Sin Za Ta Ci Gaba Da Bayar Da Gudummawar Gaggauta Maido Da Zaman Lafiya Da Walwala A Yankin Gulf
[ad_1]
Kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin Lin Jian, ya ce tasirin yakin Iran na gaggauta bazuwa, kuma hakan na matukar illata yanayin zaman lafiya da daidaito a Gabas ta Tsakiya da ma duniya baki daya.
Lin, wanda ya bayyana hakan a Larabar nan, yayin da yake jagorantar taron manema labarai na yau da kullum da aka saba gudanarwa, ya ce dakatar da bude wuta nan take, da kawo karshen tashe-tashen hankula, su ne burikan bai daya na al’ummun kasashen yankin, kana kiraye-kiraye ne da al’ummun sauran sassan kasa da kasa suka jima suna yi. Ya ce burin da ake da shi, shi ne dukkanin sassan da rikicin ya shafa su yi amfani da duk wani zarafi, da duk wata kofa wajen wanzar da zaman lafiya, da saka ‘dan ba na tattaunawar dawo da zaman lafiya cikin sauri.
Lin Jian, ya kara da cewa, kasar Sin za ta kara zurfafa taka rawa mai ma’ana, a fannin yayata bukatar zaman lafiya, da kawo karshen tashe-tashen hankula, kana za ta yi aiki tare da kasashen yankin, da sauran sassan kasa da kasa, wajen bayar da gudummawar gaggauta dawo da zaman lafiya da walwala a yankin Gulf.
Daga nan sai jami’in ya ce halin da ake ciki yanzu a Gabas ta Tsakiya, ya haifar da barazana ga tsaron makamashi na duniya, ya illata tsarin samarwa da rarraba hajojin masana’antu zuwa sassan kasa da kasa, da kuma gurgunta odar cinikayyar duniya. Don haka kamata ya yi kasashen da lamarin ya shafa su gaggauta kawo karshen matakan soji, domin dakile yiwuwar tangal-tangal da yankin yake fuskanta ta haifar da karin mummunan tasiri ga ci gaban tattalin arzikin duniya.
Ya ce Sin a shirye take, ta karfafa tsare-tsare, da hadin gwiwa tare da al’ummun kasa da kasa, wajen shawo kan batutuwan tsaron makamashi. (Saminu Alhassan)
[ad_2]
Source link