Category: Latest News

  • Ramadan: Lokutan Buda-Baki Da Sahur Na Azumi Na 21

    [ad_1]

    Mota Sahur (Fajr/Imsak) Iftar (Maghrib)
    Abuja 05:13 AM 06:58 PM
    Idan 05:08 na safe 06:52 PM
    Kano 05:09 AM 06:57 PM
    Kaduna 05:13 AM 07:00 PM
    Legas 05:27 AM 07:17 PM
    Maiduguri 05:04 AM 06:37 PM
    Sokoto 05:26 AM 07:10 PM
    Fatakwal 05:18 AM 06:59 PM

    [ad_2]

    Source link

  • Dalilin da na koma jam’iyyar APC — Gwamnan Zamfara

    [ad_1]



    Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya ce rikicin cikin gida da kuma taƙaddamar shari’a da ke addabar jam’iyyar PDP su ne manyan dalilan da suka sa ya fice daga jam’iyyar zuwa APC.

    Mataimakin gwamnan jihar, Mani Mummuni, ne ya sanar da sauya shekar a hukumance ranar Litinin bayan wani taron masu ruwa da tsaki da aka gudanar a gidan gwamnati da ke Gusau.

    A wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan, Sulaiman Bala Idris, ya fitar, ya ce matakin komawa Jam’iyyar APC ya zama dole domin ci gaba da bunƙasa al’umma da kuma kare muradun Jihar Zamfara.

    Sanarwar ta ce shawarar sauya sheƙar ta biyo bayan matsalolin shari’a da rikicin cikin gida da PDP ke fuskanta, wanda ya haddasa jerin ƙalubale da ka iya shafar shirye-shiryen jam’iyyar a zaɓukan shekarar 2027.

    Sanarwar ta ƙara da cewa Gwamna Dauda Lawal ya yi ƙoƙari wajen sasanta ɓangarorin jam’iyyar domin a samu haɗin kai, amma ƙoƙarin samar da sulhu ba tare da zuwa kotu ba bai yi nasara ba.

    Sanarwar ta kuma bayyana cewa gwamnan ya yanke hukuncin sauya sheƙar ne bayan hukuncin da Kotun Ɗaukaka Ƙara da ke Abuja ta yanke ranar Litinin, wanda ya tabbatar da hukuncin Babbar Kotun Tarayya da ta hana Hukumar Zaɓe (INEC) amincewa da sakamakon babban taron jam’iyyar PDP na ƙasa da aka gudanar a Ibadan, Jihar Oyo.

    A cewar sanarwar, gwamnan ya shiga APC ne domin ci gaba da aiwatar da shirinsa na “Ceto da Sake Gina Zamfara” tare da fifita muradun al’ummar jihar.


    [ad_2]

    Source link

  • Matasa Biyu Sun Afka Tafkin Ruwa Yayin Tserewa Masu Ƙwacen Waya A Kano

    [ad_1]

    Matasa biyu sun rasa rayukansu a jihar Kano bayan sun faɗa cikin wani tafki yayin da suke kokarin tserewa wasu da ake zargin masu kwacen waya ne.

    Da take tabbatar da faruwar lamarin, Hukumar Kashe Gobara ta Jihar Kano ta ce abin ya faru ne ranar Juma’a, 6 ga Maris, 2026, a Ring Road Kureken Sani da ke karamar hukumar Kumbotso.

    • APC Na Da Gwamnoni 31 Bayan Sauya Sheƙar Gwamnan Zamfara
    • Kotu Ta Ci Tarar Gwamnatin Kano Miliyan 1 A Shari’arta Da Tsofaffin Kwamishinoni

    Mai magana da yawun hukumar, Saminu Yusuf Abdullahi, ya ce wadanda suka rasun sune Sadiq Isyaku mai shekaru 18 da Auwal Isyaku.

    Ya bayyana cewa an tsamo su daga cikin tafkin a sume, amma daga bisani aka tabbatar da rasuwarsu.

    A cewarsa, an miƙa gawarwakinsu ga mahaifinsu, Ibrahim Shehu, mazaunin Unguwa Uku.

    [ad_2]

    Source link

  • Iran ta kama wani mutum kan zargin yi wa Amurka da Isra’ila leƙen asiri

    [ad_1]



    Ma’aikatar tattara bayanan sirri ta Iran ta sanar da kama mutane 30 da ake zargi da aikata leƙen asiri, ciki har da wani baƙo ɗan ƙasar waje, a rana ta 11 da fara yaƙin Gabas ta Tsakiya.

