APC Na Da Gwamnoni 31 Bayan Sauya Sheƙar Gwamnan Zamfara

[ad_1]

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya fice daga jam’iyyar PDP tare da komawa APC.

Mai taimaka masa kan harkokin yaɗa labarai, Nuhu Anka ne, ya tabbatar da hakan cikin wata sanarwa da ya fitar ranar Litinin.

  • Yaƙin Amurka Da Iran Na Iya Tura Farashin Litar Fetur Zuwa N2,000 A Nijeriya – PETROAN
  • Majalisar Dattawa Za Ta Gayyaci Kyari Kan Zargin Giɓin Kuɗi Har Naira Tiriliyan 210 A NNPCL

Sanarwar ta ce gwamna ya ɗauki wannan mataki ne bayan tuntuɓar shugabannin siyasa da magoya bayansa a jihar.

Ta kuma bayyana cewa ya bar PDP ne saboda rikicin shugabanci da saɓani da ke ci gaba da addabar jam’iyyar.

Da wannan sauya sheƙar, yawan gwamnoni na jam’iyyar APC a faɗin Najeriya ya kai 31.

Wannan na zuwa ne kwanaki kaɗan bayan gwamnan Jihar Adamawa, Ahmadu Fintiri, shi ma ya sauya sheƙa daga PDP zuwa APC.

Sauya sheƙar Lawal zuwa APC zai taimaka wajen ƙara haɗin kai da gwamnatin tarayya, tare da bunƙasa tsaro da ci gaban Jihar Zamfara.

[ad_2]

Source link

Similar Posts

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *