Category: Latest News

  • An Gudanar Da Taron Tattaunawa Na Duniya Na “Sin A Yanayin Bazara” A Brazil

    [ad_1]

    A ranar Laraba 18 ga watan nan ne, babban rukunin gidan rediyo da talibijin na kasar Sin wato CMG, da ofishin jakadancin kasar Sin dake kasar Brazil, suka gudanar da taron tattaunawa na duniya bisa taken “Sin a yanayin bazara: ci gaban Sin, dama ga duniya” a birnin Brasilia, fadar mulkin kasar Brazil.

    A yayin taron, shugaban CMG Shen Haixiong, da ministan harkokin kiwon lafiyar kasar Brazil Alexandre Padilha sun gabatar da jawabai ta kafar bidiyo. Kana, jakadan kasar Sin dake Brazil Zhu Qingqiao, da wakilai game da harkokin siyasa, da kasuwanci, da ilmi, da kafofin watsa labarai kimanin 120 sun halarci bikin.

    Cikin jawabinsa, Shen Haixiong ya bayyana cewa, kasar Sin da kasashen duniya suna dogaro da juna wajen neman ci gaba da wadata. CMG za ta yi amfani da karfinsa na kasancewar kafar watsa labarai ta zamani, dake sahun gaba a duniya mai hade fifikon yada labarai da kirkire-kirkire na fasaha, da kuma albarkatun kafafen yada labarai, wajen inganta sakamakon tsarin zamanantar da al’ummar Sin, ta yadda hakan zai fi amfanar da duniya baki daya. (Mai Fassara: Maryam Yang)

    [ad_2]

    Source link

  • Wang Yi Ya Zanta Ta Wayar Tarho Da Ministar Harkokin Wajen Birtaniya

    [ad_1]

    Ministan harkokin wajen kasar Sin Wang Yi ya tattauna ta wayar tarho da takwararsa ta Birtaniya Madam Yvette Cooper a jiya Alhamis bisa gayyata. Bangarorin biyu sun mayar da hankali kan musayar ra’ayi kan halin da ake ciki a Gabas ta Tsakiya.

    Cooper ta bayyana ra’ayin Birtaniya kan halin da ake ciki a Gabas ta Tsakiya, cewar bisa yanayin duniya na karuwar tashin hankali, Birtaniya na fatan kara tuntubar bangaren Sin don gaggauta kawo karshen yakin, da sake bude tattaunawa ta diflomasiyya, da neman mafita ta dogon lokaci.

    Wang Yi ya bayyana cewa, ba wanda zai cimma nasara daga yaki marar karewa, kuma tsagaita wuta da dakatar da yaki shi ne burin jama’a. Bangaren Sin ya bukaci dukkan bangarori da su dakatar da ayyukan soja nan take, da warware sabanin ra’ayi ta hanyar tattaunawa bisa daidaito, da kuma kiyaye zaman lafiya da kwanciyar hankali a yankin.

    Ya ce, Sin da Birtaniya a matsayinsu na mambobin dindindin na kwamitin sulhun MDD, ya kamata su karfafa mu’ammala, su tsaya tsayin daka wajen aiwatar da matakai da suka dace da zaman lafiya, da kuma hada kai don kiyaye manufa, da ka’idodin kundin mulkin MDD, da ka’idojin kasa da kasa na wanzar da dangantaka, don hana sake tabarbarewar tsarin kasa da kasa da kuma lalacewar tushen zaman lafiya na duniya.

    Bangarorin biyu sun kuma yi musayar ra’ayi kan dangantakar Sin da Birtaniya, kuma sun kai ga matsaya daya ta ci gaba da inganta dangantaka ta abota a dukkannin fannoni bisa manyan tsare-tsare masu dorewa tsakanin Sin da Birtaniya, ta yadda za a samarwa dukkanin fadin duniya kwanciyar hankali, da tabbaci duk da rikice-rikice da sauye-sauye da ake fuskanta. (Amina Xu)

    [ad_2]

    Source link

  • Uromi: Shekara guda bayan kisan mafarauta, Gwamnatin Kano ta tallafa wa iyalansu

    [ad_1]



    Shekara guda bayan kisan wasu mafarauta a yankin Uromi na Jihar Edo, Gwamnatin Jihar Kano, ta tallafa wa iyalan waɗanda abin ya shafa da kuma waɗanda suka tsira daga harin.

