Category: Latest News

  • SAHUR (Falalarsa Da Fa’idojinsa) Na 20

    [ad_1]

    Fa’idar Sahur

    1. Yin sahur koyi ne da annabi Muhammad (Sallallahu alaihi wa alihi wa sallam), kuma malamai sun yi ijma’i a kan mustahabbi ne yinsa kamar yadda Ibnul Munzir da Imamu Annawawi suka naƙalto.

    2. Yin sahur saɓa wa Yahudu da Nasara ne, domin su ba sa yin sahur a azuminsu kamar yadda Muslim da Abu Dawud Tirmizi da Nasa’i suka ruwaito.

    • Darussa Daga Ramadan Na 9: Danne Fushi Da Nutsuwa A Ramalana
    • Ramadan: Lokutan Buda-Baki Da Sahur Na Azumi Na 10

    3. Sahur albarka ne ga mai yinsa kamar yadda hadisi ya gabata.

    4. Sahur yana samar da karfi ga mai azumi wajen yin ibada, da kuma ƙaruwar nishadi, da kuma tunkuɗe mummunar dabi’a da yunwa take haifarwa. Kuma a lokacin yinsa sahur, mutum yana samun dama ya yi sadaƙa ga almajiri ko kuma su ci tare. kuma yana sa mutum ya yi zikiri da addu’a, domin lokacin ne da ake karbar addu’a… “kamar yadda Hafiz Ibnu Hajar ya bayyana a littafinsa Fathul Bari (4/496) da malaminsa Ibnu Mulaƙƙin a cikim  al’I’ilamu (5/187)

    5. Samun salati daga Allah da mala’ikunsa.

    Allah ya datar da mu ga koyi da Manzon Allah (Sallallahu alaihi wa alihi wa sallam) a cikin al’amuranmu baki daya.

    [ad_2]

    Source link

  • Ƴansanda Sun Daƙile Yunƙurin Garkuwa Da Wasu Masallata A Zamfara

    [ad_1]

    Hukumar Ƴansanda ta Jihar Zamfara ta daƙile wani yunƙurin harin da ake zargin wasu ƴan bindiga sun kai a Gundumar Ruwan Dorowa, inda aka ƙara ƙarfafa matakan kare rayuka da dukiyoyin jama’a a jihar.

    Sanarwa daga Jami’in Hulɗa da Jama’a na Hukumar, DSP Yazid Abubakar, ta ce lamarin ya faru da misalin ƙarfe 8 na dare, lokacin da wani babbar tawagar ƴan bindiga ta bayyana a hanyar Maru.

    • Gwamna Lawal Ya Haramta Karbar Kuɗaɗen Shiga Da Tsabar Kuɗi A Zamfara
    • Uwargidan Gwamnan Zamfara Ta Ƙaddamar Da Tallafin Abincin Azumi Da Sallah Ga Mutane 16,000

    An ce masu hari sun nufi mazauna yankin da suke gudanar da Sallar Isha’i a masallatai.

    Bisa ga bayanan sirri na gaskiya, jami’in rundunar gunduma ya tura tawagar jami’an tsaro tare da haɗin gwiwar sojoji zuwa yankin da abin ya faru. Da ganin tawagar tsaro, ƴan bindigar sun fara harbi, wanda ya haifar da musayar wuta.

    Sai dai jami’an tsaro sun rinjayi masu hari saboda ƙarfin wuta da dabaru, inda suka tilasta musu tserewa cikin daji da ake zargin sun ji rauni daga harbin bindiga.

    DSP Yazid ya ce an ƙara yawan sintiri da leƙen asiri a yankin don hana wasu barazanar gaba da kwantar da hankalin jama’a.

    Ya buƙaci jama’a su ci gaba da kasancewa masu kulawa da natsuwa, tare da bayar da bayanai masu amfani ga jami’an tsaro.

    Hukumar ta tabbatar da ƙudurinta na ci gaba da yaƙi da ƴan ta’adda da sauran laifuka, tana mai tabbatarwa mazauna Zamfara cewa tana dagewa wajen kawar da miyagu da tabbatar da tsaro. Ya buƙaci jama’a su ci gaba da kasancewa masu kulawa da natsuwa, tare da bayar da bayanai masu amfani ga jami’an tsaro.

    Hukumar ta tabbatar da ƙudurinta na ci gaba da yaƙi da ƴan ta’adda da sauran laifuka, tana mai tabbatarwa mazauna Zamfara kawar da miyagu da tabbatar da tsaro.

    [ad_2]

    Source link

  • Kamfanin Sin Ya Bude Babban Titin Nairobi Kyauta Ga Masu Ababen Hawa Da Suka Makale Saboda Ambaliya

    [ad_1]

    Kamfanin kasar Sin mai kula da babban titin Nairobi, ya bude hanyar kyauta domin taimakawa masu ababen hawa isa wuraren da za su je, bayan mamakon ruwan sama da aka yi da yammacin jiya, ya haifar da cunkoson ababen hawa mai tsanani a birnin.

    Ruwan da aka fara da misalin karfe 5 na yamma agogon kasar, ya tsananta cikin dare, inda ya cika magudanan ruwa, ya mamale manyan hanyoyi, inda gomman motoci suka makale. Dubban mutane ne suka gaza yin zirga-zirga, inda komai ya kusan tsayawa cik a birnin.

    Biyo bayan haka ne babban titin Moja ya ba masu ababen hawa damar bin titin kyauta, ba tare da karbar ‘yan kudin da ake karba na kula da titin ba. Daruruwan direbobi ne suka amfana da hakan, inda suka yabawa wannan taimako da ya ba su damar komawa gida lami lafiya. (Mai fassara: FMM)

    [ad_2]

    Source link

  • ’Yan bindiga sun kashe mutum 1, sun sace wasu 5 a Sakkwato

    [ad_1]



    Wasu da ake zargin ’yan bindiga ne sun kai hari ƙauyen Mallamawar Yari da ke Ƙaramar Hukumar Rabah a Jihar Sakkwato, inda suka kashe mutum daya tare da sace wasu biyar.

    Harin ya faru ne da sanyin safiyar ranar Lahadi lokacin da maharan suka shiga ƙauyen suka fara harbe-harbe.

    Kakakin rundunar ’yan sandan jihar, Ahmad Rufa’i, ya tabbatar da faruwar harin.

    Sai dai ya ƙaryata rahotannin da ke cewa maharan sun sa hijaban mata wajen kai harin.

    “Ba gaskiya ba ne cewa ’yan bindigar sun sa hijaban mata. Sun shigo ƙauyen ne da yawa sannan suka fara harbe-harbe,” in ji Rufa’i.

    ’Yan sanda sun ce mutum ɗaya ne ya mutu a harin, yayin da aka sace mutane biyar; mata uku da maza biyu.

    Wata majiyar tsaro ta ce maharan sun zo da yawa a kan babura kusan 30, kuma kowane babur na ɗauke da ’yan bindiga uku.

    “An sanar da mu game da harin, kuma mun yi ƙoƙarin daƙile su, amma sun fi mu yawa. Mu biyar ne kawai jami’ai, yayin da su kuma suka zo da babura da yawa,” in ji majiyar.

    Majiyar ta ƙara da cewa jami’an tsaro sun ga maharan suna tafiya da waɗanda suka sace, amma ba za su iya fafatawa da su ba saboda sun fi su yawa.

    Ta kuma bayyana cewa kwanakin suka gabata an kai wani makamancin hari a wani ƙauye, amma jami’an tsaro sun samu nasarar fatattakar maharan, tare da kashe ɗaya daga cikinsu sannan suka ƙwato makamai.


    [ad_2]

    Source link

  • Yaƙin Gabas Ta Tsakiya: Masu Tafiya Umrah Daga Nijeriya Na Fuskantar Cikas

    [ad_1]

    Akwai wani yanayi na rashin tabbas a tsakanin kamfanoni masu zaman kansu da kuma matafiya Umara daga Nijeriya zuwa ƙasar Saudiyya, yayin da yaƙin Iran da Amurka ke ci gaba da yin illa ga ayyukan jiragen sama da sauran harkokin kasuwanci.

    Jaridar Daily Trust ta ruwaito cewa, ɗimbin al’ummar musulmi suna zuwa ƙasar Saudiyya a cikin watan Ramadan, domin aikin Umara, inda sama da masu ibada miliyan 122 suka ziyarci ƙasar a cikin watan Ramadana na shekarar 2025.

    • WSCIJ Ta Naɗa Farfesa Umaru Pate A Kwamitin Amintattu
    • Mutane 42 Sun Mutu A Wani Hatsarin Tankar Dizal Da Motar Masu Umrah A Hanyar Makka

    Sai dai kuma, tashin hankalin da ake fama da shi a Gabas ta Tsakiya, tare da rufe muhimman hanyoyin jiragen sama, irin su Doha da Dubai, na tilastawa maniyyata daga Nijeriya sake duba shirin tafiyar.

    Tashe-tashen hankula sun ƙara zama abubuwan lura a kan tsaro da amincin jirgin da kuma zuwa a kan lokaci, domin gudanar da ibada, lamarin da ya sa mutane da dama, ba su da tabbas a kan ko za su samu damar zuwa aikin nasu na Umara a bana.

