Category: Latest News

  • Kotun ɗaukaka ƙara ta yi watsi da ƙorafin ɓangaren Turaki a PDP

    [ad_1]



    Kotun ɗaukaka ƙara da ke Abuja ta yi watsi da ƙorafin da tsagin jam’iyyar PDP ƙarƙashin jagorancin Tanimu Turaki ya shigar, tare da tabbatar da hukuncin Babbar Kotun Tarayya da ta rushe shugabancin da aka zaɓe shi a kai.

    Kotun ƙarƙashin jagorancin alƙalai uku ta yanke hukuncin cewa ƙorafin da ɓangaren Turaki ya shigar ba shi da tushe, tana mai cewa Babbar Kotun Tarayya tana kan daidai lokacin da ta hana Hukumar Zaɓe Mai Zaman ta Ƙasa (INEC) amincewa da babban taron ƙasa na PDP da aka gudanar a Ibadan, Jihar Oyo.

    Tun da farko Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja ta yanke hukunci a ranar 31 ga Oktoba cewa taron jam’iyyar da aka gudanar a ranakun 15 da 16 ga Nuwamba a Ibadan — inda aka zaɓi Turaki a matsayin shugaban jam’iyyar — bai gudana bisa ƙa’ida ba.

    Sakamakon haka ne ɓangaren Turaki ya garzaya kotun ɗaukaka ƙara domin ƙalubalantar hukuncin, yana mai cewa Babbar Kotun Tarayya ba ta da hurumin sauraron ƙarar domin batun ya shafi harkokin cikin gida na jam’iyya.

    Sai dai kotun ɗaukaka ƙarar ta yi watsi da wannan iƙirari, tana mai cewa masu ƙara suna da haƙƙin kai ƙara domin kare muradunsu na dimokuraɗiyya, kuma babu hujjar cewa an hana PDP damar kare kanta yadda ya kamata.

    Kotun ta kuma ci tsagin Turaki tarar naira miliyan biyu kan shigar da ƙarar da ta ce ba ta da tushe, tare da cewa za a ci gaba da sauraron wasu batutuwan da suka shafi rikicin cikin gida na jam’iyyar.


    [ad_2]

    Source link

  • Gwamnan Zamfara Dauda Dare ya koma APC

    [ad_1]



    Rahotanni sun bayyana cewa Gwamnan Zamfara, Dauda Lawal Dare ya sauya sheƙa daga jam’iyyar PDP zuwa APC mai mulki a ƙasar.

    Mataimaki kuma muƙaddashin Gwamnan, Mani Mummuni ne ya sanar da hakan bayan taron majalisar zartarwar jihar da aka gudanar a gidan gwamnati da ke Gusau.

    Bayan kammala taron, mambobin majalisar zartarwa da manyan jiga-jigan PDP a jihar sun amince da komawa APC, inda aka riƙa ɗaga tutoci da rera taken jam’iyyar APC a matsayin nuna goyon baya ga sabon matakin.

    Aminiya ta ruwaito cewa a halin yanzu gwamnan yana Saudiyya inda ya tafi Umrah.

    Ana iya tuna cewa, Gwamna Dare ya bayyana cewa hukuncin da kotun ɗaukaka ƙara za ta yanke kan halascin babban taron PDP da aka gudanar a Ibadan a bara zai taimaka wajen tantance matakin da za su ɗauka dangane da rikicin shugabanci da ke addabar jam’iyyar.

    A halin yanzu kuma, muƙaddashin gwamnan yana ganawar sirri da ‘yan majalisar dokokin jihar domin tattauna sabon matsayar siyasar da kuma yadda za su hada kai a karkashin APC.

    A wannan Litinin ɗin ce Kotun Ɗaukaka Ƙara ta tabbatar da hukuncin cewa babban taron jam’iyyar PDP da aka gudanar a birnin Ibadan na Jihar Oyo a bara, wanda ya ayyana Tanimu Turaki a matsayin shugaban jam’iyyar bai halasta ba.


    [ad_2]

    Source link

  • DSS Ta Kama Kwamandan Ƴan Ta’addan IPOB Da Ake Zargi Da Kashe Ƴansanda

    [ad_1]

    Jami’an Tsaro Na DSS sun kama wasu mutane biyu da ake zargi da mambobin ƙungiyar tsageru ƴan aware ne yayin wani sumame da suka kai a Jihar Enugu State.

    Wadanda aka kama sun hada da Sabastine Odo Odam, wanda ake zargin kwamandan Eastern Security Network ne, da kuma Ejike Daniel, mamba na Indigenous People of Biafra. An kama su ne a garuruwan Eha-Amufu da Umuhu na ƙaramar hukumar Isi-Uzo.

    • DSS Ta Kama Wasu Jami’an Tsaro Kan Zargin Taimaka Wa El-Rufai
    • Bayan Shekaru 7, DSS Ta Sake Buɗe Binciken Ɓacewar Dadiyata

    Majiyoyin tsaro sun ce an gudanar da sumamen ne ranar Juma’a bayan watanni na sa ido da tattara bayanan sirri kan ayyukan waɗanda ake zargin. An ce matakin ya biyo bayan hare-hare da dama da aka kai kan ofisoshin ‘yansanda da kuma kashe-kashen da aka samu tsakanin 2024 zuwa 2026.

    Rahotanni sun ce waɗanda ake zargin sun amsa hannu a wasu hare-hare da aka kai kan ofisoshin ‘yansanda inda aka sace makamai, ciki har da kashe ma’aikata 11 a Fabrairu 2026 da kuma ‘yansanda da dama a lokuta daban-daban.

    An ce mazauna yankin Isi-Uzo sun yi maraba da kamen jama’ar yadda jaridar Global News ta rawaito, suna fatan hakan zai taimaka wajen dawo da zaman lafiya. A halin yanzu ana tsare da waɗanda ake zargin a hannun DSS, kuma ana sa ran za a gurfanar da su a kotu bayan kammala bincike.

    [ad_2]

    Source link

  • Matatar Dangote Ta Sake Ƙara Farashin Fetur Zuwa ₦1,175

    [ad_1]

    Ana hasashen farashin kayayyaki da ayyuka a faɗin Nijeriya zai ci gaba da ƙaruwa bayan wani sabon ƙarin farashin fetur, bayan da matatar man fetur ta Dangote ta kara farashi zuwa N1,175 kan kowace lita, wanda ya zama karo na uku da aka ƙara farashin cikin mako guda.

    Sabon sauyin farashin ya zo ne sa’o’i kaɗan bayan jaridar The PUNCH ta yi hasashen cewa, farashin fetur na iya ƙaruwa karo na uku cikin mako guda, bayan dakatarwar wucin gadi da matatar ta yi kan sayar da fetur a ranar Lahadi.

    Matatar ta sanar da ‘yan kasuwa sabon ƙarin farashin ne a ranar Litinin, inda ta ɗaga farashin zuwa N1,175 kan kowace lita, daga N995 kan kowace lita da aka sanar a ranar Juma’a. Wannan na nufin an samu ƙarin N180.

    [ad_2]

    Source link

  • HOTUNA: Yadda Iraniyawa ke murnar naɗin sabon jagora Mojtaba Khamenei

    [ad_1]



    Dubban mutane sun yi dandazo a birnin Tehran domin yi wa sabon jagoran addinin Iran Mojtaba Khamenei mubaya’a, bayan sanar da naɗinsa a matsayin jagoran ƙasar.

    Rahotanni sun ce jama’ar sun fito kan manyan tituna da filayen taro a birnin, suna ɗaga tutocin Iran da kuma hotunan sabon jagoran, yayin da wasu ke rera taken goyon baya.

    Wannan dai na zuwa ne bayan Majalisar Masana ta Iran ta zaɓi Mojtaba Khamenei a matsayin jagora na uku tun bayan juyin juya halin Musulunci na 1979, domin maye gurbin mahaifinsa, Ali Khamenei da aka kashe a hare-haren da Amurka da Isra’ila suka kai.

    Magoya bayan gwamnatin Iran suna murnar naɗin Mojtaba Khamenei a matsayin sabon jagoran addinin ƙasar.

    Hotunan da Kamfanin Dillancin Labarai na Reuters ya wallafa sun nuna dubban mutane suna taruwa a wurare kamar Dandanlin Vali-Asr, inda suka riƙa taya juna murna tare da nuna goyon baya ga sabon jagoran ƙasar.

    Iraniyawan sun buƙaci sabon jagoran ya kawo ƙarshen kwanaki na rashin tabbas da ƙasar ta shiga bayan mutuwar tsohon jagoran.


    [ad_2]

    Source link

  • Ina da yaƙinin sabon jagoran Iran zai ɗora daga inda mahaifinsa ya tsaya — Putin

    [ad_1]



    Shugaban Rasha Vladimir Putin ya bayyana cewa yana yaƙinin cewa sabon jagoran addinin Iran, Mojtaba Khamenei, zai ɗora daga inda mahaifinsa Ayatollah Ali Khamenei ya tsaya.