    Gwamnatin ta raba kuɗi da kayan abinci ga waɗanda lamarin ya shafa.

    Kwamishinan Yaɗa Labarai, Ibrahim Abdullahi Waiya ne, ya bayyana hakan yayin wata ziyara da ya kai Ƙaramar Hukumar Bunkure, inda aka tara iyalan mamatan da waɗanda suka jikkata.

    Ya bayyana cewa Gwamna Abba Kabir Yusuf ne, ya bayar da umarnin raba tallafin bayan ya gano cewa ba a cika alƙawarin da aka ɗauka ba tun lokacin ziyarar ta’aziyya.

    A cewarsa, kowane daga cikin iyalai 16 na waɗanda aka kashe ya samu Naira dubu ɗari uku (N300,000).

    Waɗanda suka tsira sun samu Naira dubu ɗari biyu (N200,000) kowannensu.

    Haka kuma, kowane ya samu buhunan shinkafa guda biyu.

    Waiya, ya tuna cewa a baya, Gwamna Abba, ya ziyarci yankin tare da takwaransa na Jihar Edo, domin jajanta wa iyalan bayan harin da ya yi sanadin mutuwar mutane da dama tare da jikkata wasu.

    Ya ƙara da cewa yayin da Jihar Kano ta cika nata alƙawarin, Gwamnatin Jihar Edo ma ta tabbatar da cewa za ta biya diyyar nan ba da daɗewa ba.

    “An riga an buɗe asusun banki domin iyalansu, kuma muna sa ran Gwamnatin Jihar Edo za ta turo kuɗaɗen nan ba da jimawa ba,” in ji shi.

    Kwamishinan ya roƙi iyalan da su ci gaba da haƙuri, inda ya tabbatar musu da cewa gwamnatocin biyu na yin iyakacin ƙoƙarinsu domin tallafa musu da kuma tabbatar da adalci.

    Ya bayyana lamarin a matsayin “babban rashi ga ƙasa” tare da yin addu’ar Allah Ya jiƙan waɗanda suka rasu.

    Haka kuma, Waiya, ya bayyana cewa kwamitin da Gwamnatin Jihar Kano ta kafa ya yi aiki tare da hukumomin Jihar Edo domin magance matsalolin da suka taso.

    Ya sake jaddada ƙudirin gwamnati na ci gaba da tallafa wa waɗanda abin ya shafa da kuma nuna goyon baya ga iyalansu.


    [ad_2]

    Source link

  • Yadda ADC Ta Shiga Gaban PDP Wajen Zama Babbar Jam’iyyar Adawa A Zauren Majalisar Dattawa

    [ad_1]

    Abin da ya faru ranar Alhamis, 12 ga Maris ya sauya alkablar, inda ‘yan majalisar Dattawa tara masu rike da mukami a majalisar dattawa ta 10 suka bar jam’iyyun siyasarsu zuwa jam’iyyar ADC.

    Kamar dai kowacce zaman taron majalisar dattawa da ke gudana, amma a wannan zama ya sauya al’amura lokacin da shugaban majalisar dattawa, Sanata Godswill Akpabio ya fara karanta wasikun sauya sheka daya bayan daya.

    • Sarkin Musulmi Ya Bukaci A Sauya Fasalin Tsarin Tsaro A Yaki Da Ta’addanci
    • Rawar Da Sashen Ayyukan Hidimomi Da Biyan Bukatu Ke Kara Takawa A Kasar Sin

    ‘Yan majalisar dattawan da suka sauya sheka sun hada da Sanata Aminu Tambuwal, daga mazabar Sakwato ta kudu da Enyinnaya Abaribe, a mazabar Abiya ta kudu da Binos Yaroe, a mazabar Adamawa ta kudu da Bictor Umeh, a mazabar Anambra ta tsakiya da Tony Nwoye, a mazabar Anambra ta arewa da Lawal Usman, a mazabar Kaduna ta tsakiya da Ogoshi Onawo, a mazabar Nasarawa ta kudu da Austin Akobundu, a mazabar Abiya ta tsakiya da Ireti Kingibe, a mazabar Babban Birnin Tarayya Abuja.

    Bisa ga wannan, Abaribe da Tambuwal da wasu sun shiga jam’iyyar da tsohon shugaban majalisar dattawa, Sanata Dabid Mark ke jagoranta, tare da jaruman siyasa kamar tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar da dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar LP a 2023, Peter Obi da tsohon gwamnan Jihar Ribas, Rotimi Amaechi, da sauran su, domin takarar shugaban kasa a 2027 da kuma gudanar da ingantaccen adawa.

    Zaben shugaban kasa na 2027 shi ma zai gudana a wannan al’amari na adawa, musamman a lokacin da ‘yan ADC ke haduwa domin shirya kawar da Shugaban kasa, Bola Tinubu daga kan mulki.

    Haka kuma Sanata Seriake Dickson, na mazabar Bayelsa ta yamma ya sanar da matsayinsa na shiga ADC ba, amma zuwa sabuwar jam’iyyar Nigeria Democratic Congress, NDC inda shi ne wanda ya kafa kuma Shugaban Kasa.

    Guguwar sauya sheka ta sa ADC ta zama babban jam’iyyar adawa a majalisar dattawa da sanatoci 9, ta ragewa PDP zuwa 6, yayin da APGA ta kasance tana da 1, NNPP 1, NDC 1 da Accord 1, wanda idan aka hada da sanatoci 87 da APC ke da su, ya kai guda 106.

    [ad_2]

    Source link

  • Kasar Sin Na Fatan Inganta Raya Al’umma Mai Kyakkyawar Makoma Ta Bai Daya Ga Sin Da Afirka

    [ad_1]

    Kakakin ma’aikatar harkokin wajen Sin Lin Jian ya sanar a yau Juma’a cewa, bisa gayyatar da mataimakin shugaban Kenya Kithure Kindiki da mataimakin shugaban Afirka ta Kudu Paul Mashatile da mataimakin shugaban Seychelles Sebastien Pillay suka yi masa, mataimakin shugaban kasar Sin Han Zheng zai kai ziyarar aiki kasashen Kenya da Afirka ta Kudu da Seychelles daga ranar 22 zuwa 30 ga Maris.

    Game da batun, Lin Jian ya kara bayyana cewa, shekarar 2026 ita ce shekara ta farko ta aiwatar da shirin shekaru biyar-biyar na bunkasa tattalin arziki da zamantakewar kasar Sin na 15, kuma a ciki ake cika shekaru 70 da fara kulla huldar diflomasiyya tsakanin Sin da kasashen Afirka, haka kuma ita ce “Shekarar Cudanyar Jama’a da Musanyar Al’adu tsakanin Sin da Afirka”. Kuma wannan ziyarar wata muhimmiyar mu’amala ce tsakanin manyan shugabannin bangarorin biyu. A cewar kakakin, kasar Sin na fatan ganin cewa, ta hanyar wannan ziyara, za ta kara hada shirinta na shekaru biyar-biyar da dabarun ci gaban kasashen uku, da karfafa aminci da juna a fannin siyasa tsakaninta da kasashen uku, da kuma fadada hakikanin hadin gwiwa a fannoni daban-daban, ta yadda za a inganta raya al’umma mai kyakkyawar makoma ta bai daya ga Sin da Afirka a ko da yaushe cikin ko wane yanayi a sabon zamani. (Mai fassara Bilkisu Xin)

    [ad_2]

    Source link

  • Matsalar ADC Ta ADC Ce BA Ta APC Ba Ce

    [ad_1]

    Wannan shi ne abu na karshe da jam’iyyar (ADC) za ta so ta ji, amma dole ne a fada, ko da kuwa jam’iyyar ta ki sauraro. Lamarin ya fara ne da jinkirin rajistar jam’iyyar.

    Lokacin da abubuwa ba sa tafiya da gaggawa sauya sheka na farko galibi daga jam’iyyar (PDP), lamarin da ba su zata ba sai suka zargi jam’iyyar (APC) mai mulki da jinkirta rajistar, tare da zargin cewa tana amfani da bangaren da Ralph Okey Nwosu ke jagoranta domin kara jan kafa.

