Category: Latest News

  • Gidaje fiye da 40 sun lalace a lokacin ruwa da iska

    [ad_1]



    Mazauna yankin Egbeda Egga da ke ƙaramar hukumar Ijumu a jihar Kogi da dama ne suka rasa matsugunansu, sakamakon iskar guguwa da ta lalata gidajen kwanan mutane sama da 40.

    Rahotanni daga yankin a ranar Alhamis sun nuna cewa ruwan saman da ba a yi  tsammani ba a ranakun Talata da Laraba, ya zo ne da guguwa mai ƙarfi wacce ta lalata majami’u, wuraren sana’o’i, da makarantu, inda aka yi asarar dukiya na miliyoyin Nairori.

    Shugaban ƙungiyar raya yankin Egbeda-Egga (EDU) na ƙasa, Dakta Emmanuel Dare Otitolaiye, ya bayyana cewa girman ɓarnar ya bar iyalai da dama cikin mawuyacin hali na neman mafita. Ya ce: “Mazauna yankin da dama sun rasa muhallansu, kuma a halin yanzu suna fake ne a gidajen maƙwabta da na ’yan uwa.”

    Ya ce: “Mazauna yankin da dama sun rasa matsugunansu, kuma a halin yanzu sun fake ne a gidajen makwabta da na ’yan uwa.”

    “Muna kira ga hukumomi da su gaggauta bayar da tallafi ga mutanenmu waɗanda suka rasa gidajensu, sana’o’insu, da hanyoyin neman abincinsu.” In ji shi.

    Dakta Otitolaiye ya ƙara jaddada cewa, al’ummar na buƙatar kayan agajin gaggawa, waɗanda suka haɗa da: wurin kwana, abinci da magunguna, domin taimaka wa waɗanda abin ya shafa su farfaɗo daga wannan ibtila’i .

    Haka zalika, ƙungiyar raya yankin Okun (ODA) ta bayyana alhininta game da wannan ibtila’i da ya haifar da gagarumar asara da kuma ƙunci ga mazauna yankin Egbeda-Egga.

    ƙungiyar ta yi kira ga dukkan masu ruwa da tsaki da su samar da matsuguni, abinci da magunguna ga waɗanda wannan ibtila’i ya rutsa da su.


    [ad_2]

    Source link

  • Kawar Da Dukkanin Haraji Kan Hajojin Da Ake Shigarwa Kasar Sin Daga Afirka Zai Bunkasa Cinikayyar Albarkatun Gona Na Afirka Ta Kudu

    [ad_1]

    Dan majalisar zartarwa game da harkokin noma da raya karkara na lardin Gauteng na kasar Afirka ta kudu Vuyiswa Ramokgopa, ya ce manufar nan ta kawar da haraji baki daya kan hajojin kasashen Afirka masu alakar diflomasiyya da Sin, wadanda ake shigarwa babbar kasuwar kasar Sin, za ta haifar da sabbin damammaki, na yaukaka cinikayyar albarkatun gona tsakanin Afirka ta kudu da Sin.

    Vuyiswa Ramokgopa, ya bayyana hakan ne yayin zantawarsa da kamfanin dillancin labarai na kasar Sin Xinhua, a gefen taron baje kolin kasa da kasa dangane da sana’ar kiwon tsuntsayen gida da dabbobi na nahiyar Afirka ko IPLEX.

    Jami’in ya kara da cewa, suna maraba da sanarwar jingine harajin da Sin ta ayyana. Ya ce manufar za ta samar da muhimmiyar dama ga kasashen Afirka, musamman Afirka ta kudu, a fannin fadada fitar da hajojinta, da bude sabon babi na ci gaba a muhimman fannoni irin su noma.

    Taron baje koli na IPLEX, daya ne daga manyan taruka masu nasaba da sana’ar noma da ake gudanarwa a nahiyar Afirka, wanda ke bayar da damar baje fasahohin kirkire-kirkire na duniya, dangane da kiwon tsuntsayen gida da dabbobi, da kuma sada manoma na gida da masu samar da fasahohin zamani na kasa da kasa, da masu kera kayayyakin noma.

    Mahalarta taron na wannan karo sun jaddada cewa, karfafa hadin gwiwa tsakanin Sin da kasashen Afirka a fannin noma, na iya taimakawa wajen karfafa tsarin samar da hajoji a fannin, da fadada damar shiga kasuwanni, da bullo da sabbin damammaki ga manoma, da kasuwancin albarkatun gona a dukkanin sassan nahiyar. (Saminu Alhassan)

    [ad_2]

    Source link

  • Xi Ya Ba Da Amsar Wasikar Malamai Da Dalibai Na Ajin Sinanci Na Makarantar Kasa Da Kasa Ta Faransa

    [ad_1]

    Kwanan nan, shugaban Sin Xi Jinping ya ba da amsar wasikar malamai da dalibai na ajin Sinanci na makarantar kasa da kasa dake yankin Provence-Alpes-Cote d’Azur na Faransa, inda ya nuna fatan alherinsa gare su da ma dukkan malamai da dalibai na makarantar.

    Xi ya bayyana cewa, koyon Sinanci ba ma kawai yana taimakawa wajen fahimtar Sin ba ne wadda kasa ce mai zamanantarwa dake da dogon tarihi, har ma ya ba da taimako wajen gina wata gada zuwa makoma mai kyau ga kasashen Sin da Faransa. Yana maraba da mutane su zo kasar don yin karatu, da ziyara, da kuma yawon shakatawa, ta yadda za su iya fahimtar Sin mai gaskiya, da bude kofa, da kuma kokarin samun ci gaba bisa dogaro da kanta.

    Kwanakin baya, wakilan malamai da dalibai daga ajin Sinanci na makarantar kasa da kasa dake Provence-Alpes-Cote d’Azur na Faransa, sun aika wa shugaba Xi Jinping wasika don bayyana ra’ayoyinsu game da koyon Sinanci da kuma sha’awarsu da al’adun kasar.(Safiyah Ma)

    [ad_2]

    Source link

  • Ramadan: Lokutan Buda-Baki Da Sahur Na Azumi Na 23

    [ad_1]

    Mota Sahur (Fajr/Imsak) Iftar (Maghrib)
    Abuja 05:11 AM 07:00 PM
    Idan 05:06 AM 06:54 PM
    Kano 05:07 AM 06:59 PM
    Kaduna 05:11 AM 07:02 PM
    Legas 05:25 AM 07:19 PM
    Maiduguri 05:02 AM 06:39 PM
    Sokoto 05:24 AM 07:12 PM
    Fatakwal 05:16 AM 07:01 PM

    [ad_2]

    Source link

  • Majalisar NPC Ta Gudanar Da Zaman Rufe Taronta Na Shekara-shekara Na Bana

    [ad_1]

    A yau Alhamis ne majalisar wakilan jama’ar kasar Sin(NPC) ta 14, ta gudanar da zaman rufe taronta na shekara-shekara, inda shugaban kasar Sin Xi Jinping, da sauran shugabannin jam’iyyar kwaminis ta kasar da shugabannin kasar suka halarci taron a babban zauren taruwar jama’a dake birnin Beijing.

    Yayin zaman, ‘yan majalisar wakilan sun zartar da kuduri game da rahoton aikin gwamnati, tare da amincewa da kundin shirin raya kasa na shekaru biyar-biyar na 15, wanda za a aiwatar tsakanin shekarar nan ta 2026 zuwa 2030, domin bunkasa tattalin arziki da zaman rayuwar al’ummun kasar ta Sin. Kana sun kada kuri’ar amincewa da dokar kare muhallin halittu da muhalli, da ta inganta hadin kan kabilun kasa da yayata ci gabansu, da kuma dokar kasa ta tsara dabarun ci gaba. (Saminu Alhassan)

    [ad_2]

    Source link

  • Sojoji sun kashe Kwamandan ISWAP da mahara a Yobe

    [ad_1]



    Sojojin rundunar haɗin gwiwa ta  Arewa maso Gabas (OPHK) sun kashe aƙalla membobin Boko Haram/ISWAP 20, ciki har da wani babban Kwamandan su mai suna  Abu Yusu, Munzir na Dursula, a wasu hare-hare da suka yi yunƙurin kaiwa kan al’ummar Goniri a ƙaramar hukumar Gujba, jihar Yobe.

