu kuma, yanayi na tabbas da aka gano wajen tarukan majalisun NPC da CPPCC na kasar Sin ya shafi zumuntar da ke tsakanin Sin da Afirka.

    A gefen tarukan majalisun NPC da CPPCC na wannan karo, ministan harkokin wajen kasar Sin Wang Yi, ya kira taron manema labaru don ayyana manufofin kasar a fannin harkar diplomasiyya, inda Fortune Abang, wakilin kamfanin dillancin labarai na kasar Najeriya (NAN), ya yi tambaya kan yanayin huldar dake tsakanin Sin da Afirka a shekarar 2026. Yayin da ya amsa tambayar, Wang Yi ya nuna kaunar da Sinawa suke da ita ga abokansu ’yan Afirka, inda ya ambaci al’adar ministan wajen kasar Sin ta mai da nahiyar Afirka wurin kaddamar da ziyara ta farko a duk wata sabuwar shekara, da tarihin kasar Sin na ba da tallafi ga kasashen Afirka, da yadda shugaban kasar Sin Xi Jinping ke dora muhimmanci kan raya huldar dake tsakanin bangarorin 2.

    Sa’an nan, fanni na 3 da yanayin tabbas da tarukan majalisun NPC da CPPCC suka nuna ya shafa, shi ne yunkurin Sin da Afirka na neman samun ci gaba na bai daya.

    Shahararren shehun malami na kasar Najeriya, Charles Onunaiju, ya bayyana a cikin wata makalar da ya rubuta a kwanan nan cewa, yadda kasar Sin ke aiwatar da shirinta na raya kasa zai haifar da dimbin damammakin raya tattalin arziki ga kasashen Afirka, musamman ma ta la’akari da manufar kasar ta yafe wa kasashe 53 dake nahiyar Afirka harajin kwastam. Ya ce da manufar, gami da niyyar gwamnatin kasar Sin ta sa kaimi ga bangaren sayayya a cikin gidanta, za a ba kasashen Afirka damar fitar da karin kayayyaki, wanda hakan zai taimaka ga bunkasa masana’antu a kasashen Afirka.

    Kana a nasa bangare, wani shehun malami dan kasar Kenya mai suna Stephen Ndegwa, ya bayyana cikin wata makalarsa cewa, kasar Sin ta samu nasara a fannin raya harkar samar da kayayyaki masu fasahohin zamani, wadanda ke taimakawa yunkurin kare muhallin halittu a kasashe daban daban. Hakan ya ba kasashen Afirka da ke da wasu ma’adinai masu muhimmanci a fannin masana’antu masu kare muhalli damar shiga a dama da su, a ayyukan sarrafa ma’adinai, da hada kayayyaki daban daban. (Bello Wang)

    [ad_2]

    Source link

  • Kwastam ta kama kayan haɗa bam a Kwara

    [ad_1]



    Hukumar Kwastam a Jihar Kwara, ta kama kayayyaki da dama da ake zargin an shigo da su ba bisa ƙa’ida ba, ciki har da waɗanda ake amfani da su wajen haɗa abubuwan fashewa.

    Muƙaddashin Kwantirolan hukumar a jihar, DC Najeem Akanmu Ogundeyi ne, ya bayyana hakan yayin da yake nuna kayayyakin da aka kama a Ilorin.

    Ya ce kayayyakin da aka kama sun haɗa da na’urori 222 da ake zargin ana amfani da su wajen haɗa abubuwan fashewa, buhun shinkafar ƙasar waje guda 1,107, motoci 14 da kuma jarkar man fetur guda 317.

    Sauran kayayyakin sun haɗa da buhun sinadarin lithium guda 120 da aka haƙo ba bisa ƙa’ida ba, kayayyakin gwanjo, tayoyi da kuma sukari da aka shigo da su daga ƙasashen waje.

    Hukumar ta ce jimillar kuɗin harajin kayayyakin ya kai Naira miliyan 478,171,315.

    Ogundeyi, ya ce hukumar ta samu nasarar kama kayayyakin ne sakamakon bayanan sirri da kuma haɗin gwiwa da sauran jami’an tsaro.

    Ya ce: “Kun san abin da ake yi da waɗannan na’urorin? Duk jami’an tsaro da ke nan sun san ana amfani da su wajen haɗa abubuwan fashewa, shi ya sa muka daƙile shigowarsu.”

    Kwanturulan ya kuma ce hana shigo da shinkafa daga waje wata manufa ce ta Gwamnatin Tarayya domin ƙarfafa noma a  cikin gida da kuma samar da ayyukan yi.

    Ya ƙara da cewa: “Duk da gargaɗin da ake yi akai-akai, wasu na ci gaba da karya dokokin gwamnati. Amma haɗin gwiwar jami’an tsaro da bayanan sirri na taimaka mana wajen daƙile irin waɗannan laifuka.”

    Ya kuma buƙaci ’yan kasuwa da al’ummomin da ke kan iyaka su guji yin fasa-ƙauri, su rungumi kasuwanci na gaskiya domin bunƙasa tattalin arziƙin ƙasa.


    [ad_2]

    Source link

  • Rikicin Gabas Ta Tsakiya: Gwamnatin Tarayya Ta Fara Kwaso ‘Yan Nijeriya Daga Iran

    [ad_1]

    Gwamnatin Tarayya ta fara kwashe ‘yan Nijeriya da ke zaune a ƙasar Iran waɗanda suka nuna cewa suna son a dawo da su gida.

    An fara fitar da su ta kan iyakar Iran zuwa ƙasar Armenia domin tabbatar da tsaron lafiyarsu yayin da rikici ke ci gaba da ƙamari a yankin Gabas ta Tsakiya.

    • Kotu A Norway Ta Ɗaure Ɗan Wasan Nijeriya Kan Zargin Aikata Fyaɗe
    • Saudiyya Ta Rage Samar Da Man Fetur Saboda Matsalar Jigila A Hormuz

    Shugabar Hukumar ‘Yan Nijeriya Mazauna Ƙasashen Waje (NiDCOM), Abike Dabiri-Erewa ce, ta bayyana hakan a wani saƙo da ta wallafa a shafinta na X, a ranar Talata.

    Ta ce kawo yanzu babu wani ɗan Nijeriya da rikicin ya shafa a Iran.

    Ta kuma ƙara da cewa jami’an ofishin jakadancin Nijeriya suna kan iyakar Iran da Armenia domin karɓar ‘yan Nijeriya da taimaka musu su tsallaka iyakar zuwa waje mafi aminci.

    Dangane da dawo da su gida ta jirgin sama, Dabiri-Erewa ta ce a halin yanzu sararin samaniyar yankin ba shi da tsaro.

    Duk da haka, ta tabbatar wa ‘yan Nijeriya da ke Gabas ta Tsakiya cewa Gwamnatin Tarayya na shirye-shiryen kwaso su da zarar an samu damar hakan.

    Ta ce: “Kwanaki biyu da suka wuce an samu jirgi daga Haɗaɗɗiyar Daular Larabawa zuwa Legas kafin daga bisani wani hari ya sa aka rufe sararin samaniyar.”

    Ta kuma ƙara da cewa: “Da zarar an buɗe sararin samaniyar, tawagar Gwamnatin Tarayya da ta ƙunshi jami’ai daga ma’aikatu daban-daban za su fara aikin kwaso ‘yan Nijeriya zuwa gida.”

    Matakin na zuwa ne bayan rikicin da aka fara tun a ranar 28 ga watan Fabrairu, bayan harin da Amurka da Isra’ila suka kai wa Iran.

    [ad_2]

    Source link

  • Minista ya gayyaci hafsoshin tsaro saboda yawaitar hare-hare

    [ad_1]



    Ministan Tsaro, Janar Christopher Musa (mai ritaya), ya gayyaci dukkanin shugabannin rundunonin sojoji taro saboda yawaitar hare-haren da ake kai wa sansanonin sojoji a yankin Arewa maso Gabas.

    An gudanar da taron ne a hedikwatar Ma’aikatar Tsaro da ke Abuja.

    Waɗanda suka halarci taron sun haɗa da Babban Hafsan Tsaro, Janar Olufemi Oluyede, da Hafsan Sojin Ƙasa, Laftanar Janar Waidi Shaibu.

    Sauran sun haɗa da Hafsan Sojin Sama, Air Marshal Sunday Aneke, da Hafsan Sojin Ruwa, Vice Admiral Idi Abass, da kuma wakilai daga Hukumar Leƙen Asiri ta Ƙasa (NIA), da sauran su.

    Aminiya ta ruwaito yadda a baya-bayan nan ’yan ta’adda sun kashe aƙalla kwamandojin rundunar sojoji uku masu muƙamin Laftanar-Kanal a Jihar Borno.

    Baya ga waɗannan kwamandoji da aka kashe, wasu sojoji da dama ma sun rasa rayukansu.

    Haka kuma ’yan ta’addan sun sace ɗaruruwan mutane a wasu hare-hare da suka kai a baya-bayan nan.

    Da yake magana game da taron, Ministan Tsaron ya ce sun amince za su sake duba dabarun da ake amfani da su wajen yaƙi da ’yan ta’adda.

    Ya ce: “Mun san cewa an yi asara a ɓangarenmu, amma asarar ta fi yawa a ɓangaren ’yan ta’adda,” in ji shi.


    [ad_2]

    Source link