Bishap Kukah Ya Bayyana Dalilin Tilasta Wa Ƴan Siyasa Sa Hannu A Yarjejeniyar Zaman Lafiya

[ad_1]

Shugaban Kwamitin Ƙasa na Zaman Lafiya, Matthew Hassan Kukah, ya bayyana dalilin da ya sa ake buƙatar ƴan siyasa su sanya hannu kan yarjejeniyar zaman lafiya kafin da bayan zaɓe.

Kukah, Bishof na Katolikan Sokoto Diocese, ya yi wannan jawabi ne a wajen taron masu ruwa da tsaki da gabatar da yarjejeniyar zaman lafiya da aka yi wa sharhi, wanda The Kukah Centre ta shirya tare da goyon bayan European Union a Abuja ranar Litinin.

  • Ƴansanda Sun Ƙaddamar Da “Operation Kukan Kura” A Kano, Sun Cafke Mutune 98.
  • Manyan Jami’o’in Kasar Sin Sun Samar Da Karin Guraben Karatu 38,000 Cikin Shekaru Biyu Da Suka Gabata

Ya ce yarjejeniyar zaman lafiya an tsara ta ne don ƙarfafa ƴan siyasa su kasance masu ɗabi’a, yana mai jaddada cewa da zarar an sanya hannu, nauyin kiyaye zaman lafiya ba wai kawai kan ƴan siyasa bane, har ma kan ƴan Nijeriya , kafofin yaɗa labarai, da ƙungiyoyin farar hula.

“Lokacin da ƴan siyasa suka sanya hannu kan yarjejeniya, ba kawai ga kwamitin zaman lafiya bane. Yana zama nauyin kowa ya tabbatar an bi shi,” in ji Kukah.

Ya lura cewa tashin hankali na siyasa, yaɗuwar labaran ƙarya, da matsalolin tsaro suna ci gaba da barazanar sahihancin zaɓe, inda ya ƙara da cewa an kafa kwamitin don tallafa wa sulhu, gina amincewa, da kyakkyawar niyya tsakanin ƴan siyasa.

A cewar shi, ayyukan sirrin kwamitin sun taimaka wajen samar da mafita masu amfani da rage rikice-rikice yayin gasa ta zaɓe.

Kukah ya ce dole ne zaɓe ya kasance cikin lumana, mai gaskiya, kuma abin amincewa, yana tunatar da ƴan siyasa cewa a kowane gasa, za a samu masu nasara da waɗanda ba su ci ba.

Ya buƙaci ƴan siyasa su ɗauki yarjejeniyar zaman lafiya a matsayin haƙiƙanin alƙawari ga ƴan Nijeriya, yana gargaɗin cewa doka kaɗai ba za ta iya tabbatar da zaman lafiya ba idan ba a canza hali ba.

“Doka tana da kyau, amma zuciyar ɗan’Adam ma dole ta canza. Idan mutane ba su da niyya, sai su zama tushen rikici,” in ji shi.

Kukah ya ƙara da cewa taron ya ba da dama don yin nazari kan yanayin zaɓe na yanzu da gano wuraren da kwamitin zai iya amfani da ikon darajar sa don tallafawa sahihancin zaɓe.

Har ila yau, ya yi kira ga kafafen watsa labarai, kungiyoyin farar hula, da hukumomin tsaro da su ci gaba da aiki tare don gina Nijeriya mai zaman lafiya da kwanciyar hankali.

[ad_2]

Source link

Similar Posts

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *