Category: Latest News

  • Binciken CGTN: Galibin Amurkawa Na Ganin Darajar Dangantaka Mai Karko Da Sin

    [ad_1]

    Ministan harkokin wajen kasar Sin Wang Yi ya bayyana a yau Lahadin cewa, ya kamata kasashen Sin da Amurka su himmatu wajen mutunta juna, da kiyaye zaman lafiya, da kuma kokarin tabbatar da hadin gwiwa ta samun nasara ga ko wane bangare a tsakanin kasashen biyu.

    Wang ya bayyana hakan ne a wani taron manema labarai a gefen taro na hudu na majalisar wakilan jama’ar kasar Sin ta 14. Wani binciken jin ra’ayoyi na baya-bayan nan da CGTN ta yi a tsakanin Amurkawa 2,001, ya nuna galibi sun amince da cewa, samun zaman lafiya mai dorewa da kyakkyawan kuzari a huldar da ke tsakanin kasashen biyu na da matukar muhimmanci, tare da bayyana kwakkwaran fatan jama’a na ganin ana samun karin hadin gwiwa na cin moriyar juna, da fadada mu’amala tsakanin kasashen biyu.

    Binciken ya nuna kwarin gwiwa da amincewar bangarori mabambanta game da darajar dangantakar Sin da Amurka kamar haka: kashi 83.1 cikin dari na masu bayyana ra’ayoyin suna ganin ci gaba da kyautata alaka da kasar Sin na da matukar muhimmanci. (Mai fassara: Abdulrazaq Yahuza Jere)

    [ad_2]

    Source link

  • Muhimman ayyuka 8 a goman ƙarshe na Ramadan

    [ad_1]



    A yayin da aka shiga kwana goman ƙarshe a watan Ramadan, ga tunarwar wasu muhimman ayyukan lada da ya kamata a dage da su a cikin watan mai alfarma.

    Fitaccen malamin Musulunci, Sheikh Aminu Ibrahim Daurawa, ya bayyana cewa riƙo da su yana da muhimmanci saboda tarin lada da aka tanadar wa mai aikata su:

    1. Itikafi: Ana so mutum idan mutum yana da hali ana ya shiga Itikafi, inda da lazimci bautar Allah. Mutum, namiji ko mace, na iya Itikafi na tsawon kwanakin ko na iya abin da ya sawwaka.
    2. Neman daren Lailatul Kadar: Mutum ya dage wajen kirdado da neman dacewa da daren Lailatul Kadari, ta hanyar gabatar da salloli da addu’o’i da sauran ayyukan ibada, musamman a dararen mara a goman karshen watan Ramadan.
    3. Sallah: Musamman Sallar Tarawihi da Tahajjud, baya ga yin sallolin farilla a cikin jam’i, da kuma yin nafilolin da ake yi kafin ko bayan sallolin na farilla.
    4. Karatun Al-Kur’ani: A dage a yawaita karatun Al-Kur’ani domin a cikin watan Ramadan aka saukar da shi, a daren Lailatul Kadar, cikin kwana goman karshe.
    5. Addu’o’i: A dage da addu’o’in neman garafa da rahamar Allah da aljannah da kuma dacewa da alherin duniya da lahira da kuma neman tsari daga wuta da kuma sharrin duniya da na lahira. Mutum na iya yin addu’a a lokutan da ake amsa addu’o’i kamar lokacin Sahur ko bude-bakin da lokacin da ake cikin azumin da cikin sujada ko a cikin sulusin karshe da dare da sauransu.
    6. Umrah: Hadisi ya nuna wanda ya yi Umra a cikin goman karshe na Ramadan zai samu ladar yin aikin Hajji tare da Manzon Allah (SAW).
    7. Zakka: Ana so duk Musulmi mai hali ya fitar da Zakkar Kono ya ba wa mabukata. Magidanci da da da hali zai fitar da sa’i daya (Mudun Nabi hudu) na hatsi, haka kuma zai fitar wa iyalansa da duk wanda yake ciyarwa. Ana iya fitarwa a bayar daga ranar 28 ga Ramadan har zuwa lokacin tafiya masallacin idi ranar Karamar Sallah.
    8. Kabbarori: Ana yin kabbarori daga bayan faduwar ranar jajibirin Karamar Sallah, har zuwa lokacin da za a idar da sallar idin.


    [ad_2]

    Source link

  • Ramadan: Lokutan Buda-Baki Da Sahur Na Azumi Na 19

    [ad_1]

    Mota Sahur (Fajr/Imsak) Iftar (Maghrib)
    Abuja 05:15 AM 06:56 PM
    Idan 05:10 na safe 06:50 PM
    Kano 05:11 AM 06:55 PM
    Kaduna 05:15 AM 06:58 PM
    Legas 05:29 AM 07:15 PM
    Maiduguri 05:06 AM 06:35 PM
    Sokoto 05:28 AM 07:08 PM
    Fatakwal 05:20 na safe 06:57 PM

    [ad_2]

    Source link

  • Yanayin kasuwa ne ya sa farashin man fetur ya tashi — NMDPRA

    [ad_1]



    Hukumar Kula da Harkokin Man Fetur ta Najeriya (NMDPRA), ta ce sauyin farashin mai da aka samu a gidajen mai ya samo asali ne da yadda kasuwa ke tafiya a yanzu.

    Mai magana da yawun hukumar, George Ene-Ita ne, ya bayyana hakan a wata hira da Kamfanin Dillacin Labarai na Najeriya (NAN) a Abuja.

    Masu ababen hawa da dama a Abuja sun nuna damuwa kan ƙarin farashin man fetur, wanda a baya ake sayarwa tsakanin Naira 875 zuwa Naira 880 kan kowace lita.

    A yanzu haka, ’yan kasuwa masu zaman kansu suna sayar da fetur tsakanin Naira 960 zuwa Naira 1,000 ko sama da haka kan kowace lita.

    Gidajen mai mallakin kamfanin man fetur na Najeriya (NNPCL) kuwa suna sayarwa kusan Naira 960 kan kowace lita.

    Ene-Ita, ya ce bambancin farashin da ake samu a sassa daban-daban na ƙasar nan ba shi da alaƙa da gwamnati, sai don yanayin kasuwa.

    “Najeriya tana amfani da tsarin sayar da man fetur ta hanyar bai wa kasuwa ’yancin gashin kai. Don haka sauyin farashin mai yana faruwa ne saboda yadda kasuwa ke tafiya,” in ji shi.

    Ya ƙara da cewa a irin wannan tsarin, farashin mai yana canzawa ne gwargwadon yanayin kasuwa.

    Ya kuma bayyana cewa manufar wannan tsari ita ce ƙarfafa gasa tsakanin ’yan kasuwa, inganta aiki, da kuma jawo ƙarin jari a ɓangaren man fetur da iskar gas a Najeriya.


    [ad_2]

    Source link

  • Wane Ne Alireza Aarafi, Shugaban Kwamitin Zaɓen Sabon Ayatollah A Iran?

    [ad_1]

    Hukumomin Iran sun sanar da Alireza Aarafi, wanda wakili ne a Majalisar Magabatan ƙasar, domin ya jagoranci majalisar tafiyar da mulkin riƙon-ƙwarya na ƙasar.

    Bayan tabbatar da rasuwar Ali Khamenei a ranar 29 ga watan Fabarairu, za a kafa majalisar riƙon ƙwarya ta ƙasar, bisa dogaro da sashe na 111 na kundin tsarin mulkin ƙasar, wadda za ta ƙunshi shugaban ƙasa da babban alƙalin alƙalai da kuma wani wakili daga Majalisar Magabatan ƙasar.

    • Yaƙin Iran: Gwamnatin Tarayya Ta Gargaɗi Ƴan Nijeriya Kan Matakan Tsaro A Yankin Gabas
    • Dalilin Da Ya Sa Muka Kai Wa Iran Hari — Donald Trump

    Bayan sanar da Mista Aarafi a matsayin mamban wannan majalisa, ana sa ran mutanen uku ne za su karɓi ragamar tafiyar da lamurran ƙasar har sai majalisar masana ta ƙasar ta sanar da sabon jagoran addinin ƙasar.

    Sashe na 111 na kundin tsarin mulki ya bayyana cewa, daga lokacin rasuwar jagoran addini zuwa lokacin da Majalisar Masana za ta sanar da sabon Jagora, Majalisar wasu mutane guda uku ne za su tafiyar da ayyukan ofishin Jagora.

    Wakilan wannan majalisa su ne Shugaban ƙasa, da Babban alƙalin ƙasa da kuma wakilin Majalisar Magabata wanda Majalisar lura da buƙatun gaggawa ke zaɓa.

    Sai dai, wannan Majalisa ta Mutane uku ba ta da cikakken iko, kuma tana buƙatar amincewar kashi uku cikin huɗu na Majalisar lura da buƙatun gaggawa kafin aiwatar da abubuwa kamar haka:

    Kasancewar an kashe babban kwamandan rundunar juyin juya halin ƙasar, da shugaban rundunar tsaro ta ƙasar da kuma da dama daga cikin manyan hafsoshin sojin ƙasar, ana sa ran majalisar shugabancin ta riƙon ƙwarya za ta riƙa zartar da manufofi ne ta hanyar samun amincewar kashi uku bisa huɗu na wakilan majalisar ƙasar.

    Wasu kafofin yaɗa labarai na ciki da wajen ƙasar, ciki har da jaridar New York Times cewa an samar da “mataki huɗu na magadan jagororin” ƙasar, sai dai kafofin yaɗa labarai da ke kusa da gwamnatin ƙasar sun bayyana lamarin a matsayin “farfagandar yaƙi.”

    Wane ne Alireza Aarafi?

    Bayanai daga kafofin yaɗa labaran Iran sun ce an haifi Alireza Aarafi ne a shekara ta 1955 a birnin Meybod da ke lardin Yazd.

    Mahaifinsa Mohammad Ebrahim Aarafi shahararren malami ne a lokacin rayuwarsa, wanda ya yi adawa da jagorancin sarki Pahlaɓi, kuma yana da alaƙa ta ƙut da ƙut da malaman da ke kusa da Ruhollah Khomeini.

    Mahaifiyarsa ‘ya ce ga Sheikh Kazem Malek Afzal Ardakani.

    Alireza Aarafi ya yi karatunsa na farko-farko ne, kamar ilimin Ƙur’ani da adabi da harkar shari’a a wurin mahaifinsa da kuma wasu malamai.

    Ya koma birnin Ƙom a shekarar 1960, sannan bayan kammala karatun elemantare ya fara karatun koyon maluntan addini a shekarar 1977.

    Bayan kammala matakin farko, sai ya fara tafiya wurin manyan malaman shi’a daban-daban ya yi karatun shari’a, ciki har da Morteza Haeri, da Mohammad Fazel Lankarani, da Hossein Ɓahid Khorasani, da Jaɓad Tabrizi, da Ali Meshkini, da kuma Hassan Hassanzadeh Amoli, sannan ya yi karatun falsafa a wurin Mohammad Taƙi Misbah Yazdi.

    Ya kuma yi karatun harkokin addini a tsangayoyi da jami’o’i kamar Allameh Tabataba’i da Tarbiat Modarres.

    Alireza Aarafi ya kasance cikin harkokin siyasa tun yana matashi, kuma ya bi sahun mahaifinsa wajen adawa da gwamnatin Pahlaɓi.

    An kama shi tare da ɗaure shi a gidan yari tun yana da shekara 16.

    A shekarar 1979, an kafa wata ƙungiyar mai lura da ɗalibai waɗanda ba ƴan asalin ƙasar Iran ba a cibiyar karatun addini ta Ƙom.

    Wadda daga baya ƙungiyar ta zama ‘Cibiyar Kimiyyar Musulunci ta Duniya’, inda ta koma ƙarƙashin kulawar jagoran addini na Iran.

    A shekara ta 2002 ne aka naɗa Alireza Aarafi a matsayin shugaban cibiyar bisa amincewar Ayatollah Ali Khamenei.

    Yana daga cikin iyayen jami’ar Kimiyyar Ƙur’ani da ilimi.

    Aarafi ya kasance limamin Juma’a na Meybod tun daga shekara ta 1992, kuma an naɗa shi limamin juma’a na Ƙom a 1994.

    Shi mamba ne a ƙungiyar malaman cibiyar horar da malaman addini ta Ƙom.

    Mista Aarafi ya yi takarar shiga majalisar ƙwararru ta Iran a zaɓen shekara ta 2015 domin wakiltar mazaɓar Tehran, sai dai bai samu nasara ba.

    Ya sake gwada yin takara a zaɓukan tsakiyar zango, inda ya samu nasara, domin wakiltar Tehran.

    Ya samu shiga majalisar ne karon farko daga Tehran a zaɓen da aka yi a watan Maris na 2023, inda ya samu ƙuri’a 888,618.

    A ranar 14 ga watan Yulin 2019 aka naɗa Mista Aarafi zuwa Majalisar Magabata bisa amincewar Ali Khamenei.

    Daga Majalisar Masana zuwa jagoran riƙo

    A shekarun baya-bayan nan ne mutane suka fara sanin Alireza Aarafi, a baya idan za a ambace shi a labarai, akan kira shi da laƙabin “Hujjat al-Islam”, amma a yanzu za a riƙa masa laƙabi da “Ayatollah”.

    Alireza na cikin mutanen da Ali Khamenei ya amince da su kuma yana cikin na kusa da shi. Wannan karɓuwa da ya samu a wurin jagoran addinin ta sanya darajarsa ta riƙa ɗagawa, har ya kai ga inda ake ambaton sunansa a matsayin wanda zai iya gadon Ali Khamenei.

    [ad_2]

    Source link

  • Yadda Aka Gano Ƙasusuwan Dabba Mai Shekara Miliyan 100 A Nijar

    [ad_1]

    Wata tawagar masu bincike da ke aiki a yankin Sahara na Jamhuriyar Nijar sun sanar da gano ƙasusuwan dabbar Dinosaur wadda ta yi rayuwa sama da shekara miliyan 100 da suka shuɗe.

    Wasu masu bincike 20 ne daga jami’ar jihar Chicago ƙarƙashin jagorancin Dr. Paul Sereno suka gano ƙasusuwan, kuma sun ce abu ne mai muhimmanci: zai zama ɗaya daga cikin hujjoji na ƙasusuwan wata dabba da aka gano a cikin sama da ƙarni.

    • Sojoji Sun Ƙwato Dabbobi 257 Da Aka Sace A Kano
    • Yunkurin Kasar Amurka Na “Neman Cin Nasara” Ya Sa Sauran Kasashe Yin Watsi Da Ita

    A ƙarƙashin tsananin zafi da ake yi a yankin na Sahara, masu binciken suka gano sauran ƙasusuwan dabbar ta Dinosaur, wadda ake ɗauka a matsayin wata dabba ta daban a tsawon ƙarni.

    Tafiyar da masu binciken suka yi ƙarƙashin jagorancin masanin halittu Dr. Paul Sereno, na jami’ar Chicago, ya sake haifar da muhawara kan wanzuwar dabbar Dinosaur a Afirka kuma ya bayyana abin da ya daɗe a ɓoye a cikin Saharar.

    A tsakiyar Sahara da babu kowa…

    Tawagar masu binciken sun shafe tsawon kwanaki suna yawo cikin Sahara ba tare da sun san inda za su nufa ba, ga ƙura da ƙishirwa – sai dai ba su sani ba a she akwai babban abin da za su gano a gaba.

    A 2019, sun koma Jamhuriyar Nijar domin bincike a wani wuri da aka yi musu bayani a kai.

    A lokacin ne wani abu da suka gamu da shi ya so kawo musu cikas.

    “Wani mutun ne ya shiga sansaninmu. Ya yi kama da mutum-mutumin ƴan ƙabilar Tuareg. Yana ɗauke da adda a bayansa kuma yana zaune kusa da wata mota ƙirar Honda. Yana magan da yaruka daban-daban. Ya faɗa mana cewa zai kai mu wani wuri mai nisa,” a cewar Dr Paul.

    Ba tare da wata-wata ba, tawagar ta aminta da shi. Sun yi ta keta sahara na tsawon kwana ɗaya da rabi har man ɗin su ya kusa ƙarewa. Daga ƙarshe, mutumin ya jagorance su zuwa wurin da ƙasusuwan suke a tsakiyar Sahara.

    “Muna da sauran rabin sa’a kafin nan muka juya don tsira,” kamar yadda mai binciken ya bayyana. Masana kimiyyar sun yi aiki cikin matsi, inda suka yi ta kwan-gaba kwan-baya domin gano wasu ƙkasusuwa da kuma gane wurin da suke.

    Bayan komawa ɗakin gwaje-gwaje, sun cika da mamaki: sun gano cewa ƙasusuwan dabbar Dinosaur ne wadda ta yi rayuwa sama da shekara miliyan 100 da suka shuɗe.

    Gano sabon na’uin halittu

    Lokacin da harkoki a duniya suka tsaya cik a 2019 sakamakon annobar Korona, hakan ya shafi binciken da Dr. Paul da tawagarsa ke yi inda suka dakata har na tsawon shekara biyu.

    “Daga ƙarshe lokaci ya zo da muka sake haɗa kayanmu don komawa bincike,” in ji Paul. Ya ce a lokacin burinsu shi ne su koma don tattara waɗannan ƙasusuwa son ransu.

    Ba su daɗe da komawa ba suka fara gano ƙasusuwan. “Cikin ƙasa da sa’a ɗaya da isar mu, wani ya zo yana gudu a gare ni yana cewa: ‘Ya kamata ku ga wannan abu!…kamar yadda Paul ya tuna.

    Daga nan farin ciki ya fara rufe su. Sa’o’i biyu bayan haka, wani mai bincike ya gano wani ƙashi a cikin ƙasa. “Ya tambaye ni mene ne. Ƙashin dabbar ta Dinosaur ne. Mun yi matuƙar kaɗuwa a lokacin,”in ji shugaban masu binciken.

    “Babu wanda ya taɓa ganin irin ƙashin,” in ji shi.

    Masu binciken sun ɗauki hotunan ƙasusuwan ta kowane ɓangare domin kafa hujja kan bincikensu.

    Tafiya zuwa cikin Sahara

    Wannan sabon na’ui na dabbar Dinosaur da aka gano a saharar Nijar za ta taimaka wajen ƙara ilimi irin na’uin dabbobin da ake da su.

    A cewar Paul, dabbar ta fi kama da wasu dabbobi maimakon waɗanda ke rayuwa a cikin ruwa. Tsawonsa ya kai mita 12u, kuma yana da damar afka wa cikin ruwa da kuma a fili,” in ji shi.

    Dabbar ba ta iya ninƙaya sosai ba a cikin ruwa, ba kamar yadda wasu bincike suka nuna ba. “Ba ta iya yawo sosai a cikin ruwa ba kamar sauran dabbobi, tana bin koguna inda take cin kifaye a matsayin abincinta.

    Binciken da aka gano a Nijar ɗin ya sha bamban da wanda aka yi a tarihi a arewacin Amurka.

    Ga masu binciken, wannan farawa ne kaɗai. “Wannan shi ne na farko a cikin dogon bincike kan ɓacewar dabbar a duniya,” in ji shi.

    Me ya sa binciken ke da muhimmanci?

    Ga Dakta Paul Sereno, binciken ya wuce na ɓurbushin halittu kaɗai. Yana ba da labarin wata tafiyar binciken kimiyya mai muhimmanci, kuma ya buɗe sabon babi a tarihin dabbar Dinosaur.

    Mai binciken ya bar Ingila tare da tawagarsa a cikin wata tsohuwar mota ƙirar Land Roɓers, inda suka nufi wani yanki mai haɗari a duniya. Sai dai balaguron da zai gano wani abu mai muhimmanci.

    “Kamar yadda za ku iya gani a cikin hotunan da muka ɗauka, ina son motar sosai kuma na kasance ina lallaɓa ta tsawon shekara 30. Ita ma kamar Dinosaur suke,” ya faɗa cikin barkwanci. Motar ta kai mu zuwa cikin Sahara da kuma dawo da mu ba tare da an samu matsala ba

    Sun fara tashi ne daga birnin Southampton da ke Ingila, inda suka isa saharar Nijar – wani wuri da yake ganin ba a yin bincike a cikinsa yadda ya kamata.

    “A farkon rayuwata na gano wani abu ɗaya: yankin Sahara shi ne wuri ɗaya da ya rage da a ba yi bincike kan dabbobin Dinosaur da ke cikinsa ba,” in ji shi.

    Yayin binciken, jami’an sun cire ƙasusuwa kusan tan 55 daga tsakiyar Sahara. Wanda kuma shi ne irinsa na farko a yankin da ba shi da ababen more rayuwa.

    Amma ga Sereno, abu mafi mahimmanci shi ne. “Har yanzu akwai abubuwa da yawa da ya kamata a yi bincike a kai. Muna matakin farko na gano yadda dabbobin Dinosaur na Afirka suke,” ya faɗa cikin farin ciki.

    Mu ciro muku daga BBC Hausa

    [ad_2]

    Source link

  • Sojoji sun ƙaryata rahoton kashe dakarunsu 40 a Borno

    [ad_1]



    Rundunar Sojin Najeriya ta ƙaryata rahotannin da ke cewa an kashe sojoji sama da 40 a hare-haren da Boko Haram ta kai a Jihar Borno.

    Mai magana da yawun rundunar Operation HADIN KAI a Arewa Maso Gabas, Laftanar Kanal Sani Uba ne, ya bayyana hakan.

    Ya ce rahoton da wata kafar sadarwa ta wallafa ya wuce gona da iri kuma ba a tabbatar da sahihancinsa ba, don haka ya buƙaci jama’a su yi watsi da shi.

    “Rahoton da ke cewa an kashe sojoji sama da 40 a hare-haren ta’addanci da aka kai a Borno ba gaskiya ba ne, kuma ya dogara ne kan bayanai da ba a tabbatar da su ba,” in ji Uba.

    Ya bayyana cewa hare-haren sun faru ne bayan ragowar mayaƙan Boko Haram da aka fatattaka daga dajin Sambisa suka sake haɗuwa suka kai hare-hare kan al’ummomi da sansanonin sojoji a yankunan Konduga, Ngoshe, Mainok da Jakana.

    Ya ƙara da cewa sojojin da ke wajen sun yi gaggawar mayar da martani tare da kare al’ummomin da aka kai wa hari.

    “Sojojinmu sun yi jarumtaka wajen daƙile harin ’yan ta’addan da kuma kare al’ummomin.

    “An kashe wasu daga cikin ’yan ta’addan a yayin artabun, amma abin takaici wani kwamandan runduna da wasu sojoji sun rasa rayukansu,” in ji shi.

    Rundunar sojin ta kuma ce ba a fatattaki sojojin ba kamar yadda rahoton ya nuna, domin sun fafata da maharan domin kare jama’ar yankin.

    Babban Hafsan Sojin Kasa, Laftanar Janar Waidi Shaibu, ya ziyarci sojojin da ke aiki a Maiduguri, inda ya ba da umarnin ƙara tura sojoji da kayan aiki domin ƙarfafa yaƙi da ’yan ta’adda.

    Rundunar sojin ta tabbatar wa ’yan Najeriya cewa za ta ci gaba da kai farmaki har sai ta murƙushe dukkanin ƙungiyoyin ta’addanci.


    [ad_2]

    Source link

  • Matasa A Jihar Nasarawa Sun Buƙaci Gwamnati Ta Inganta Wutar Lantarki

    [ad_1]

    A ranar Litinin da ta gabata ne, matasa suka fita kan titunan garin Lafia, Babban Birnin Jihar Nasarawa, suna neman a inganta musu wutar lantarki a faɗin jihar.

    An ga mazauna garin ɗauke da alluna tare kuma da rera waƙoƙi, kan abin da suka bayyana a matsayin rashin samar da wutar lantarki da Kamfanin Rarraba Wutar Lantarki ta Abuja (AEDC) ya yi.

    • Zan Tabbatar Duk Ƴan Dakon Hatsi A Nassarawa Sun Mallaki Katin Zaɓe — Alhaji Danji
    • Kotu Ta Dakatar Da Yunkurin Aminu Ado Bayero Na Gyaran Fadar Nassarawa

    Har ila yau, sun zargi kamfanin rarraba wutar da “sanya su a duhu” duk da matsalolin da mazauna yankin suke fama da su.

    Jagoran masu zanga-zangar, Kwamared Ibrahim Abdullahi Attama, ya ce; babban birnin jihar, ya daɗe yana fama da matsalar rashin isasshiyar wutar lantarki, yana mai bayyana lamarin a matsayin wanda yake gurgunta tattalin arziƙi da walwalar al’umma.

    Ya ƙara da cewa, daɗewar da aka yi ana fama da matsalar rashin tsaro da kuma gurgunta ƙananan sana’o’i, yana da alaƙa da wannan matsala.

    “A duk al’ummar da babu haske a tare da ita, babu rayuwa mai daɗi, domin kuwa kasuwanci yana rushewa, rashin tsaro yana ƙaruwa, sannan kuma mazauna yankin suna fama da buƙatu iri daban-daban,” in ji shi.

    Kwamared Atama ya lura cewa, duk da cewa; tana da muhimmanci da kuma tasiri ga tattalin arziƙin ƙasar, amma rabon wutar lantarkin ga jihar, ko kaɗan bai isa ba, musamman domin biyan buƙatun da ake da su, wanda hakan ke haifar da durƙusar da ƙananan sa’o’i da kuma rashin tabbas a tsakanin al’umma.

    Har wa yau, Atama ya bayyana cewa; zanga-zangar na nufin jawo hankalin gwamnati, ba tayar da hayaniya ko tarzoma ba.

    “A bayyane yake cewa, rabon wutar lantarki ga Jihar Nasarawa, musamman babban birnin jihar, ko kaɗan bai wadatar ba, musamman wajen biyan buƙatun da ake da su.

    Sannan, ya buƙaci gwamnati da ta yi hulɗa da hukumomin samar da wutar lantarki ta tarayya, don tabbatar da samun isasshiyar wutar lantarkin da kuma samun daidaitaccen rabon wutar ga jihar.

    [ad_2]

    Source link

  • ADC Ta Yi Fatali Da Sabon Jadawalin Zaɓe Da INEC Ta Fitar

    [ad_1]

    Jam’iyyar ADC ta yi fatali da sabon jadawalin zaɓe da hukumar zaɓe mai zaman kanta ta ƙasa (INEC) ta fitar, tana iƙirarin cewa an tsara shi ne don ware jam’iyyun adawa kafin zaɓen 2027.

    A cikin wata sanarwa da sakataren yaɗa labarai na jam’iyyar, Bolaji Abdullahi, ya sanya hannu, jam’iyyar ta ce jadawalin da aka sake tsarawa ba kawai shirin gudanarwa ba ne, wani tuggun siyasa ne da rai raunana ƴan adawa.

    ADC ta yi iƙirarin cewa sabbin abubuwan da aka ƙaƙaba a cikin dokar zaɓe ta 2026 sun yi wa jam’iyyun adawa sauri yawa.

    A cewar sabon jadawalin zaɓeni, za a gudanar da zaɓen fitar da gwani na jam’iyyu tsakanin 23 ga Afrilu da 30 ga Mayu, 2026. Duk da haka, jam’iyyu dole ne su miƙa cikakken rajistar mambobinsu ta na’urar zamani ga INEC kafin ranar 2 ga Afrilu, 2026, makonni kaɗan masu zuwa.

    Jam’iyyar ta nuna cewa sashe na 77 na dokar, wanda ke cewa kowace jam’iyya da ta kasa gabatar da rajistar mambobinta akan lokaci, ba za ta gabatar da ɗan takara a wannan zaɓe ba. ADC ta bayyana wannan lamarin a matsayin wanda ya saɓa wa doka wacce aka saɓa.

    “Wannan ba dokokin cikin gida ba ne. An ƙirƙiresu ne da gangan don sanya shinge ga ‘yan adawa daga shiga zaɓen da ke tafe,” in ji sanarwar.

    ADC ta bayyana cewa jam’iyyar mai mulki ta riga ta fara tattara irin wannan rajista tun daga watan Fabrairu 2025, kafin ta samar da dokar, wanda ya ba ta babbar dama.

    Ta ƙara da cewa yayin da jam’iyyar mai mulki ta kwashe kusan shekara guda tana yin shiri, ana sa ran sauran jam’iyyun adawa su kammala wannan tsari a kusan wata guda. ADC ta bayyana wannan a matsayin abin da ba zai yiwu ba a aikace.

    Jam’iyyar ta kuma zargi cewa tasirin sabon jadawalin da dokar zaɓe sun bayyana Ƙarara cewa Shugaban ƙasa, Bola Tinubu ake share wa hanya don ya yi tazarce a zaɓen 2027.

