Category: Latest News

  • APC Na Da Gwamnoni 31 Bayan Sauya Sheƙar Gwamnan Zamfara

    [ad_1]

    Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya fice daga jam’iyyar PDP tare da komawa APC.

    Mai taimaka masa kan harkokin yaɗa labarai, Nuhu Anka ne, ya tabbatar da hakan cikin wata sanarwa da ya fitar ranar Litinin.

    • Yaƙin Amurka Da Iran Na Iya Tura Farashin Litar Fetur Zuwa N2,000 A Nijeriya – PETROAN
    • Majalisar Dattawa Za Ta Gayyaci Kyari Kan Zargin Giɓin Kuɗi Har Naira Tiriliyan 210 A NNPCL

    Sanarwar ta ce gwamna ya ɗauki wannan mataki ne bayan tuntuɓar shugabannin siyasa da magoya bayansa a jihar.

    Ta kuma bayyana cewa ya bar PDP ne saboda rikicin shugabanci da saɓani da ke ci gaba da addabar jam’iyyar.

    Da wannan sauya sheƙar, yawan gwamnoni na jam’iyyar APC a faɗin Najeriya ya kai 31.

    Wannan na zuwa ne kwanaki kaɗan bayan gwamnan Jihar Adamawa, Ahmadu Fintiri, shi ma ya sauya sheƙa daga PDP zuwa APC.

    Sauya sheƙar Lawal zuwa APC zai taimaka wajen ƙara haɗin kai da gwamnatin tarayya, tare da bunƙasa tsaro da ci gaban Jihar Zamfara.

    [ad_2]

    Source link

  • SAHUR (Falalarsa Da Fa’idojinsa) Na 21

    [ad_1]

    Fa’idar Sahur

    1. Yin sahur koyi ne da annabi Muhammad (Sallallahu alaihi wa alihi wa sallam), kuma malamai sun yi ijma’i a kan mustahabbi ne yinsa kamar yadda Ibnul Munzir da Imamu Annawawi suka naƙalto.

    2. Yin sahur saɓa wa Yahudu da Nasara ne, domin su ba sa yin sahur a azuminsu kamar yadda Muslim da Abu Dawud Tirmizi da Nasa’i suka ruwaito.

    • Darussa Daga Ramadan Na 9: Danne Fushi Da Nutsuwa A Ramalana
    • Ramadan: Lokutan Buda-Baki Da Sahur Na Azumi Na 10

    3. Sahur albarka ne ga mai yinsa kamar yadda hadisi ya gabata.

    4. Sahur yana samar da karfi ga mai azumi wajen yin ibada, da kuma ƙaruwar nishadi, da kuma tunkuɗe mummunar dabi’a da yunwa take haifarwa. Kuma a lokacin yinsa sahur, mutum yana samun dama ya yi sadaƙa ga almajiri ko kuma su ci tare. kuma yana sa mutum ya yi zikiri da addu’a, domin lokacin ne da ake karbar addu’a… “kamar yadda Hafiz Ibnu Hajar ya bayyana a littafinsa Fathul Bari (4/496) da malaminsa Ibnu Mulaƙƙin a cikim  al’I’ilamu (5/187)

    5. Samun salati daga Allah da mala’ikunsa.

    Allah ya datar da mu ga koyi da Manzon Allah (Sallallahu alaihi wa alihi wa sallam) a cikin al’amuranmu baki daya.

    [ad_2]

    Source link

  • Sin Za Ta Ci Gaba Da Samar Da Sababbin Damammaki Ga Kasashe Masu Tasowa Ta Hanyar Ci Gabanta Mai Inganci

    [ad_1]

    An gudanar da taron karawa juna sani kan ci gaba mai dorewa da hakkin tattalin arziki, zamantakewa da al’adu a taron kasa da kasa na kwamiti mai kula da hakkin dan Adam karo na 61 na MDD a ranar 5 ga watan nan. Mataimakiyar shugaban tawagar Sin a taron kasa da kasa na kwmamiti mai kula da hakkin dan Adam karo na 61 na MDD Li Xiaomei, ta halarci taron kuma ta bayyana ra’ayi da matsayar kasar Sin.

    Li Xiaomei ta nuna cewa, shawarar ci gaban duniya da Sin ta gabatar ta sanya samar da kudaden ci gaba a matsayin muhimmin fagen hadin gwiwa, kuma shawarar ta riga ta tattara sama da dala biliyan 23, don tallafawa ci gaba da bunkasar kasashe masu tasowa.

    Kazalika, Sin ta gabatar da kudurori kan hakkin tattalin arziki, da zamantakewa da al’adu, da kuma hakkin ci gaba don inganta hakkin dan Adam a kwamitin, matakin da ya ingiza karfin hadin gwiwar da zai amfani mabambantan bangarori. Har ila yau, Sin ta raba ra’ayoyi da ci gaban da ta samu na kare hakkin dan Adam, da kuma gina sababbin dandaloli don horar da kwararrun ma’aikata, da gina makamar aiki a kasashe masu tasowa.

    Li Xiaomei ta kara da cewa, bangaren Sin yana fatan samar da sababbin damammaki ga kasashe masu tasowa ta hanyar ci gabanta mai inganci, ta yadda za ta inganta hakkin ci gaba, da hakkin tattalin arziki, da kuma zamantakewa da al’adu da sauran hakkokin bil’adama, ba tare da barin kowa a baya ba. (Amina Xu)

    [ad_2]

    Source link

  • Sin Za Ta Inganta Sufuri Mai Amfani Da Fasahohin Zamani Da Makamashi Mai Tsafta

    [ad_1]

    Ministan sufuri Liu Wei ya bayyana a yau Litinin cewa, kasar Sin za ta sa kaimi ga inganta sashen sufuri mai amfani da fasahohin zamani da sauyawa zuwa makamashi mara gurbata muhalli a cikin shirin shekaru biyar-biyar karo na 15 da za a aiwatar tsakanin 2026 zuwa 2030.

    Liu ya fada a gefen taron shekara-shekara na majalisar wakilan jama’ar kasar Sin cewa, a cikin shekaru 5 masu zuwa, kasar za ta sa kaimi ga yin amfani da fasahar kirkirarriyar basira a sashen sufuri, da yin kokari wajen habaka amfani da fasahohin zamani a manyan hanyoyin mota, da tashoshin jiragen ruwa, da fiton kayayyaki.

    Har ila yau, kasar za ta kuma karfafa bunkasa yankuna da tashohin sufuri masu karancin fitar da hayaki mai gurbata muhalli, a wani bangare na kokarin habaka ci gaban sufuri mai karancin fitar da hayaki mai gurbata muhalli, kana Liu ya kara da cewa, kasar Sin za ta kara yin amfani da kayayyakin sufuri masu amfani da makamashi mai tsafta kamar motocin sabbin makamashi da jiragen ruwa a tsakanin wannan lokacin. (Mai fassara: Abdulrazaq Yahuza Jere)

    [ad_2]

    Source link

  • Yaƙin Amurka Da Iran Na Iya Tura Farashin Litar Fetur Zuwa N2,000 A Nijeriya – PETROAN

    [ad_1]

    Ƙungiyar masu gidajen sayar da man fetur ta yi gargaɗin cewa farashin litar fetur a Nijeriya na iya kaiwa kusan ₦2,000 idan rikicin da ke tsakanin Amurka da Iran ya ci gaba da dagula samar da man fetur a duniya.

    Shugaban ƙungiyar na ƙasa, Billy Gillis-Harry, ya bayyana haka a wani taro da aka gudanar a Fatakwal, inda ya gabatar da jawabi kan batun tsaron makamashi. Ya ce yaƙin da ya haɗa da Israel, Amurka da Iran na tura farashin mai a kasuwar duniya sama.

    • Kamfanin Matatar Man Fetur Na Dangote Ya Rage Farashin Mai Zuwa ₦774
    • Matatar Dangote Ta Sake Ƙara Farashin Fetur Zuwa ₦1,175

    A wata sanarwa da jami’in hulɗa da jama’a na PETROAN, Joseph Obele, ya sanya wa hannu, ƙungiyar ta ce hare-haren jiragen sama marasa matuƙi da makamai masu linzami a yankin na barazana ga manyan hanyoyin jigilar mai da muhimman kayayyakin mai, abin da ke haifar da rashin tabbas a kasuwar duniya.

    Ƙungiyar ta ce kafin rikicin, ana sayar da fetur kusan N774 a lita, amma yanzu farashin ya haura N1,000, wanda ya nuna ƙarin kusan kashi 30 cikin ɗari. Haka kuma farashin dizal ya tashi daga kusan N950 zuwa sama da N1,400 a lita.

    Shugaban PETROAN ya ƙara da cewa idan rikicin ya ci gaba, farashin fetur na iya kusantar N2,000 a lita, yayin da dizal kuma zai iya kai kusan N3,000, lamarin da zai ƙara tsananta matsin tattalin arziƙin ga ‘yan kasuwa da al’umma a Nijeriya.

    [ad_2]

    Source link

  • An Yi Zama Na Biyu Na Taron Majalisar Wakilan Jama’ar Kasar Sin

    [ad_1]

    A yau Litinin, aka yi zama na 2 na taro na 4 na majalisar wakilan jama’ar kasar Sin (NPC) ta 14.

    Shugaban kasar Sin Xi Jinping da sauran shugabannin kasar da na Jam’iyyar Kwaminis ta kasar Sin ne suka halarci taron.

    Yayin zaman, shugaban kwamitin dindindin na majalisar wakilan jama’ar Zhao Leji, ya gabatar da rahoton aikin kwamitinsa

    Shi ma shugaban hukumar koli mai karbar korafe-korafen jama’a Ying Yong, ya gabatar da rahoton aiki na hukumar, wanda ya bayyana cewa, adadin mutanen da aka yanke wa hukunci kan laifukan da suka shafi cin zarafin kananan yara ya ragu da kaso 2.2 bisa dari, yayin da adadin yaran da aka yanke wa hukunci bayan aikata laifuka, ya ragu da kaso 9.8 bisa dari.

    A rahoton da ya gabatar ga majalisar, shugaban kotun koli na kasar Zhang Jun, ya ce tsarin shari’a ta kasar Sin ba ta lamunci cin zarafin yara ba ko kadan. Ya ce a shekarar 2025, an kammla sauraron kararraki 40,000 da suka shafi zarafin yara, adadin da ya ragu da kaso 1.8 bisa dari kan mizanin shekara-shekara, kana kuma an yanke wa mutane 44,000 hukunci.

    A cewar rahoton kotun kolin, a bara, jimilar kararraki 25,000 na laifukan da suka shafi kafar intanet aka kammala sauraro, adadin da ya ragu da kaso 62 kan mizanin shekara-shekara, kana an yanke wa mutane 38,000 hukunci.

    Har ila yau a shekarar 2025, kotunan kasar Sin sun kammala sauraron kararraki 36,000 kamar na cin hanci da rashawa wadanda suka shafi ma’aikatan gwamnati, adadin da ya karu da kaso 22.4 kan mizanin shekara-shekara.

    Shi kuwa rahoton kwamitin dindindin na majalisar NPC ya bayyana cewa, domin karfafa dokokin da suka shafi tattalin arziki, ya zartar da dokar kyautata wa bangarori masu zaman kansu, wadda ta zayyana ka’idojin rashin nuna wariya da tabbatar da takara cikin adalci da ba da kariya da samar da ci gaba na bai daya.

    Haka kuma, ya sake bitar dokar da ta shafi harkokin teku da ta warware sabani da ta cinikayya da kasa da kasa, ta yadda za su yi daidai da dokokin kasa da kasa da kuma kara kyautata manufar bude kofa ta kasar Sin.