    Ma’aikatar ta ce cikin waɗanda aka kama akwai wani ɗan ƙasar waje da ake zargi da tura muhimman bayanan tsaro ga wasu gwamnatocin ƙasashen yankin Tekun Fasha guda biyu, waɗanda daga bisani suka miƙa bayanan ga Amurka da Isra’ila.

    Wata sanarwa da aka wallafa a shafin Mizan Online na ma’aikatar shari’a, hukumomin Iran sun ce an kama baƙon mutumin ne a arewa maso gabashin ƙasar.

    Sai dai sanarwar ba ta bayyana ƙasar da mutumin ya fito ba, kuma ba ta fayyace ranar da aka kama shi ba.

    Kazalika, sanarwar ta kuma bayyana cewa wasu mutane 19 daga cikin waɗanda aka kama ana zargin su da zama ma’aikatan jarida da kuma masu hulɗa da masu adawa da gwamnati da ke da alaƙa da Isra’ila.

    Hukumomin Iran ba su bayyana ƙasashen da ake zargin suna da hannu a lamarin ba, haka kuma ba su bayar da cikakken bayani kan sauran waɗanda aka kama ba.


    [ad_2]

    Source link

  • Kotu Ta Ci Tarar Gwamnatin Kano Miliyan 1 A Shari’arta Da Tsofaffin Kwamishinoni

    [ad_1]

    Wata kotun ma’aikata da ke zamanta a Jihar Kano, ta umarci gwamnatin jihar ta biya tarar naira miliyan ɗaya a shari’ar da wasu tsofaffin kwamishinonin jihar suka shigar kan motocin gwamnati da aka ba su lokacin da suke riƙe da muƙami.

    Kotun, wadda Mahmood Abba Namtari ke jagoranta, ta yanke hukuncin ne a ranar Talata bayan lauyan gwamnati ya nemi a ɗage shari’ar domin samun lokacin da zai shirya martaninsa.

    • Rikice-rikicen Da Suka Addabi PDP Ne Suka Sa Na Koma APC — Gwamnan Zamfara
    • Ramadan: ‘Yansanda Sun Buƙaci A Sanya Ido A Kano A Goman Ƙarshe

    Lauyan gwamnati, Barista S. U. Jibril, ya shaida wa kotu cewa an sanar da shi batun shari’ar ne a ranar Litinin da rana, don haka bai samu isasshen lokaci ba don shirya takardun da ake buƙata.

    Sai dai lauyan masu ƙara, Suraj Sa’ed (SAN), ya ce ba su da matsala kan ɗage shari’ar, amma ya roƙi kotu ta saka tarar kuɗi tun an riga an miƙa wa gwamnati takardun shari’ar.

    Mai shari’a Namtari ya ce bayanai sun nuna an miƙa takardun tun a ranar 26 ga watan Fabrairu.

    Daga nan kotun ta umarci a biya Naira 200,000 a kowace daga cikin shari’o’i biyar, wanda ya kai jimillar kuɗin zuwa Naira miliyan ɗaya.

    Sannan ta ɗage shari’ar zuwa ranar 28 ga watan Afrilu, 2026.

    Tsofaffin kwamishinonin suna neman kotu ta hana gwamnatin jihar ƙwace motocin gwamnati da aka ba su lokacin da suke riƙe da muƙamansu.

    [ad_2]

    Source link

  • Sojoji sun kashe ‘yan ta’adda 3, sun ƙwato makamai a dajin Sakkwato

    [ad_1]



    Dakarun Sojojin Najeriya da ke ƙarƙashin rundunar Fansan Yamma, sun kashe wasu ‘yan ta’adda uku tare da ƙwato makamai yayin wani samame a dajin Kadam da ke Ƙaramar Hukumar Tangaza a Jihar Sakkwato.

    Mukaddashin Mataimakin Daraktan Hulɗa da Jama’a na rundunar, Laftanar Kanar Olaniyi Osoba ne ya bayyana hakan cikin wata sanarwa a ranar Talata.

    Ya ce dakarun wata bataliya ta musamman ce suka gudanar da farmakin bayan samun bayanan sirri kan matsugunnin ‘yan ta’addan.

    Olaniyi ya ce bayanan sirrin sun nuna cewa sama da ‘yan ta’adda 100 sun taru a cikin dajin domin shirya hare-hare da sace mutane a garuruwan da ke kewaye, lamarin da ya sa dakarun suka kai musu farmaki inda aka gwabza faɗa mai zafi.

    A cewarsa, bayan artabun, an kashe ‘yan ta’adda uku yayin da wasu suka tsere da raunukan harbi, yayin da sojojin suka ƙwato bindigar PKT, bindigogi AK-47 guda biyu, harsasai, rediyoyin sadarwa, babura uku da wayar hannu, inda ya ƙara da cewa ana ci gaba da sintiri domin kamo sauran ‘yan ta’addan.


    [ad_2]

    Source link

  • Za mu kawo ƙarshen yaƙin Iran nan ba da daɗewa ba — Trump

    [ad_1]



    Shugaban Amurka Donald Trump ya ce nan ba da daɗewa ba za su kawo ƙarshen hare-haren da suke kaiwa kan Iran, yana mai ƙoƙarin kwantar da hankalin kasuwannin duniya da yaƙin Gabas ta Tsakiya ya girgiza.

    Trump ya bayyana hakan ne a wani taron manema labarai a jihar Florida, inda ya ce yaƙin zai kasance na ɗan lokaci kaɗan.

    “(Yaƙin) zai ƙare nan ba da daɗewa ba, kuma idan ya sake faruwa, za su (Iran) fuskanci farmaki mafi tsanani,” in ji shi.

    Maganar tasa ta taimaka wajen farfaɗo da kasuwannin hannayen jari, inda kasuwar Wall Street ta farfaɗo, yayin da kasuwannin Tokyo da Seoul ma suka buɗe da ƙarfi duk da ci gaba da tashin hankali a yankin.

    A gefe guda kuma, farashin ɗanyen mai ya sauka da kusan kashi biyar cikin ɗari, bayan da ya haura dala 100 kan kowace ganga a ranar Litinin — mafi girma tun bayan yaƙin Rasha da Ukraine a 2022.

    Sai dai rundunar juyin-juya hali ta Iran ta mayar da martani, tana cewa ita ce za ta yanke hukunci kan lokacin da za a kawo ƙarshen yaƙin, ba Amurka ba.

    Sabon jagoran addinin, Iran Mojtaba Khamenei, ɗan tsohon jagoran Ayatollah Ali Khamenei, ya fara aikinsa da ƙaddamar da sabbin hare-haren makamai masu linzami da jiragen marasa matuƙa kan Saudiyya, Bahrain, Qatar, Haɗɗaɗiyar Daular Larabawa da kuma Isra’ila.

    Haka kuma Iran ta ci gaba da rufe Mashigar Hormuz, wadda kusan kashi 20 na man fetur na duniya ke wucewa ta cikinta, lamarin da ya jefa kasuwannin duniya cikin fargaba.

    A wani ɓangaren kuma, shugaban Faransa Emmanuel Macron ya ce ƙasarsa tare da abokan hulɗarta na shirin wani gudanar da wani aikin soji na haɗin gwiwa domin sake buɗe mashigar ruwan bayan rikicin ya lafa.

    Yaƙin ya kuma ƙara tsananta a Lebanon, inda musayar wuta tsakanin Isra’ila da ƙungiyar Hezbollah ta kashe aƙalla mutum 486 tare da jikkata sama da 1,300 tun farkon watan Maris.


    [ad_2]

    Source link

  • Rikice-rikicen Da Suka Addabi PDP Ne Suka Sa Na Koma APC — Gwamnan Zamfara

    [ad_1]

    Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya bayyana cewa rikicin cikin gida da kuma shari’o’in da suka dabaibaye tsohuwar jam’iyyarsa ta PDP ne suka sa ya fice daga jam’iyyar ya koma APC.

    A ranar Litinin ne gwamnan ya sanar da sauya sheƙarsa daga PDP zuwa jam’iyya mai mulki ta APC a hukumance.

    • Ramadan: ‘Yansanda Sun Buƙaci A Sanya Ido A Kano A Goman Ƙarshe
    • APC Na Da Gwamnoni 31 Bayan Sauya Sheƙar Gwamnan Zamfara

    Hakan ya faru ne bayan wani taron masu ruwa da tsaki da aka gudanar a gidan gwamnatin jihar da ke Gusau.

    A wata sanarwa da kakakin gwamnan, Sulaiman Bala Idris, ya fitar, ya ce gwamnan ya ɗauki wannan mataki ne domin muradun al’ummar Zamfara.

    Sanarwar ta ƙara da cewa an yanke shawarar komawa APC ne bayan tattaunawa da masu ruwa da tsaki a jihar, musamman ganin matsalolin shari’a da jam’iyyar PDP ke fuskanta a halin yanzu.