    Ya yi kira ga ƙungiyoyin fararen hula da ɗaukacin ‘yan Nijeriya daga ɓangarorin siyasa daban-daban su duba wannan jadawalin tare da haɗa kai da su wajen neman adalci. Ta yi gargaɗin cewa dimokuraɗiyya ba za ta iya wanzuwa ba idan an shamfiɗa dokoki don fifita wani ɓangare guda ɗaya.

    [ad_2]

    Source link

  • Yanzu Maza Sun Waye Ba Sa Son Bayar Da Ramadan Basket

    [ad_1]

    Shafin TASKIRA shafi ne da ya saba zaƙulo muku batutuwa daban-daban, waɗanda suka shafi al’umma.

    Tsokacinmu na yau, zai yi duba ne game da Ramadan Baske, wanda masoya ke kai wa juna. Shin har yanzu wannan al’ada tana nan ko kuwa ta sauya zani?

    Dalilin haka ya sa wannan shafi jin ta bakin wasu daga cikin mabiyansa game da wannan batu; “Ko wacce wainar ake toyawa game da Ramadan Basket a wannan shekarar? Ya batun tsadar kaya wajen kawo barazana ga masu haɗa Ramadan Basket? Wacce shawara ya kamata a bai wa matasa masu ƙoƙarin haɗa Ramadan Basket ko kayan toshi, musamman masoyan da suke rabuwa da juna saboda rashin Ramadan Basket?

    • An Fara Bincike Bayan Mutuwar Mutum Huɗu A Turmutsutsun Karɓar Tallafin Ramadan A Katsina
    • Ramadan: Lokutan Buda-Baki Da Sahur Na Azumi Na 18

    Ga dai bayanan nasu kamar haka:

    Sunana Hadiza Ibrahim D. Auta, Ƙaura-Namoda, Jihar Zamfara:

    Ramadan Basket, a wannan shekarar maza da yawa sun jingine wannan al’adar. Duk da wasu masu ƙwarin zuciya da ƙarfin kyautatawa, sun yi wa ‘yan matansu. Amma kashi bakwai cikin goma na masu yi, sun jingine. Tabbss tsadar kaya ya taka muhimmiyar rawa, ta wani gefen kuma kiranyen da wasu malamai ke yi wa samarin, a kan cewa babu dole ba sai sun yi ba.

    Hakan ya gurgunta zuciyoyin masu fafutukar son burge waɗanda suke so a irin wannan fuskar. Wasu kuma da man can hannun ‘yan dambe gare su, sai suka samu hanyar fakewa, domin doje wa Ramadan Basket. Shawarata ga matasa masu ƙoƙarin haɗa Ramadan Baske, kada su daina su yi iya ƙarfinsu, saboda tukuicin so, kyauta ne. A duk lokacin da suka kyautata, ana jin daɗi, sannan kuma soyayya tana ƙara danƙo.

    Har ila yau, matan da suke ƙwallafa rai a kan don an yi wa wata, su ma dole sai an yi musu, idan kuma ba a yi musu ba su rabu da mai son su; sun jahilci zaman gaskiya da amana. Idan akwai ƙauna ta domin Allah, wannan dalilin bai kai matsayin da zai raba soyayya ba.

    Sunana Fatima Nura Kila, Jihar Jigawa:

    Batun Ramadan Basket, kusan yanzu gaskiya ba a fiya yin sa ba, duba da yadda kayan masarufi, musamman na shago yake tsada, sannnan babu kuɗi a hannun samari. Tabbas tsadar kaya ya yi yawa, yayin da a da mutum dubu goma ta isa a haɗa Ramadan Basket, amma yanzu sai a haɗa na dubu hamsin, kuma ba wani kayan a zo a gani ba ne.

    Har kullum, matuƙar kina son mutum, ki so shi saboda Allah, domin idan wata rana akwai, wata ranar babu, idan babu sai ki tuno alhairansa a gare ki.

    Sunana Lawan Isma’il (Lisary), Rano, a Jihar Kano:

    Gaskiya ban ji ana maganar Ramadan Baske ba a namu yankin, duk da kayan ba ya tsada kamar shekarun baya, amma kuma kuɗin ne babu sosai a hannun mutane. Ai ba lefin tsadar kaya ba ne kaɗai, a samu a yi ɗinkin sallah da kuma abin da za a ci a wannan azumin shi ne ya fi a kan Ramadan basket. Shawarata a gare su ita ce, kawai su sadaukar da kuɗin wajen ɗinka wa marayun unguwarsu kayan sallah ko kuma su ciyar da mabuƙata a cikin wannan watan na Ramadan, zai fi musu. Allah kasa mu dace, amin.

    Sunana Khadija Auwal Ahmad Ƙoki, A Jihar Kano:

    Eh to, Ramadan basket, ana nan ana yi; wasu tuni sun riga sun yi, wasu kuma sai nan gaba. Gaskiya A’a, ai kayan ba kamar da ba, Alhmadulillah, yanzu kuma babu abin da ya sauya na game da masu haɗa Ramadan basket ɗin. Gaskiya shawarar da zan bayar ita ce, idan aka samu rabuwa saboda abin duniya, to wannan soyayyar daman ba ta Allah ba ce, koda-yaushe zai iya rabuwa da ke, don haka idan ya dawo ta yi nazari sosai a kansa.