    Putin ya bayyana hakan ne cikin wani saƙon taya murna da aka wallafa a shafin Kremlin, inda ya tabbatar da goyon bayan Rasha ga Iran a wannan lokaci da ƙasar ke fuskantar hare-hare.

    “Ina miƙa gaisuwa ta musamman tare da taya Mojtaba Khamenei murna kan naɗinsa a matsayin jagoran addinin Iran,” in ji Putin.

    Ya ƙara da cewa Rasha za ta ci gaba da kasancewa abokiyar Iran mai aminci tare da ba ta goyon baya ba tare da wata shakka ba.

    Putin ya ce yana da yaƙinin cewa sabon jagoran zai ɗora daga inda mahaifinsa ya tsaya cikin girmamawa, tare da haɗa kan al’ummar Iran a wannan mawuyacin lokaci.

    “A wannan lokaci da Iran ke fuskantar manyan hare-hare, tabbas za a buƙaci ƙarfin zuciya da sadaukarwa.

    “Ina da yaƙinin cewa za ka ci gaba daga inda mahaifinka ya tsaya cikin girmamawa kuma ka haɗa kan al’ummar Iran a wannan mawuyacin lokaci,” in ji shi.

    Aminiya ta ruwaito cewa, majalisar ƙoli ta malaman addini ta Iran, wadda ta ƙunshi mutum 88 kuma take da alhakin naɗa manyan jami’an addini da na siyasar ƙasar bisa kundin tsarin mulkin ƙasar, ce ta zaɓi Mojtaba Khamenei mai shekara 56 a ranar Lahadin da ta gabata.

    Da naɗinsa, Mojtaba ya zama jagoran addinin Iran na uku tun juyin juya halin shekarar 1979, inda ya zama shugaba a wani mawuyacin lokaci na yankin Gabas ta Tsakiya da kuma rashin tabbas a cikin ƙasar.


    [ad_2]

    Source link

  • An Harbe Kwamandan Soja Yayin Da Boko Haram Ta Kai Hari Wani Sansanin Soji

    [ad_1]

    ‘Yan ta’addan Boko Haram sun sake kwace wani sansanin soji a Jihar Borno, inda suka kashe kwamandan sansanin da wasu jami’an soja.

    Sabon harin ya faru ne a Karamar Hukumar Kukawa ta Jihar Borno da sanyin safiyar ranar Litinin.

    • Gwamnatin Tarayya Ta Yabawa Zulum Kan Faɗaɗa Ilimin Fasaha Da Sana’o’i A Borno
    • Wike Ya Amince Da Kashe Naira Biliyan 8.4 Domin Shawo Kan Matsalar Tsaro A Abuja

    Wata majiya daga garin ta bayyana cewa ‘yan ta’addan sun kai hari sansanin sojin ne da misalin karfe 12:30 na dare.

    “Sun shigo garin daga ɓangarori da dama sannan suka kaddamar da hari kan sansanin sojin,” in ji majiyar.

    Wata majiyar tsaro kuma ta ce, ‘yan ta’addan sun fatattaki sojojin daga sansanin, sannan suka kone wasu motocin soja tare da kwashe makamai da alburusai.

    “Ba zan iya bayyana yawan waɗanda suka rasu ba a yanzu, amma abin bakin ciki ne cewa, mun rasa kwamandan sansanin a wannan harin,” in ji ɗaya daga cikin majiyoyin tsaron.

    [ad_2]

    Source link

  • Gwamnatin Tarayya Ta Yabawa Zulum Kan Faɗaɗa Ilimin Fasaha Da Sana’o’i A Borno

    [ad_1]

    Gwamnatin Tarayyar Nijeriya ta yabawa gwamnan Jihar Borno, Babagana Umara Zulum, bisa ƙarfafa Ilimin Fasaha da Horon Sana’o’i a jihar, bayan kammala horar da kusan ɗalibai 3,000 daga cibiyoyin koyon sana’o’i guda tara da ke faɗin jihar.

    Yabon ya fito ne a cikin wata sanarwa da aka fitar ranar Lahadi, wadda Boriowo Folasade, Daraktar Yaɗa Labarai da Hulɗa da Jama’a ta Ma’aikatar Ilimi ta Tarayya, ta sanya wa hannu.

    A cewar sanarwar, Ministan Ilimi, Maruf Tunji Alausa, ya bayyana wannan shiri a matsayin babban mataki na ƙarfafa matasan Nijeriya ta hanyar ba su ƙwarewa masu amfani da za su iya samun aikin yi da su.

    Ministan ya ce: “Wannan shiri da Gwamna Zulum ya ƙaddamar babban mataki ne na bai wa matasan Nijeriya ƙwarewa ta aiki da za su iya dogaro da ita wajen samun abin yi.”

    [ad_2]

    Source link

  • Majalisar Dattawa Za Ta Gayyaci Kyari Kan Zargin Giɓin Kuɗi Har Naira Tiriliyan 210 A NNPCL

    [ad_1]

    Majalisar Dattawan Nijeriya ta jaddada cewa tsohon Babban Darakta na rukunin kamfanin man fetur na kasa, NNPCL, Mele Kyari, tare da wasu tsofaffin manyan jami’an kamfanin mai na ƙasa dole su yi bayani kan giɓin kuɗi da ya kai kusan naira tiriliyan 210 da aka gano a cikin rahotannin binciken kuɗaɗen kamfanin daga shekarar 2017 zuwa 2023.

    Shugaban Kwamitin Majalisar Dattawa kan Asusun Jama’a, Aliyu Wadada, ya ce za a gayyaci tsoffin shugabannin kamfanin domin su bayyana a gaban kwamitin a wani zaman sauraro na jama’a domin su yi karin haske kan batutuwan da aka bankaɗo a rahotannin binciken kuɗin.

    • Wike Ya Amince Da Kashe Naira Biliyan 8.4 Domin Shawo Kan Matsalar Tsaro A Abuja
    • Ƴansanda Sun Daƙile Yunƙurin Garkuwa Da Wasu Masallata A Zamfara

    Wadada ya bayyana hakan ne a ranar Lahadi yayin da yake magana a shirin Politics Today na tashar Channels Television, inda ya jaddada cewa kwamitin ya kuduri aniyar gano gaskiyar abin da ya haifar da wannan giɓin kuɗin.

    A cewarsa: “Za mu gayyace su su bayyana a gaban kwamitin a zaman sauraro na jama’a domin su fayyace gaskiyar batu kan wannan lamari mai cike da cece-kuce, ruɗani kuma wanda ba za a amince da shi ba.

    “Ana kammala bukukuwan Sallah, za mu rubuta musu takardar gayyata ta hannun Babban Manajan Darakta (GMD) na NNPCL,” in ji shi.

    [ad_2]

    Source link

  • An kama tsohon kansila da kilo 40 na tabar wiwi a Legas

    [ad_1]



    Jami’an Hukumar Hana Sha da Fataucin Miyagun Ƙwayoyi ta Ƙasa (NDLEA) sun kama wani tsohon kansila a Jihar Legas kuma mataimaki na musamman ga wani ɗan majalisa, bayan da suka gano kilo 40 na tabar wiwi nau’in skunk a gidansa da ke Ilado a yankin Ibeju-Lekki.

    Kakakin NDLEA, Femi Babafemi, ya bayyana a wata sanarwa ranar Lahadi cewa wanda ake zargin mai suna Sheleru Sadiq Olalekan mai shekara 45, an kama shi ne bayan da jami’an hukumar suka kai samame gidansa sakamakon sahihan bayanan sirri da suka samu.

    A cewarsa, an gano miyagun ƙwayoyin a ɗaya daga cikin ɗakunan gidan, inda a yayin tambayoyi, Olalekan ya amsa cewa ƙwayoyin da aka samu nasa ne kuma gidan da aka same su a ciki nasa ne.

    NDLEA ta ce Olalekan ya kuma tabbatar da cewa ya taɓa yin wa’adin mulki biyu a matsayin kansilan da ya wakilci al’ummar Orimedu a Ƙaramar Hukumar Ibeju-Lekki.

    A wani samame na daban a Abuja kuwa, jami’an NDLEA sun kama wani ɗan kasuwa mai shekara 32, Emeka Hyginus Okwor, wanda ke tafiya daga Obollo-Afor a Jihar Enugu zuwa Zuba a Babban Birnin Tarayya.

    Binciken da aka yi a kayansa ya nuna an ɓoye ƙwayoyi 1,000 na tapentadol a cikin ƙunzugun jarirai.

    Rahotanni sun ce wanda ake zargin ya amsa cewa yana kai kwayoyin ne zuwa ƙauyen Guduwa da ke Ƙaramar Hukumar Gurara ta Jihar Neja, inda yake gudanar da wani shagon sayar da kayan abinci.


    [ad_2]

    Source link