    Hare-haren, waɗanda suka fara a daren Litinin, 9 ga Maris 2026, kuma suka ci gaba har zuwa safiyar Talata, 10 ga Maris 2026, sun kai hari kan sansanonin sojoji a ƙarkashin sashe na 2 na Operation HADIN KAI (OPHK).

    Majiyar na cewar, wasu sojoji sun samu raunuka a lokacin fafatawar amma an kwashe su nan take kuma a halin yanzu suna cikin kwanciyar hankali.

    An tabbatar da hakan a cikin wata sanarwa da Laftanar Kanar Sani Uba, jami’in yaɗa labarai na OPHK ya fitar, yadda ya ce sojoji sun yi nasarar daƙile ƙoƙarin da ‘yan ta’addan suka yi, wanda ya haɗa da ci gaba da mamaye ƙauyen Goniri da kuma mahaɗar Ngamdu a wani yunƙuri na kewaye sansanonin sojoji.

    “Sojojin da ke cikin shirin sun mayar da martani da sauri da ƙarfin wuta da dabarun yaƙi, suna daidaita tsaron su yayin da aka tura ƙarin sojoji da tallafin mayaƙan sama,” in ji Laftanar Kanar Uba.”

    “‘A cewarsa ‘yan ta’addan sun gaji inda suka tilasta musu ja da baya cikin ruɗani da ƙarfin wuta, suna fuskantar mummunan rauni, ciki har da babban Kwamandan su da ya riga mu gidan gaskiya.”

    Bayan rikicin, sojoji sun gano gawarwaki da dama, makamai, harsasai, na’urorin fashewa (IEDs) da sauran kayan aiki na ‘yan ta’addan da suka tsere suka yi watsi da su.

    samamen da aka kai a Triangle na Timbuktu, musamman a kusa da Gwaigomari, sun haifar da gano ƙarin asarar rayukan ‘yan ta’adda.

    Laftanar Kanar Uba ya jaddada cewa, a yanzu haka yankin yana ƙarƙashin ikon sojoji kuma sojojin ƙasa da na sama suna ci gaba da ayyukan bin diddigi masu ƙarfi a cikin al’ummomin da ke kewaye don gano duk wani ɗan ta’adda da ya tsira.

    Ya ƙara da cewa, “Operation HADIN KAI ta ci gaba da jajircewa wajen kawar da ta’addanci gaba ɗaya da kuma dawo da zaman lafiya da tsaro mai ɗorewa a duk faɗin Arewa maso Gabas.

    “Babban Kwamandan Soja ya yaba wa sojojin saboda jarumtakar su da juriyarsu yayin da yake kira gare su da su ci gaba da aiki tukuru.”


    [ad_2]

    Source link

  • Iran Ta Kama Mutane Kusan 200 Kan Zargin Yi Wa Amurka Da Isra’ila Leƙen Asiri

    [ad_1]

    Hukumomin Iran sun kama kusan mutane 200 da ake zargi da yi wa Amurka da Isra’ila leƙen asiri a lokacin da ake yaƙi tsakanin ƙasashen.

    Wata ƙungiyar kare haƙƙin bil’adama mai suna Human Rights Activists News Agency ta ce an kama mutane 195 a birnin Tehran da wasu birane, ciki har da Tabriz.

    • NNPC Ta Rage Farashin Fetur
    • Sojoji Sun Daƙile Harin ISWAP, Sun Kashe ’Yan Ta’adda 20 A Yobe

    A cewar ƙungiyar, an kama mutanen ne saboda zargin suna amfani da kafofin sada zumunta wajen aike hotuna da bidiyon hare-haren da Amurka da Isra’ila suka kai a Iran zuwa kafafen yaɗa labarai na duniya.

    Rahotanni sun ce rundunar sojin Iran ma ta kama wasu mutane 10 da ake zargi da aika bidiyon hare-haren zuwa kafafen labarai na waje.

    An kuma nuna su a talabijin suna amsa laifinsu.

    Shugaban rundunar ’yansandan ƙasar, Ahmad Reza Radan, ya yi gargaɗin cewa duk wanda ya shiga zanga-zanga a wannan lokaci za a ɗauke shi a matsayin mai cin amanar ƙasa.

    Hukumomin ƙasar sun kuma yi gargaɗi ga iyaye da su hana ’ya’yansu shiga zanga-zanga a ciki ko wajen ƙasar yayin da Iran ke ci gaba da gwabza yaƙi.

    Wannan na zuwa ne a lokacin da rikicin da Amurka da Isra’ila ke yaƙi da Iran.

    [ad_2]

    Source link

  • An sace tumaki 1,400 da kashe makiyayi a Borno

    [ad_1]



    Rundunar ’yan sandan jihar Borno ta bayyana cewa wasu da ake zargin ’yan ƙungiyar Boko Haram ne sun kai hari wani matsugunin makiyaya a ƙaramar hukumar Konduga, inda suka kashe makiyayi guda tare da sace tumaki kusan 1,400.

    A cikin wata sanarwa da ta fitar ranar Alhamis, jami’in hulɗa da jama’a na rundunar, Nahum Kenneth Daso, ya bayyana cewa lamarin ya faru ne a ƙauyen Wuturo, wani matsugunin makiyaya kusa da garin Konduga. Daso ya ce mambobin ƙungiyar makiyaya ta Miyetti Allah ne suka kai rahoton harin zuwa ofishin ’yan sanda na Konduga.

    A cewar sanarwar, maharan sun isa matsugunin ne da daddare a kan babura.

    “Bayan samun rahoto daga ƙungiyar Miyetti Allah ta Konduga a ofishin ’yan sanda na Konduga cewa a ranar 10 ga Maris, 2026, da misalin ƙarfe 22:30 na dare, wasu ’yan bindiga da ba a san ko su wanene ba a kan babura biyar sun kutsa kai cikin matsugunin,” in ji sanarwar.

    Rundunar ta ce binciken farko ya nuna cewa, an kashe mutum guda yayin harin, yayin da wani kuma ya samu raunuka.

    “Binciken farko ya nuna cewa yayin harin, Ahmadu Baida, mai shekaru 40, ya samu raunukan harbin bindiga da suka yi sanadiyyar mutuwarsa, yayin da Mohammadu Baida, mai shekara 30, ya samu rauni a ƙafarsa ta hagu. Maharan sun kuma yi awon gaba da tumaki kusan dubu ɗaya da ɗari huɗu (1,400) na makiyayan,” in ji sanarwar.

    An tura jami’an tsaro zuwa yankin jim kaɗan bayan samun rahoton.

    “Bayan samun rahoton, wata haɗin guiwar tawagar ’yan sanda, sojoji da sauran masu ruwa da tsaki a harkar tsaro, ciki har da jami’an sa-kai (Civilian JTF) da mafarauta, ƙarƙashin jagorancin baturen ’yan sanda na Konduga, sun gaggauta isa wurin,” in ji Daso.

    Ya kara da cewa an kai wadanda abin ya shafa asibiti, inda aka tabbatar da mutuwar ɗaya daga cikinsu.

    “An ɗauke waɗanda abin ya shafa zuwa asibiti inda likita ya tabbatar da mutuwar Ahmadu Baida lokacin da aka isa, yayin da shi kuma wanda ya ji rauni yake karbar magani kuma yana samun sauki,” in ji shi.

    Kwamishinan ’yan sanda na jihar, Naziru Abdulmajid, ya yi Allah-wadai da harin, sannan ya miƙa saƙon ta’aziyya ga iyalan mamacin. Kakakin rundunar ya ce tuni hukumomin tsaro suka fara gudanar da bincike da nufin kamo waɗanda suka aikata laifin tare da dawo da dabbobin da aka sace.


    [ad_2]

    Source link

  • NNPC Ta Rage Farashin Fetur

    [ad_1]

    Kamfanin man fetur na ƙasa (NNPC) ya rage farashin litar fetur a gidajen sayar da man fetur nasa zuwa N1,130 a Lagos da kuma N1,165 a Abuja.

    Ragin farashin, wanda ya fara aiki ranar Laraba, ya nuna saukar N100 daga tsohon farashin N1,230 a Lagos, yayin da a Abuja kuma aka rage N95 daga N1,260 a lita.

    • Ƙungiyar PNGI Ta Yaba Wa Bayo Ojulari Bisa Nasarorin Gyare-gyare Da Aka Fara Samu A NNPC
    • Majalisar Dattawa Za Ta Gayyaci Kyari Kan Zargin Giɓin Kuɗi Har Naira Tiriliyan 210 A NNPCL

    An lura da sabon farashin a wasu gidajen mai na NNPC da ke kan titin Isheri Oshun Road, Apple Junction da Ago Palace Way a Lagos, haka kuma a gidajen sayar da mai na kamfanin da ke yankunan Jabi da Wuse a Abuja.

    Saukar farashin na zuwa ne duk da cewa wasu ‘yan kasuwar mai ba su fara aiwatar da sabon farashin da Matatar Dangote ta rage ba, inda matatar ta rage farashin ɗauka da N100 zuwa N1,075 a lita bayan faduwar farashin ɗanyen mai a kasuwar duniya.

    Rahotanni sun nuna cewa farashin ɗanyen mai ya fara sauka bayan yaƙin da ake yi a Gabas ta Tsakiya tsakanin Amurka, Iran da Israel. Haka kuma shugaban Amurka, Donald Trump, ya ce rikicin na iya kawo ƙarshe nan ba da jimawa ba, abin da ya rage fargabar dagulewar samar da mai a duniya.

    [ad_2]

    Source link

  • NNPC ya rage farashin man fetur a Legas da Abuja

    [ad_1]



    Kamfanin Man Fetur na ƙasa (NNPC) ya rage farashin litar man fetur a gidajen mansa zuwa N1,130 a birnin Legas, da kuma N1,165 a Abuja.

    Wannan sabon farashin ya nuna ragi na N100 daga tsohon farashin da ake sayarwa N1,230 a Legas, sannan an samu ragin N95 daga N1,260 da ake sayarwa a Abuja.

    Bincike ya nuna cewa tuni aka fara sayar da man a kan sabon farashin a gidajen man NNPC da dama a Legas, ciki har da waɗanda ke kan hanyar Isheri Oshun, Apple Junction, da Ago Palace Way.

    Haka zalika, wasu gidajen man na kamfanin na ƙasa da ke Babban Birnin Tarayya sun fara sayar da man fetur ɗin a kan N1,165 kowace lita, ciki har da gidajen man da ke yankunan Jabi, Lifecamp, Wuse Zone 5, da Wuse Zone 4.

    Wannan sabon farashin ya biyo bayan ragin da matatar man Dangote ta yi kwanan nan, inda ta rage nata farashin zuwa N1,075 a daidai lokacin da farashin ɗanyen mai ke faɗuwa a kasuwar duniya.

    A cewar shafin OilPrice.comfarashin ɗanyen mai na Brent ya faɗi warwas a ranar Talata da kusan kashi 27 cikin 100, inda ya sauka daga $119 a kowace ganga zuwa kusan $87.

    Haka kuma, farashin man dizal yanzu ya koma N1,430 kowace lita, wanda ke nuna ragin N190 daga tsohon farashin sa na N1,620.


    [ad_2]

    Source link