    Sunana Abba Abubakar Yakubu, Daga Jos, Jihar Filato:

    Ra’ayina game da batun Ramadan Basket zan iya cewa, ai tuni ya zama tsohon ya yi. Koda-yake, ya zama kamar wata al’ada, amma har yanzu akwai masu yin hidimar Ramadan Basket, domin nuna wa wacce suke so tsantsar ƙauna tare da ɗaga darajarta a tsakanin ƙawayenta da ‘yan’uwa.

    Sai dai, gaskiya yanzu ba kamar a shekarun baya ba, musamman a manyan birane, hidimar Ramadan Basket ta zama tsohuwar al’ada, saboda sauyin yanayin zamantakewa, tattalin arziƙi da ci gaban rayuwa. Samari sun fi mayar da hankali wajen saya wa ‘yan matansu wayoyi masu tsada da ɗinkin kayan sallah, ko dai wata kyauta ta musamman, ba lallai cikin tsarin baya na Ramadan Basket ba. Ramadan Basket, abu ne da yake ƙara danƙon soyayya a tsakanin masoya, yanayin rayuwa yanzu ya sa tilas a yi haƙuri da abin da ya samu, a tafiyar da rayuwa a yadda ta zo. Kadaran-kadahan!

    Sunana Sadik Abubakar Abdullahi, Rijiyar Lemo, Ƙaramar Hukumar Dala, Jihar Kano:

    Ramadan basket, wani nau’in farantawa ne, kuma al’ada ce mai kyau da ta daɗe tana gudana tsakanin masoya, tun shekaru aru-aru. A lokutan baya, wannan al’ada ta fi tasiri duk da cewa, a lokacin ba wasu kaya ba ne masu yawa ake yi ko kuma ƙayyadewa.

    Daidai ƙarfin saurayi zai yi wa budurwarsa abin da zai faranta mata rai tare da sanya mata farin ciki, sannan ya fitar da ita kunya. Idan bai yi mata ba, ba ta nuna damuwa ko kuma ta nemi su ɓata. To sai dai, a wannan zamanin al’adar ta sauya sosai, abin ya zama wani iri daban. ‘Yan mata, su kan ɗora buri sosai a kan Ramadan basket, wanda hakan ke razana wasu daga cikin samarin har ta kai ga an ɓata.

    Bayan haka, akwai tasirin tsadar kayayyaki a irin burin ‘yan mata na wannan zamani, ba sa kallon abin da ake kawowa a matsayin kyautatawa da kulawa. Sun fi mayar da hankali a kan yawan abin da za a kawo musu.

    Don haka, shawarata ga matasa ita ce, su yi ƙoƙari daidai gwargwadon ƙarfinsu su yi abin da zai faranta wa ‘yan matansu rai, kada ƙarancin abin da zai yi ya hana shi yi, lallai ya yi ko da babu yawa. Su ma ‘yan matan su gane, idan samarinsu ba su yi musu Ramadan basket ba, ko kuma suka yi kaɗan, to su karɓa su yi godiya su nuna farincikinsu.

    Sunana Hafsat Sa’eed, Jihar Neja:

    Ramadan Basket, wani alhairi ne wanda masoya suka sanya masa wannan suna na Ramadan Basket, a nawa tunanin, bai zama dole sai an yi wani abu ba. Idan mutum ya kawo maka sai ka karɓa, idan bai kawo maka ba, ka haƙura, ba abu ne na takurawa ba.

    A halin yanzu, ba za a iya cewa; akwai tsadar kaya da zai hana yin Ramadan Basket ba, musamman ga me niyya, yanzu an samu sauƙi sai dai a ce Alhamdulillah, a kan waccan shekarar.

    Sunana Aisha T. Bello, Jihar Kaduna:

    Yanzu gaskiya maza sun waye, ba sa son bayar da Ramadan Basket, amma duk da haka kuma akwai masu bayar wa. Eh, maza yanzu ba sa son ba da Ramadan Basket, saboda tsadar rayuwa, amma mata idan ba a ba su ba, wasu har rabuwa ake a kansa, gaskiya musamman wacce take tara samari, za ki ji tana wane na ji shiru batun Ramadan Basket ɗinsa, to gaskiya idan rowa ce, za mu rabu da shi ba na yi, haka wasu matan suke yi.

    Saboda haka, shawarata a nan ga masu Ramadan Basket, musamman mata waɗanda suka mayar shi dole, Ramadan Basket ba dole ba ne, su yi haƙuri rayuwa ce ta canja, yadda rayuwar take a da, yanzu ba haka take ba. Ramadan Basket ba dole ba ne. Don haka, mata don Allah mu yi haƙuri, Allah ya ba mu dacewa, amin.

    [ad_2]

    Source link