    Ƙasashen Iran da Iraƙi da Isra’ila da Syria da Kuwait da Ƙatar da kuma Hadaddiyar Daular Larabawa, sun sanar da cewa; an rufe sararin samaniyarsu, bayan da Amurka da Isra’ila suka kai wa Iran hari, lamarin da ya kawo dakatar da zirga-zirgar jiragen sama na farar hula a Gabas ta Tsakiya.

    Fitattun kamfanonin jiragen sama da suka dakatar ayyukan, sun haɗa da kamfanin Emirates, Etihad, Ƙatar Airways, Air France, British Airways, Syria Air, Air India, Turkish Airlines, EgyptAir, Lufthansa da kuma Habasha Airlines.

    Sai dai, sauran kamfanonin jiragen saman irin su Saudi Arabian Airlines, na ci gaba da zirga-zirgar jiragen sama zuwa ƙasar, saboda Saudiyya ba ta rufe sararin samaniyarta a hukumance ba, duk da katsewar yankin.

    Sararin samaniyar Saudiyya na ci gaba da karɓar jiragen farar hula, bayan hare-haren ramuwar gayya a yankin Gabas ta Tsakiya.

    Duk da cewa dai kuma, hare-haren makami mai linzami da jiragen sama na baya-bayan nan da aka kai kan ababen more rayuwa na yankin Gulf, ciki har da harin da aka kai a wata cibiyar matatar mai a Saudiyya, ya haifar da fargabar cewa; Riyadh na iya sanya takunkumin sararin samaniya, idan rikicin ya ƙara tsananta.

    Mahajjata suna bayyana ra’ayoyinsu kusan iri ɗaya, waɗanda suka zanta da Daily trust, sun bayyana ra’ayoyinsu daban-daban, inda wasu ke tunanin soke tafiye-tafiyen nasu.

    Alhaji Auwal Sani, wanda ya yi niyyar zuwa aikin Umara a Kano, ya ce; an dakatar da tafiyasa wadda ya shirya yi a ranar Litinin.

    “Zan yi tafi ne a jirgin Ƙatar Airways, amma sai na samu saƙo daga wurinsu cewa; an buɗe tikitin bayan an soke shi, haka kuma ba a ba ni bizar ba har yanzu, kuma na shirya tafiya tare da iyalina a yau, amma ga mu duk a maƙale, Allah ne mafi sanin abin da ya fi dacewa da mu.

    “Sun ce za a buɗe sararin samaniya a ranar 6 ga watan Maris, sannan kuma za a ba mu biza, domin mu tafi,” in ji shi.

    Salihu Shu’aibu, wanda ke shirin tafiya Umrah, ya ce; halin da ake ciki a halin yanzu ya sa shi cikin damuwa ƙwarai da gaske.

    “Gaskiya, abin da yake faruwa, yana ba ni tsoro shi yasa nake tunanin ko kawai ma na soke tafiyar tawa kwata-kwata,” in ji shi.

    Ya ƙara da cewa, tsoron abin da ba a sani ba, ya dabaibaye maniyyata da dama a Jihar Kwara.

    [ad_2]

    Source link

  • Ranar Mata ta Duniya: Matakai 8 Na Inganta Rayuwar Mata Da Samar Da Daidaito A Duniya

    [ad_1]

    Babban Sakataren Majalisar Ɗinkin Duniya, António Guterres, ya bayyana wasu muhimman matakai takwas da ya ce za su taimaka wajen ƙara girmama mata da inganta daidaito a duniya, a yayin da ake bikin Ranar Mata ta Duniya.

    Ya ce cikin sama da shekaru goma da yake jagorantar Majalisar Ɗinkin Duniya, ya shaida yadda duniya ta fuskanci ƙalubale iri-iri, ciki har da sauyin yanayi, ƙaruwa da talauci, rikice-rikicen tashin hankali da kuma takaita ’yancin jama’a.

    • Guterres: Jerin Shawarwarin Da Sin Ta Gabatar Sun Cika Ka’idar Kundin Tsarin Majalisar Dinkin Duniya
    • Yunwa Ta Kazanta A Sansanonin ‘Yan Gudun Hijira Tun Bayan Da Majalisar Dinkin Duniya Ta Dakatar Da Ayyukanta

    Sai dai ya ƙara da cewa duk da waɗannan matsaloli, an samu hanyoyin warware su a wurare da dama na duniya, kuma abu guda da ya haɗa su shi ne rawar da mata suka taka.

    A cewarsa, lokaci ya yi da duniya za ta fahimci cewa rashin daidaito tsakanin maza da mata na daga cikin manyan ƙalubalen kare haƙƙin ɗan Adam a wannan zamani. Ya ce inganta daidaito tsakanin jinsi kuma yana daga cikin hanyoyin da ke taimakawa wajen samar da ci gaba mai ɗorewa da kuma zaman lafiya.

    Matakai Takwas da Aka Nuna

    1. Gurbi a Tsarin Mulki

    Guterres ya ce har yanzu maza ne suka fi rinjaye a yawancin cibiyoyin da ke tsara yadda duniya ke tafiya. Ya ƙara da cewa ƙaruwa da mulkin kama-karya a wasu wurare na ƙara zurfafa wannan gibi, tare da barazana ga wasu muhimman haƙƙoƙi na mata, ciki har da haƙƙin aiki da kuma na lafiyar haihuwa.

    2. Rashin Isasshen Wakilci

    A cewarsa, mata har yanzu ba su da isasshen wakilci a gwamnati da kuma manyan muƙaman yanke shawara a duniya. Ya ce a Majalisar Ɗinkin Duniya an ɗauki matakin ba wa daidaito tsakanin maza da mata muhimmanci musamman a manyan mukamai.

    3. Amfanin Zuba Jari a Mata

    Ya bayyana cewa saka jari a ilimi da lafiyar mata na kawo riba mai yawa ga al’umma. A cewarsa, kuɗin da ake kashewa wajen ilimantar da ’yan mata na iya samar da riba sau uku, yayin da saka jari a lafiyar uwa da tsarin iyali ke haifar da riba sau takwas.

    4. Muhimmancin Shigar Mata a Sulhu

    Guterres ya ce yarjejeniyar zaman lafiya na fi ɗorewa idan mata sun taka rawa a tattaunawa da aiwatar da ita. Duk da haka, a yawancin rikice-rikice na duniya ana barin mata a gefe, duk da cewa su ne ke ɗaukar babban nauyin wahalar yaƙi.

    5. Wariyar Launin Fata

    Ya ce a sassa da dama na duniya, mata ba su da cikakken damar shari’a kamar maza. A wasu ƙasashe ba su da cikakken ikon mallakar dukiya ko kuma samun wasu ’yancin aiki da zamantakewa.

    6. Cin Zarafi ga Mata

    Babban Sakataren ya ce cin zarafi da ake yi wa mata da ’yan mata ya zama babbar matsala ta duniya, wadda ta samo asali daga rashin daidaito tsakanin jinsi. Ya jaddada cewa kowace mace da yarinya na da haƙƙin rayuwa cikin aminci ba tare da tsoro ba.

    7. Wariyar Fasaha

    A fannin fasaha kuwa, mata suna da ƙanƙanin wakilci. A halin yanzu suna wakiltar kusan kashi ɗaya cikin huɗu ne kawai. Haka kuma ya ce ƙiyayya ga mata a yanar gizo na ƙaruwa, lamarin da ke barazana ga tsaro da haɗin kai a cikin al’umma.

    8. Jagorancin Mata wajen Sauyin Yanayi

    Guterres ya ce sauyin yanayi na shafar mata fiye da maza a lokuta da dama. Sai dai duk da haka, mata suna kan gaba wajen samar da mafita, ta hanyar jagorantar manufofin kare muhalli da kuma motsa al’umma zuwa sauyi.

    A ƙarshe, ya ce a ƙwarewarsa ya ga waɗannan matakai suna aiki a wurare daban-daban – daga wuraren yaƙi zuwa majalisun dokoki, makarantu da kuma cikin al’umma.

    Ya kuma jaddada cewa idan shugabanni suka ɗauki daidaito tsakanin maza da mata da muhimmanci, tare da ɗaukar matakan aiwatar da shi tun yanzu, za a iya samar da duniya mafi adalci ga mata da ’yan mata, da kuma ga kowa baki ɗaya.

    [ad_2]

    Source link

  • Gwamnatin Kebbi Ta Yi Rabon Kayan Aikin Noman Rani

    [ad_1]

    Gwamna Nasir Idris na Jihar Kebbi ya raba kayan aikin gona, ciki har da injinan niƙa ƙasa da na’urar famfo mai amfani da hasken rana, ga manoma a matsayin wani ɓangare na ƙoƙarin fara aikin gona na kakar rani ta 2026.

    An gudanar da rarraba kayan ne ƙarƙashin shirin raya aikin gona na Kauran Gwandu (KADAGE), inda kuma aka ƙaddamar da tallafin Ramadan ga mazauna jihar.

    • Sojoji Sun Kashe ‘Yan Ta’adda 5 A Kebbi
    • Sojoji Sun Kashe ‘Yan Ta’adda 2, Sun Ceto Mutane 62 Da Aka Yi Garkuwa Da Su A Kebbi Da Zamfara

    Gwamnan ya bayyana cewa wannan shiri na nufin ƙarfafa manoma, haɓaka amfanin gona, da ƙarfafa tsaron abinci a jihar da ma duk Nijeriya baki ɗaya.

    Ya lura cewa samar da shinkafa a jihar ya ƙaru daga tan miliyan 3.5 a shekarar da ta gabata, kuma ana sa ran zai kai fiye da tan miliyan 3.8 a wannan shekarar.

    Haka kuma, ya ce gwamnatin ta riga ta raba taki mai darajar sama da Naira biliyan 3 kyauta ga manoma domin ƙara yawan amfanin gona.

    Gwamna Idris ya kuma bayyana cewa an sayi nau’ukan hatsi daban-daban don rabawa ga sama da mazauna miliyan ɗaya a matsayin tallafin Ramadan.

    Ministan Aikin Gona da Tsaron Abinci, Abubakar Kyari, wanda ya halarci taron, ya bayyana Kebbi a matsayin muhimmiyar cibiyar aikin gona inda noma ke kasancewa babbar hanyar samun rayuwa.

    Ya ce jihar na bi daidai da shirin Gwamnatin Tarayya na “Renewed Hope Agenda” kan tsaron abinci, sannan ya yaba da rarraba kayan aikin gona na zamani.

    Kwamishinan Aikin Gona na Jihar, Shehu Mu’azu, ya ce wannan mataki ya cika alƙawuran yaƙin neman zaɓe ga manoma, yayin da Shugaban RIFAN, Yusuf Gabi Argungu, ya yaba da gwamnati, yana mai alƙawarin ci gaba da goyon bayan manoma ga sauye-sauyen aikin gona.

    [ad_2]

    Source link

  • Darussa Daga Ramadan Na 15: Kusancin Allah Da Amsar Addu’a A Ramalana

    [ad_1]

    A watan Ramalana muna ƙara fahimtar cewa Allah Maɗaukaki Yana kusa da mu da iliminsa, kusa da jinsa, kusa da taimakonsa da rahamarsa. Ba kusanci na tazara ba ne, amma kusanci ne na kulawa da amsa addu’a da kiran da ake yi masa tsarki ya tabbata a gare Shi.

    A tsakiyar ayoyin azumi, Allah Ya kawo wata aya mai cike da ta’aziyya da bege. Ya ce a cikin Alƙur’ani, a Suratul Baƙara aya ta ( 186): “Kuma idan bayina suka tambaye ka dangane da Ni, to, lalle Ni kusa Nake. Ina amsa kiran mai kira idan ya kiraye Ni. Don haka su amsa Mini kiran, kuma su yi imani da Ni, domin su shiryu”

    • Darussa Daga Ramadan Na 14: Yawaita Kyauta Da Ihsani A Ramalana
    • Darussa Daga Ramadan Na 13: Tsayuwar Dare

    Ka lura da yadda ayar ta zo kai tsaye; ba a ce “Ka ce musu Ina kusa” ba; Allah Ya ce “Ni kusa Nake”. Wannan yana nuna kusanci na musamman, kusancin rahama, da kusancin jin ƙorafi, kusancin amsa koke.

    Ramalana wata ne da wannan kusanci yake bayyana sosai. Zuciya tana laushi, hawaye suna sauƙin zuba, addu’a tana fitowa daga zurfin ran bil’adama. Mumini yana jin cewa babu shamaki tsakaninsa da Ubangijinsa.

    Wannan aya ta ƙunshi manyan darussa:

    1. Allah Yana kusa da bayi: babu buƙatar mai shiga tsakani wajen roƙonsa.
    2. Yana amsa addu’a: komai girman buƙata ko ƙarancinta.
    3. Akwai sharaɗi na amsa addu’a: shi ne “su amsa Mini kiran” watau su yi biyayya ga umarninsa.
    3. Imani shi ne hanyar shiriya: duk wanda ya yi imani da gaske, zai samu jagoranci.

    Saboda haka, karɓuwar addu’a tana da alaƙa da biyayya. Idan bawa yana so Allah Ya amsa masa, shi ma ya amsa wa Allah ta hanyar aikata umarni da nisantar hani.

    Ramalana yana koya mana cewa Allah ba Ya nesa. Idan damuwa ta yi yawa, Yana kusa. Idan buƙata ta yi girma, Yana kusa. Idan zuciya ta karye, Yana kusa. Kuma Yana jin kukan bawa ko da a cikin dare ne mai zurfi Fahimtr haka; tana haifar da kwanciyar hankali. Domin wanda ya san Allah Yana kusa, ba ya yanke ƙauna. Wanda ya san Allah Yana ji, ba ya jin shi kaɗai ne. Wanda ya san Allah Yana amsawa, ba ya daina addu’a.

    Saboda haka, mu yawaita kiran Sa a Ramalana. Mu roƙe Shi da zuciya mai ƙasƙantar da kai. Mu haɗa addu’a da biyayya. Mu haɗa bege da tsoron Allah.

    Allah Ya sa mu kasance cikin masu gane kusancinsa, masu amsa kiransa, masu samun amsar addu’a da shiriya a duniya da Lahira. Amin.

    [ad_2]

    Source link

  • Ko Shirin Ciyar Da Mabuƙata Buɗa Baki Na Bilyan Ɗaya Ya Yi Tasiri A Sakkwato?

    [ad_1]

    Watan azumi muhimmin lokaci ne da mabuƙata ke buƙatar sanyayawa daga gwamnatoci, ‘yan uwa da masu hannu da shuni domin gudanar da ibada a cikin sauƙi musamman domin rage masu raɗaɗin matsin tattalin arziki.

    A Sakkwato akwai ɗimbin al’ummar da suka dogara da ciyarwar buɗa baki da mabambantan gwamnatoci a jihar ke yi a tsayin shekaru domin sa wa a baka kasancewar ba su da zarafin ciyar da kan su a watan mai albarka.

    • Ramadan: Lokutan Buda-Baki Da Sahur Na Azumi Na 19
    • Harin Iran: Amurka Da Isra’ila Sun Bata Lissafi

    A yayin da watan Ramadan ya shiga mako na biyu labari ya yaɗu a kafafen sadarwar zamani cewar wata sabuwa ta bayyana a Sakkwato a yayin da gwamnatin jihar ke raba garin kwaki da ƙuli- ƙuli a matsayin abincin buɗa baki.

    Lamarin ya ɗauki hankalin al’umma musamman ganin irin maƙuddan kuɗin da gwamnatin jihar ta ware kan ciyarwar amma kuma a rabawa mabuƙata gari a watan Ramadan.

    Shin da gaske gwamnatin jihar ta raba garin kwaki da ƙuli- ƙuli? Idan ta raba a waɗanne cibiyoyin buɗa baki ne aka yi rabon ko kuwa a duka cibiyoyin buɗa bakin ne aka raba garin?

    LEADERSHIP Hausa ta kasa gano wata unguwa ko wani gari da aka ga gwamnatin jihar ta raba garin kwaki da ƙuli- ƙuli a matsayin abincin buɗa baki kamar yadda aka labarta labarin a soshiyal midiya, haka ma babu rahoto kan wani ɗan siyasa ko masu hannu da shunin da suka raba garin kwaki da ƙuli- ƙuli a faɗin jihar a watan Ramadan.

    Hasalima ofishin Kwamishinan Addinin Musulunci na jihar, Dakta Jabir Sani Mai- hula ya wallafa sanarwa a shafinsa na Facebook inda ya bayyana cewar ko kaɗan babu ƙamshin gaskiya a zancen raba gari da ƙuli- ƙuli ga al’umma a yayin buɗa baki.

    Ma’aikatar ta bayyana cewar suna raba abinci mai kyau ga al’ummar jihar wanda kuma ma’aikatar ke sa idanu da ziyarar gani da ido ga cibiyoyin buɗa bakin domin tabbatar da bin ƙa’idojin shirin ciyarwar yadda ya kamata.

    Rahotanni a jihar sun tabbatar da cewar kamar yadda ta saba a kowace shekara, gwamnatin jihar Sakkwato a azumin bana ta jagoranci gudanar da shirin ciyar da al’ummar jihar buɗa baki da manufar raba kwanan abinci 34, 000 a kullum.

    A yayin da wasu gwamnatocin jihohi ke ware ɗaruruwan miliyoyi domin shirin buɗa bakin Ramadan na shekarar 2026, Gwamnatin jihar Sakkwato ta keɓe tsabar kuɗi har naira bilyan ɗaya musamman domin amfanin al’umma dubu 986, 000.

    A yayin ƙaddamar da shirin ciyarwar, Gwamna Ahmed Aliyu ya bayyana cewar ciyar da mabuƙata a lokacin Ramadan na ɗaya daga cikin ƙudurorin gwamnnatin sa na sanyawawa jama’a a lokacin buƙata.

    A shirin na bana gwamnatin jiha ta ƙara adadin cibiyoyin buɗa baki daga 155 zuwa 170 a bisa ga ƙorafe- ƙorafen buƙatar ƙarin cibiyoyin ta yadda kowace cibiya za ta riƙa kula da buɗa bakin aƙalla mutane 200 a lokaci ɗaya.

    Kuɗin shirin biliyan ɗaya kamar yadda Gwamnatin ta bayyana sun ƙunshi sayen kayan abinci, biyan ma’aikata da sauran kuɗaɗen gudanarwa domin tabbatar da aiwatar da shirin cikin tsari da nasara.

    Kwamitin shirin ciyar da mabuƙata buɗa baki na gwamnatin Sakkwato yana a ƙarƙashin jagorancin ɗan majalisar Mai Alfarma Sarkin Musulmi kuma Galadiman Garin Sakkwato, Alhaji Aliyu Attahiru Galadanchi a yayin da Ma’aikatar Lamurran Addini a ƙarƙashin jagorancin Dakta Jabir Mai-hula ke sanya idanu.

    Gabanin lokacin shan ruwa, ƴan kwamitin shirin kan fara shirye-shiryen da suka haɗa da tsara kayan abinci, rabawa da kuma tabbatar da cewa komai ya kammala cikin tsafta da nagarta. A na shirya abincin cikin kulawa domin tabbatar da cewa ya kai ga duk wanda ya cancanta ba tare da tangarɗa ba.

    Haka kuma, ‘yan kwamitin kan tsara layuka cikin tsari tare da sanya ido kan yadda ake rabon domin gujewa cunkoso da wawaso a a yayin da tuni mabuƙata suke hallara a cibiyoyin suna zaman jiran lokacin shan ruwa.

    Abincin da kwamitin ke rabawa shine, shinkafa da miya da naman kaji, kunu, ƙosai, alale, lemu, dabino da ruwa ga ɗimbin mabuƙatan da ke ke buɗa baki a cibiyoyin a kowace rana

    Gwamna Ahmed Aliyu a yayin ƙaddamar da shirin ya bayyana shi a matsayin wani muhimmin shirin tallafin jinƙai da nufin rage raɗaɗin azumi ga al’ummar Musulmi tare da ƙarfafa tausayi, haɗin kai da goyon bayan juna a cikin watan Ramadan mai alfarma.

    “Ina ba ku tabbacin cewa abincin zai kasance mai tsafta, an shirya shi cikin tsari mai kyau kuma mai inganci. Haka kuma, an ɗauki ma’aikatan wucin gadi domin tabbatar da tafiyar da shirin cikin nasara a duk tsawon watan Ramadan.” In ji Gwamnan a yayin ƙaddamar da shirin.

    Ya ce shirin rabon abincin na daga cikin manyan tsare-tsaren gwamnatinsa na bunƙasa fa’idojin Musulunci da walwalar al’umma. Ya ce hakan ya haɗa da gyaran masallatai da makarantu tare da biyan alawus na wata-wata ga masallatan Juma’a domin tallafa musu wajen gudanar da ayyukansu.

    Gwamnan ya ce shirin wanda aka ƙaddamar shekaru 19 da suka gabata a zamanin mulkin tsohon gwamna Aliyu Wamakko, ya ci- gaba da samar da sauƙi da tallafi ga dubban al’ummar jihar, lamarin da ke nuna jajircewar jihar wajen yaƙi da talauci da inganta rayuwar al’umma.

    Shin kwamitin buɗa bakin na gudanar da aikin ciyarwar yadda ya kamata, ko gwamnatin jihar ta gamsu da yadda buɗa bakin ke tafiya kuma yaya take gani da kallon alfanu ko tasirin shirin?

    Da yake bayyana ra’ayinsa kan shirin ciyarwar, tuni Gwamnan Jihar Sakkwato, Ahmed Aliyu ya bayyana gamsuwa da inganci da wadatar abincin buɗa baki da gwamnatin ke aiwatarwa a watan Ramadan a ƙarƙashin shirin ciyarwa na naira bilyan ɗaya.

    Aliyu ya bayyana hakan ne a yayin da ya ziyarci cibiyoyin buɗa bakin azumi da ke kan titin Clapperton, Lodge Road, Gidan Dallatu, Asibitin Ƙwararru da kuma yankin Maɗunka a inda ya gana da masu cin gajiyar shirin tare da mambobin kwamitocin ciyarwar.

    Da yake jawabi bayan kammala duba cibiyoyin, Gwamnan ya yabawa kwamitin ciyarwar yana mai cewa an samu gagarumin ci- gaba a yadda ake gudanar da shirin idan aka kwatanta da shekarar da ta gabata.

    Ya ce ya gamsu da abin da ya gani a cibiyoyin a kan hakan ya buƙaci mambobin kwamitocin cibiyoyin ciyarwar da su ci- gaba da ƙara ƙaimi da jajircewa wajen tabbatar da cikar manufofin shirin.

    “Manufar wannan shiri ita ce tallafawa marasa galihu ta hanyar samar musu wurin buɗa baki cikin sauƙi, saboda haka muna buƙatar ƙarin jajircewa daga kwamitocin cibiyoyin ciyarwar.” In ji gwamnan.

    Haka kuma, ya yi kira ga masu hannu da shuni a cikin al’umma da su taimaka wajen marawa ƙoƙarin gwamnati baya ta hanyar kafa cibiyoyin ciyarwa a cikin al’ummominsu don tallafawa marasa galihu.

    Malam Harande Sani, mazaunin Unguwar Rogo, ya bayyana shirin a matsayin abin a yaba, yana mai cewa yana taimakawa marasa galihu musamman a wannan lokaci na tsadar rayuwa. “Wannan shiri ya rage mana nauyi sosai a watan Ramadan. Mutane da dama da ba su da hali ire- ire na suna samun damar buɗa baki cikin kwanciyar hankali.”

    A nasa ɓangaren Kallamu Gandi daga unguwar Bado cewa ya yi “Shirin yana da muhimmanci matuƙa domin yana tallafawa dubban iyalai. Ina ganin gwamnati ta yi ƙoƙari amma ya kamata a ƙara yawan abinci ko cibiyoyi domin rage cincirindon jama’a da ke akwai a wasu cibiyoyin.”

    [ad_2]

    Source link

  • Bishap Kukah Ya Bayyana Dalilin Tilasta Wa Ƴan Siyasa Sa Hannu A Yarjejeniyar Zaman Lafiya

    [ad_1]

    Shugaban Kwamitin Ƙasa na Zaman Lafiya, Matthew Hassan Kukah, ya bayyana dalilin da ya sa ake buƙatar ƴan siyasa su sanya hannu kan yarjejeniyar zaman lafiya kafin da bayan zaɓe.

    Kukah, Bishof na Katolikan Sokoto Diocese, ya yi wannan jawabi ne a wajen taron masu ruwa da tsaki da gabatar da yarjejeniyar zaman lafiya da aka yi wa sharhi, wanda The Kukah Centre ta shirya tare da goyon bayan European Union a Abuja ranar Litinin.

    • Ƴansanda Sun Ƙaddamar Da “Operation Kukan Kura” A Kano, Sun Cafke Mutune 98.
    • Manyan Jami’o’in Kasar Sin Sun Samar Da Karin Guraben Karatu 38,000 Cikin Shekaru Biyu Da Suka Gabata

    Ya ce yarjejeniyar zaman lafiya an tsara ta ne don ƙarfafa ƴan siyasa su kasance masu ɗabi’a, yana mai jaddada cewa da zarar an sanya hannu, nauyin kiyaye zaman lafiya ba wai kawai kan ƴan siyasa bane, har ma kan ƴan Nijeriya , kafofin yaɗa labarai, da ƙungiyoyin farar hula.

    “Lokacin da ƴan siyasa suka sanya hannu kan yarjejeniya, ba kawai ga kwamitin zaman lafiya bane. Yana zama nauyin kowa ya tabbatar an bi shi,” in ji Kukah.

    Ya lura cewa tashin hankali na siyasa, yaɗuwar labaran ƙarya, da matsalolin tsaro suna ci gaba da barazanar sahihancin zaɓe, inda ya ƙara da cewa an kafa kwamitin don tallafa wa sulhu, gina amincewa, da kyakkyawar niyya tsakanin ƴan siyasa.

    A cewar shi, ayyukan sirrin kwamitin sun taimaka wajen samar da mafita masu amfani da rage rikice-rikice yayin gasa ta zaɓe.

    Kukah ya ce dole ne zaɓe ya kasance cikin lumana, mai gaskiya, kuma abin amincewa, yana tunatar da ƴan siyasa cewa a kowane gasa, za a samu masu nasara da waɗanda ba su ci ba.

    Ya buƙaci ƴan siyasa su ɗauki yarjejeniyar zaman lafiya a matsayin haƙiƙanin alƙawari ga ƴan Nijeriya, yana gargaɗin cewa doka kaɗai ba za ta iya tabbatar da zaman lafiya ba idan ba a canza hali ba.

    “Doka tana da kyau, amma zuciyar ɗan’Adam ma dole ta canza. Idan mutane ba su da niyya, sai su zama tushen rikici,” in ji shi.

    Kukah ya ƙara da cewa taron ya ba da dama don yin nazari kan yanayin zaɓe na yanzu da gano wuraren da kwamitin zai iya amfani da ikon darajar sa don tallafawa sahihancin zaɓe.

    Har ila yau, ya yi kira ga kafafen watsa labarai, kungiyoyin farar hula, da hukumomin tsaro da su ci gaba da aiki tare don gina Nijeriya mai zaman lafiya da kwanciyar hankali.

    [ad_2]

    Source link