    Gwamna Dauda Lawal ya ce ya yi ƙoƙari sosai domin sasanta rikicin da ke tsakanin ɓangarorin PDP, domin a samu haɗin kai kuma jam’iyyar ta samu damar tsayar da ‘yan takara a zaɓuka masu zuwa.

    Sai dai ya ce duk ƙoƙarin da aka yi na sasanci bai yi nasara ba.

    Wannan ne ya jawo yawaitar shari’o’i da ka iya kawo cikas ga ‘yan siyasa da ke shirin tsayawa takara a zaɓen 2027.

    Ficewar Dauda Lawal daga PDP na zuwa ne mako guda bayan gwamnan Adamawa ya sauya sheƙa daga PDP zuwa APC.

    A yanzu haka PDP na da gwamnoni biyu kacal, yayin da APC ke da gwamnoni 31 a faɗin ƙasar.

    [ad_2]

    Source link

  • Ramadan: ‘Yansanda Sun Buƙaci A Sanya Ido A Kano A Goman Ƙarshe

    [ad_1]

    Rundunar ‘Yansandan Nijeriya da ke hedikwatar Shiyya ta Ɗaya a Jihar Kano, ta buƙaci mazauna jihar, musamman Musulmi, su kasance cikin shiri da sanya ido a kwanakin goman karshe na watan Ramadan.

    A cikin wata sanarwar tsaro da aka fitar ranar Litinin, kakakin rundunar a shiyyar, DSP Abdullahi Hussaini, ya ce wannan gargaɗi ya fito ne daga Mataimakin Sufeto Janar na ‘yansanda mai kula da shiyyar, Garba Ahmed.

    • SAHUR (Falalarsa Da Fa’idojinsa) Na 21
    • Majalisar Dattawa Za Ta Gayyaci Kyari Kan Zargin Giɓin Kuɗi Har Naira Tiriliyan 210 A NNPCL

    Ya tunatar da masu ibada da su kasance masu lura da tsaro, domin a wannan lokaci mutane da dama kan halarci salla cikin dare.

    Rundunar ‘yansandan ta ce wasu ɓata-gari na iya amfani da wannan lokaci wajen aikata laifuka.

    Saboda haka, an shawarci masu ibada su guji bin hanyoyin da babu mutane, su kula da kayayyakinsu, sannan su riƙa kai rahoton duk wani abun zargi ga ofishin ‘yansanda mafi kusa.

    Rundunar ta kuma tabbatar wa da jama’a cewa tana ci gaba da ɗaukar matakai domin kare rayuka da dukiyoyinsu.

    A gefe guda ta buƙaci al’umma su ci gaba da haɗa kai da jami’an tsaro domin tabbatar da zaman lafiya.

    [ad_2]

    Source link

  • Jami’an Tsaro Sun Kashe ‘Yan Bindiga 5 A Jihar Zamfara

    [ad_1]

    An kashe wasu da ake zargin ‘yan bindiga biyar a wani samame da rundunar Joint Task Force (JTF) ta kai a ƙaramar hukumar Tsafe da ke Jihar Zamfara.

    Wannan na cikin wani saƙo da masanin harkokin tsaro, Zagazola Makama, ya wallafa a shafinsa na X a ranar Litinin.

    • Yaƙin Amurka Da Iran Na Iya Tura Farashin Litar Fetur Zuwa N2,000 A Nijeriya – PETROAN
    • Majalisar Dattawa Za Ta Gayyaci Kyari Kan Zargin Giɓin Kuɗi Har Naira Tiriliyan 210 A NNPCL

    A cewarsa, jami’an tsaro sun yi arangama da ‘yan bindigar a lokacin samamen, lamarin da ya yi sanadin mutuwar mutane biyar da ake zargin ‘yan bindiga ne.

    Ya ƙara da cewa jami’an tsaron sun kuma ƙwato wasu kayayyaki daga wajen da aka kai samamen.

    Makama ya ce an gudanar da aikin ne a Kan Biri da ke wajen garin Kwaren Ganuwa a ƙaramar hukumar Tsafe ta Jihar Zamfara.

    Ya ce a yayin samamen, jami’an tsaro sun ƙwato babura da kuma bindigogi daga hannun waɗanda ake zargin.

    Makama ya kuma yaba wa rundunar JTF bisa yadda suke sadaukar da rayuwarsu a kullum wajen yaƙi da ƙungiyoyi masu ɗauke da makamai da kuma kare al’ummomi.

    [ad_2]

    Source link