    A cewar rahoton, domin inganta dokar yaki da cin hanci ta kasa, kasar Sin za ta yi doka kan yaki da cin hanci tsakanin kasa da kasa. Bugu da kari, za ta inganta tsara dokokin da suka shafi kadarorin gwamnati, a matsayin wani bangare na kokarin samar da tattalin arziki irin na gurguzu mai matukar inganci. (FMM)

    [ad_2]

    Source link

  • A gaggauta sakin ’yan Najeriya 42 da aka kama a Mozambique — NiDCOM

    [ad_1]



    Hukumar ’Yan Najeriya Mazauna Ƙasashen Waje (NiDCOM) ta buƙaci mahukuntan ƙasar Mozambique su gaggauta sakin ’yan Najeriya 42 da aka kama a ƙasar ba tare da bayyana takamaiman laifin da suka aikata ba.

    Shugabar hukumar, Abike Dabiri-Erewa, ta bayyana damuwa kan lamarin, tana mai cewa kama ’yan Najeriya ba tare da tuhuma ba abin takaici ne kuma ya kamata a sake su ko kuma a gurfanar da su a gaban kotu idan sun aikata wani laifi.

    A wata sanarwa da kakakin NiDCOM, Abdur-Rahman Balogun, ya fitar a Abuja ranar Lahadi, Dabiri-Erewa ta ce abin damuwa ne yadda aka kama ’yan Najeriya kaɗai a yayin wani samame da aka kai a wata kasuwar sayar da kayan gyaran motoci.

    Ta ce rahotanni sun nuna cewa an bar ’yan kasuwa na wasu ƙasashe da ke wurin, yayin da aka kama ’yan Najeriya kaɗai, lamarin da ta ce na iya nuna wariya ko nuna ƙyama ga ’yan ƙasar.

    “Abin takaici ne a ji cewa ’yan Najeriya kaɗai aka je aka kama,” in ji ta. “Idan har sun karya doka, ya kamata mahukunta su gurfanar da su a gaban kotu.”

    NiDCOM ta kuma ce bayanan da ta samu sun nuna cewa waɗanda aka kama suna zaune a Mozambique bisa ƙa’ida, kuma babu wata tuhuma da Ofishin Jakadancin Najeriya ya samu a kansu.

    “Kamen ’yan Najeriya kaɗai da aka yi farat ɗaya yana nuni da cewa an yi kamen ne saboda nuna ƙyama ko wariya ga ’yan ƙasar Nijeriya,” in ji Dabiri-Erewa.

    Hukumar ta kuma ambato rahotannin da ke cewa an doki wasu daga cikinsu lokacin kamen, an kwashe musu kayayyakinsu, sannan wasu sun kamu da rashin lafiya a gidan yari kuma suna buƙatar kulawar likitoci.

    Dabiri-Erewa ta buƙaci mahukuntan Mozambique su tabbatar da tsaro da lafiyar ’yan Najeriyar da aka tsare yayin da ake ƙoƙarin warware matsalar.


    [ad_2]

    Source link

  • Darussa Daga Ramadan Na 16: Amfani Da Dama Kafin Ta Wuce

    [ad_1]

    A cikin watan Ramalana muna koyon darasi mai girma, watau amfani da dama kafin ta kuɓuce. Domin dama idan ta shuɗe, ba lallai ta dawo da irin yanayinta ba. Lokaci kamar gajimare ne, yana wucewa ba tare da tsayawa ba.

    Allah Maɗaukaki Ya tuna mana da ƙimar lokaci a cikin ayoyin azumi, inda Ya ce a cikin Suratul Baƙara aya ta (184): “Waɗansu kwanaki ne ƙididdigaggu” Watau Ramalana ba wata ba ne mai dawwama; kwanaki ne kaɗan, masu ƙidaya, masu iyaka. Wannan kalma ta ‘ƙididdigaggu’ tana tunasar da mu cewa duk wata dama da Allah Ya ba mu tana da iyaka. Idan muka yi sakaci da ita, za ta shuɗe kamar ba ta taɓa zuwa ba.

    • Darussa Daga Ramadan Na 14: Yawaita Kyauta Da Ihsani A Ramalana
    • Darussa Daga Ramadan Na 13: Tsayuwar Dare

    Ramalana yana koya mana yadda za mu daraja lokaci. Yana koya mana cewa yini guda na iya zama hanyar samun gafara, dare guda na iya zama sanadin tsira, kuma awa guda na iya sauya makomar rayuwa.

    Idan muka san cewa kwanakin Ramalana ƙalilan ne, za mu yi ƙoƙari mu cika su da alheri. Za mu nisanci ɓata lokaci a kan abin da ba ya amfanar da mu. Za mu fahimci cewa jinkiri da sakaci su ne manyan maƙiyan nasara.

    Wannan darasi bai tsaya a kan Ramalana kaɗai ba. Rayuwarmu gaba ɗaya ‘kwanaki ne ƙididdigaggu’ Shekaru suna wucewa, ƙuruciya tana gushewa, ƙarfi yana raguwa. Duk wanda ya fahimci haka, to zai yi gaggawar cika rayuwarsa da ayyukan da za su amfane shi a duniya da Lahira.

    Ramalana wata dama ce ta sabunta rayuwa. Idan muka iya amfani da kwanakin nan yadda ya kamata, za su zama hujja a gare mu, ba hujja a kanmu ba. Saboda haka, mu riƙe kowace rana a matsayin baiwa a gare mu. Mu riƙe kowane dare a matsayin wata dama ce babba a tare da mu. Kada mu bari lokutanmu su tafi a iska. Domin idan dama ta wuce, ba za ta dawo da irin darajarta ba.

    Allah Ya taimake mu wajen amfani da lokutanmu cikin abin da zai amfane mu, Ya sa kwanakinmu su zama masu albarka, Ya kuma ba mu kyakkyawan ƙarshe. Amin.

    [ad_2]

    Source link

  • Kamfanonin Kasa Da Kasa Sun Nuna Gamsuwa Da Dimbin Damarmakin Da Kasuwar Kasar Sin Ta Samar

    [ad_1]

    A yayin taron NPC da na CPPCC, muhimman tsare-tsare da sabbin kalmomi a cikin rahoton aikin gwamnati, sun zama muhimmiyar taga ga kamfanonin kasashen waje ta kallon kasar Sin, tare da tsara shirinsu a nan kasar Sin.

    Babban jami’in kamfanin Yihai Kerry Arawana Holdings Co. Ltd Tu Changming ya bayyana cewa, rahoton aikin gwamnatin ya gabatar da bukatar gina babbar kasuwar Sin mai karfi a cikin gidanta, da kara nauyin aljihun jama’a, tare da bunkasa tattalin arziki. Wannan yana nufin cewa, kasuwar cin abinci, da ta man girki za ta ci gaba da girma, kuma bukatun jama’a za su canza daga cika ciki zuwa cin abinci mai kyau da lafiya. Wannan ya yi daidai da tsarin dukkannin sassan kamfanonin.

    Shi kuwa shugaban kamfanin Sanofi na babban yankin Sin Shi Wang, cewa ya yi saurin kashe kudaden bincike a Sin ya yi matukar karuwa, inda yawan kudaden da ake kashewa a wannan bangare ya karu sosai. Ya ce fiye da kashi 90% na muhimman kayayyakin da kamfanin ke samarwa a duniya, kasuwar Sin da sauran kasuwannin duniya suna gwada su da yin bincike kan su tare da kamfanin. Kazalika, jami’in ya yi fatan kamfanin zai shiga aikin kirkire-kirkiren kwayoyin halitta, da magunguna da Sin ke gudanarwa, da kuma amfani da wadannan sababbin kayayyaki domin hidimtawa marasa lafiya a duniya. (Amina Xu)

    [ad_2]

    Source link

  • Mafarkin Kasashen Afrika Zai Tabbata Albarkacin Kasar Sin

    [ad_1]

    A lokacin da taro na 4 na majalisar wakilan jama’ar kasar Sin, wadda ke zaman majalisar dokokin kasar ke gudana a birnin Beijing, ministan harkokin wajen kasar Wang Yi, ya kira taron manema labarai a jiya Lahadi, inda ya yi karin haske kan manufofin diplomasiyyar kasar Sin.

    Mun riga mun san cewa, burin kasar Sin har kullum shi ne, zaman tare bisa adalci da daidaito da hakuri da girmama juna da kuma samun ci gaba na bai daya a duniya.

    Da aka yi masa tambaya game da irin sabbin ci gaban da za a gani a dangantakar Sin da Afrika a bana, Wang Yi ya bayyana wasu batutuwa 3:

    Na farko, al’umma mai makoma ta bai daya ta Sin da Afrika. Wannan na nufin bangarorin biyu sun zarce abokan hulda kawai, abokai ne da za su rika tafiya tare kafada da kafada a kan tafarki daya na samun ci gaba. Haka kuma yana nufin Sin za ta kasance babbar yaya wajen jagorantar kasashen Afrika su lalubo hanyar da ta dace da su ta samu ci gaba da kuma dogaro da kansu. Wannan ya nuna cewa, Sin tana son kasashen Afrika su kasance masu tsayawa da kafarsu, masu karfin fada a ji kan lamuran da suka shafe su, haka kuma masu bijerewa baba-kere da cin zali. Wanda zai taimaka matuka wajen ganin sun amfanawa kansu da kansu ba tare da neman taimako mai tattare da sharuda da katsalandan ba.

    Batu na biyu shi ne, soke harajin kwastam. A duniyar dake fama da rikicin cinikayya da karuwar harajin fito, ba tare da la’akari da matsayin kasashen Afrika na masu tasowa ba, Sin ta kara nuna matsayinta na babbar yaya, ta soke haraji kan kayayyakin kasashen Afrika 53 dake da huldar diplomasiyya da ita. Abun nufi, kasar Sin ta bude kofarta da katafariyar kasuwarta ga kasashen Afrika su shigo su ci gajiya. A ko da yaushe burin kasashen shi ne, su tashi daga masu dogaro da kayayyaki daga kasashen waje, su zama masu sarrafawa da fitar da kayayyaki. Kuma a bana, mafarkinsu zai tabbata albarkacin kasar Sin. Wannan abu ne da zai karfafa takardun kudinsu da bunkasa masana’antu da ayyukan gona, wadanda za su samar da aikin yi. Idan hakan ta samu kuma, arziki zai wadata a cikin al’umma, kuma za a samu raguwar aikata laifuka da tabbatuwar zaman lafiya.

    Batu na 3, aiwatar da shirye-shirye 600 na musayar al’adu tsakanin Sin da Afrika. Fahimtar juna ita ce kashin bayan kowane mu’amala. Yayin da ake samun habakar hulda ta cinikayya da tattalin arziki, ya zama wajibi a fahimci juna tsakanin mabambantan al’ummomi domin kaucewa rigingimu. Musaya tsakanin Sin da Afrika za ta bayar da muhimmiyar gudunmawa ga burin gina al’umma mai makoma ta bai daya. Za ta kara kyautata mu’amala tsakanin al’ummominsu, haka kuma, za ta toshe duk wata kafa da masu yada jita-jita ke amfani da ita ta haddasa fitina.

    Idan muka nazarci wadannan batutuwa da ya zayyano, a dunkule abubuwa ne da za su inganta ci gaban kasashen Afrika da bude musu kofar samun karin wadata. Hakika ci gaban Sin, ci gaba ne ga nahiyar Afrika. Kasar Sin ta zama jagora mai haskawa kasashen Afrika hanyar samun ci gaban da suke buri. (FMM)

    [ad_2]

    Source link