2027: Ministocin Da Ake Tsammanin Za Su Yi Murabus Kafin Wa’adin Tinubu Na Ranar 31 ga Maris
Akalla ministoci shida a cikin majalisar zartarwar Shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu na iya yin murabus kafin cikar wa’adin shugaban kasa na ranar 31 ga Maris ga masu mukaman siyasa da ke neman tsayawa takara a zaben 2027. Wani umarni daga Tinubu, wanda ofishin sakataren gwamnatin tarayya, George Akume, ya bayar, ya umarci duk jami’an…