    • 2027: Ba Ni Da Tabbacin Samun Tikitin Takarar Shugaban Ƙasa A ADC — Peter Obi
    • ADC Ta Buƙaci Gwamnatin Tarayya Ta Saki El-Rufai Ko Ta Gurfanar Da Shi A Kotu

    A karshe an yi rajistar jam’iyyar a watan Yuni. Amma hakan bai kawo karshen sabani ba. Yayin da PDP ke durkushewa kuma mambobinta da dama musamman gwamnoni suka sauya sheka, ADC ta zargi APC da lallashi, bayar da cin hanci ko kuma matsin lamba domin mayar da Nijeriya kasa mai kama da jam’iyya guda daya.

    hakan na zuwa ne bayan sun gaza bayar da gamsasshiyar jujja, wadda ke cewa ko da dukkan gwamnoni a Nijeriya sun koma APC, hakan ba zai ceci jam’iyyar mai mulki daga hukuncin masu zabe mai tsauri a shekara mai zuwa ba, saboda rashin kyakkyawan aikinta.

    Zaben Shugabanni

    Sabuwar hujjar ita ce, jam’iyyar APC na shirin amfani da irin dabarar da ta yi amfani da ita wajen tarwatsa jam’iyyar Labour Party da kuma PDP a kan ADC: wato dasa shugaba domin raunana jam’iyyar, raba ta gida biyu, da kuma haddasa rikice-rikicen cikin gida.

    Wata sanarwa da jam’iyyar ta fitar a ranar Litinin ta zargi jam’iyyar mai mulki da shirin amfani da Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Kasa (INEC) domin amincewa da wani dan jam’iyyar da aka kora, Nafiu Bala Gombe, a matsayin shugaban kasa na ADC.

    Me ya sa? “Domin tabbatar da cewa Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya fito ba tare da hamayya ba a matsayin dan takara guda daya mai karfi a takardar zabe ta 2027.”

    Ban san wane irin wani sabon kulli ko zargi ADC za ta kirkiro kafin kasuwa ta gaba ba, amma ina ganin babbar matsalar jam’iyyar ita ce kanta. Idan ta ci gaba a haka, kafin APC ta kashe ta, tuni za ta riga ta mutu, kuma a kan kabarinta za a rubuta: nan ne ragowar wata jam’iyya da ta yi tunanin za ta samu mulki cikin sauki kamar ana zabar abinci daga menu!

    Hanyoyin Karbe Shugabanci

    Ba a ba da mulki; ana karbarsa ne, har ma a kwace shi ta hanyar tsari, shiri, da aiki. Ba a kafa jam’iyyar ADC domin ta dade ba, kamar yadda ake gina gida daga tushe, tubali bayan tubali, da hakuri a kowane mataki tare da bin tsari.

    A mafi yawan lokuta, jam’iyyar hadin gwiwa ce ta masu jin haushi da kuma masu matsananciyar sha’awar mulki, bayan wasu manyan jiga-jiganta sun lalata ta ta hanyar lomawa jam’iyyar PDP.

    Mun fi sanin burin zama shugaban kasa na tsohon mataimakin shugaban kasa Atiku Abubakar, da Peter Obi, da kuma Rotimi Amaechi, fiye da abin da jam’iyyar take tsayawa a kai a zahiri.

    Kwanan nan a Benin, Jihar Edo, an samu sabani tsakanin Odigie Oyegun da Rowland Owie, dukkansu dattawan siyasa masu shekaru da suka koma ADC, kan ko yankin Kudu maso Kudu ya kamata ya mara wa Amaechi ko Atiku baya, yayin da magoya bayan Obi ke gefe suna nuna damuwa.

    Abin da ake fada da kuma aikatawa domin tabbatar da tikitin takarar shugaban kasa ga daya daga cikin ukun ya fi yawa fiye da abin da muka sani game da kokarin gina jam’iyyar.

    A cikin wani yanayi da ya zama juyin akida mai muni ga asalin manufar jam’iyyar siyasa a matsayin wata cibiya, jam’iyyun sun zama kamar takardun nade-nade da ake yarwa, yayin da sauya sheka ya zama kamar wata dabara ta yaudara.

    Dubi Ga Tarihi

    Makomar jam’iyyun siyasa a Jamhuriyar Nijeriya ta Hudu na nuna wani labari mai tayar da hankali.

    Tsakanin 1999 zuwa 2015, lokacin da ludayin jam’iyyar PDP ke kan dawo, har yanzu tana iya raba ganimar siyasa ta hanyar da ta bai wa dimokuraxiyya makoma da kuma fata. Shugaba Olusegun Obasanjo ya lashe zaben shugaban kasa da kashi 62.78 cikin dari na kuri’u, rinjaye cikakke wanda ya kayar da abokin hamayyarsa Olu Falae, wanda shi ne dan takarar hadin gwiwa na jam’iyyun (APP) da (AD).

    Jam’iyyar PDP ta rike jihohi 21 cikin 36, yayin da jam’iyyun APP da AD suka rike jihohi 9 da 6 bi da bi. Haka kuma PDP ta samu kujeru 59 cikin 109 na Majalisar Dattawa da kuma kujeru 206 cikin 360 na Majalisar Wakilai a wancan lokacin. Don haka abin mamaki ne ga masana tarihin siyasa cewa cikin kasa da shekaru 27 kacal na kasancewa kungiya mai karfi haka, PDP ta zama kamar ba a iya ganinta, ko da kuwa don a adana ta ne kamar gawar da aka shanya.

    Tambayar, me ya faru, tana samun amsa mai sauki amma mai dacewa, wato dora laifi kan Tinubu, duk da cewa tsutsar da ke cin ‘yan adawa tana cikin ‘yan adawar ne da kansu.

    Tuna Baya Shi Ne Roko

    Bayan zaben gama-gari na 2023, PDP, ragowar da daga ciki da yawa daga mambobin ADC suka fito ta samu kujerun gwamna 10: Adamawa, Akwa Ibom, Bauchi, Delta, Enugu, Oyo, Filato, Rivers, Taraba, da Zamfara, yayin da ta 11 ita ce Bayelsa a zaben da aka yi a lokacin da ba cikakken zagaye ba. Wannan ya isa don bai wa jam’iyyar damar fafatawa, idan shugabanninta suna da gaskiya.

    Manyan jam’iyyun da suka haifa su ne APC (ACN, CPC, da ANPP), wadanda suka kayar da PDP a 2015 tare da taimakon wasu gwamnonin da suka tsere daga PDP, sun rike jihohi 11 kacal. A gaskiya, bayan zaben 2003, Lagos ce kawai jiha ta AD a Kudu maso Yamma, sauran jihohi biyar kuwa PDP ta cinye.

    Amma a kidayar karshe, PDP ta rasa tsofaffin matsugunninta na karfi a Kudu maso Kudu, Kudu maso Gabas, da Arewa Tsakiya saboda ambaliyar sauya sheka. Gwamnoni da ke kallon sake zabe da wasu da ke neman ritaya mai dandano zuwa Majalisar Dattawa kusan gaba daya sun bar PDP kamar masu sauka daga jirgi mai fadowa.

    A cikin wani yanayi mai tsanani na juyin kaddara, jam’iyyar ta zama wacca kaddara ta shafa saboda mugun misalin da ta kafa a harkar siyasa, inda babu sakamako ga wadanda suka tsere daga jam’iyya ko suka shiga, suna dauke da kujerunsu tare da su.

    Daga cikin gwamnonin 11 a watan Mayu 2023, biyu kacal Bala Mohammed na Bauchi da Seyi Makinde na Oyo ne suka rage a bangaren PDP.

    Mohammed, wanda ya yi kokari sosai wajen jan tsohon Shugaba Goodluck Jonathan cikin zaben shugaban kasa na 2027, ya ga mafarkinsa ya rushe yayin da jam’iyyar ke rugujewa a cikin rikice-rikicen shari’a, sauya sheka, da rikicin iko. Kuma jita-jita na cewa Bala na kan kusurwar barin duk abin da ya rage na tagwayen PDP tare da Makinde nan ba da jimawa ba.

    Kula Da Yadda Abubuwa Ke Tafiya

    Halin da ake gani a fadin Nijeriya gabadaya yana nuna sakamakon daya a zaben gama-gari na shekara mai zuwa nasara ga jam’iyyar APC mai mulki. Ba saboda kyakkyawan aikin da ta yi ba, sai don saboda ‘yan adawa, musamman ADC, sun shimfida tsari ta hanyar sanya kansu ba a matsayin madadi don canji ba, amma a matsayin wuri inda ‘yan siyasa kadan masu matsananciyar sha’awar mulki ke fafatawa.

    Ina dariya duk lokacin da ADC ke kiran kanta jam’iyyar adawa. Kusan tana adawa ne. Za ka yi mamaki ka san cewa wani babban jigon ADC yana sadaukar da kansa ga manyan shugabannin APC domin kare muradunsa na kasuwanci da ke cikin hadari.

    Tantance Tarihi

    A karshe, babban abokin adawar APC zai kasance APC kanta. Wannan shi ne darasin tarihi. Daga Jam’iyyar Conservative ta Birtaniya zuwa Indian National Congress, kuma daga African National Congress zuwa ragowar PDP ta Nijeriya (wadda nan ba da jimawa ba za ta dauki Tinubu a matsayin dan takararta), tarihi ya nuna cewa jam’iyyun da ke mulki akarshe suna lalacewa da raguwa daga cikin kansu.

    Hadewar rashin kulawa, rarrabuwar cikin gida, da gazawar daidaitawa da sabbin yanayi na jama’a, ko cin hanci da rashin dabi’a mai kyau, a karshe yana shafar su kuma ya rinjaye su.

    Halin APC ba zai bambanta ba, ba saboda hayaniyar da ADC ke yi ba.

    Ishiekwene shi ne Babban Editan jaridar LEADERSHIP kuma marubucin littafin Writing for Media and Monetising It.

    [ad_2]

    Source link

  •  “Yadda Na Shirya Gudanar Da Bikin Karamar Sallar Bana”

    [ad_1]

    Shafin TASKIRA shafi ne da ya saba zakulo muku batutuwa daban-daban wadanda suka shafi al’umma, ciki sun hadar da zamantakewar aure, rayuwar yau da kullum, rayuwar matasa, soyayya da dai sauransu.

    Tsokacinmu na yau zai yi duba game da abin da ya shafin Bikin Sallah Karama, kasancewar wannan rana ita ce ranar da ake shagulgulan Sallah Karama, ya sa wannan shafi jin ta bakin wasu daga cikin ma’abota shafin game da wannan batu; “Wane irin abinci da abin sha ake da muradin ci/sha da zarar an dawo daga sallar idi?, Wane wurare ake da sha’awar zuwa tare da kai ziyara?, A fadi muhimmancin zumunci wanda aka sani, wacce shawara za a bawa ‘yan’uwa musulmi game da abin da ya shafi bikin Sallah Karama?”.

    Ga dai bayanan nasu kamar haka:

    Sunana Abba Abubakar Yakubu daga Jos a Jihar Filato:

    Da farko dai zan fara da taya daukacin ‘yan’uwa Musulmi, Barka Da Sallah. Da fatan an sha ruwa lafiya. Allah Ya sa mun yi ibada karbabbiya cikin wannan wata mai albarka da muka yi bankwana da shi. Yanzu da ake bikin sallah karama, baki ya bude za a koma ciye-ciye da nishadi iri-iri don nuna murna da farin ciki. Ni dai na fi sha’awar abu mai ruwa-ruwa, don haka zan fi son in samu lemo ko ‘ya’yan marmari da soyayyen nama da cincin, don ban fiye son abu mai maiko ba. Bayan nan zan zauna a gida tare da iyali da makwafta, sai zuwa yamma bayan rana ta yi sanyi, zan fita zuwa gaishe da iyaye, kawunnai, da yayye a gidajensu, don yi musu gaisuwar Barka Da Sallah. Hakan yana da muhimmanci sosai a tarbiyyar addinin Musulunci da kuma al’ada ta Malam Bahaushe. Sada zumunci da tallafawa juna a irin wannan lokaci abu ne da yake sanya farinciki a zukatan ‘yan’uwa da surukai da sauran dangi. A raba abinci dafaffe da abin sha a tsakanin juna, a yi wa yara alheri wajen basu kyautar kudade da sunan goron sallah, hatta mata a cikin gidaje kar a manta da su. Ka bai wa mata da yaranka goron sallah, yana kara soyayya da farinciki a tsakanin iyali. Allah Ya maimaita mana na badin badada. Amin.

    Sunana Hafsat Sa’eed, daga Jihar Neja:

    Abin ci da sha duk wanda Allah ya bayar mu dai muna ganin shi ne daidai, ba mu da zabi sai na gurin Allah. Shawara kuma ga mutane, shi ne muna fatan yadda muka shiga cikin wannan watan sallah lafiya, Allah ya nuna mana na badi lafiya. Allah kuma ya karbi ibadunmu, ya saka mu cikin ‘yantattun bayi. Ayi sallah lafiya.

    Sunana Aminu Adamu Malam Madori:

    Allah ya karbi ibadarmu. Batun abinci kuma, waina (masa) da miyar yakuwa, zamu fara amfani da su bayan mun ci dabino mun tafi Sallar Idi, sai kuma abun sha shi ne Kunun Aya. To, batun ziyara kuma zamu ziyarci gidajen ‘yan’uwa da abokan arziki domin ayi gaishe-gaishe da zumunci, har ma da dubiya ga marasa lafiya, ‘yan’uwa da abokan arziki. Batun muhimmanci zumunci kuma abu ne wanda yafi gaban kidayawa domin addininmu musulunci yayi magana akan muhimmanci na zumunci da kuma sakamakon masu yin zumunci. Shawarata a nan ita ce, mutane su yi bukata daidai aljihunsu, domin lokaci ne me wucewa kada ayi gasa ko wuce gona da iri wajen bukata, daga karshe kuma ya kamata mu dage da addu’ar samun zaman lafiya a kasar mu Najeriya baki daya dama duniya.

    Sunana Fatima Nura Kila daga Jihar Jigawa

    Alhamdulillah gaskiya sai dai mu yi wa Allah godiya, ganin ga shi kamar yau za a fara amma har ana sallah. Gaskiya ni ana dawo wa nafi so na samu dan abin sha kafin akai ga abincin. Alhamdulillah zamu kai ziyara garin dangi da abokan ardiki. Gaskiya zumunci abu ne mai kyau, wanda mu mutanen yanzu bamu fiya damuwa da shi ba, amma zumunci ginshiki ne a rayuwar dan’adam. Ya kamata wadanda basu da shi su taimakawa na kasa da su domin kowa yayi bikin sallah lafiya cikin farinciki.

    Sunana Anas Bin Malik Achilafia ‘Yankwashi daga Jihar Jigawa:

    Da zarar an dawo daga Sallar Idi, mutane da yawa suna da muradin cin abinci irinsu; Tuwo da miya, Shinkafa, Fura da Nono, ko kayan zaki, tare da shan abubuwa kamar; Kunu ko Lemo domin yin walima tare da iyali. Haka kuma mutane sukan yi sha’awar ziyartar iyaye, dangi, abokai, da makwafta, domin kara dankon zumunci da farinciki. Muhimmancin zumunci kuwa shi ne yana karfafa soyayya da hadin kai a tsakanin al’umma, yana kawo zaman lafiya da taimakon juna. Don haka shawarar da zan ba wa ‘yan’uwa Musulmi ita ce su yi bikin Sallah cikin ladabi, su guji barna da aikata abubuwan da ba su dace ba a addinance da al’adance, su taimaki marasa karfi, kuma su karfafa zumunci da juna.

    Sunana Hassana Sulaiman daga Hadejia Jihar Jigawa

    Kai ziyara sun hada da gidajen ‘yan’uwa da abokan arziki domin samun ladan zumunci musamman a wannan rana. Zumunci na da muhimmanci sosai a addinin musulunci kuma abu ne wanda ma’aiki ya kwadaitar da mu a kansa, saboda falala dake cikinsa dan kuwa ubangiji ma ya jaddada muhimmancin da tagomashin da masu yinsa za su samu da kuma tsoratarwa ga masu yanke shi. Shawarar da zan bawa ‘yan’uwa musulman duniya bakidaya, su zama masu taimakon juna da kulawarsu ga masu karamin karfi dama makwaftansu har da hakkin zamantakewa domin rabauta gobe kiyama.

    Sunana Abubakar Usman Malam Madori:

    A lokuta da dama ana dafa shinkafa da miya da kifi ko nama, ko kuma Funkaso ko Masa domin liyafar sallah. A ranar idi, mutane da dama kan so su je gidajen iyaye, ‘yan’uwa da abokai domin gaishe su. Wasu lokuta ana zuwa yawon shakatawa kamar gidan tarihi, gidan Zoo da wuraren wasa. Zumunci yana kara kauna da hadin kai tsakanin ’yan’uwa, yana saka mutane su rika taimakon juna a lokacin bukata. Haka kuma yana kawo zaman lafiya da fahimtar juna a cikin iyali. Shawara ya kamata Musulmai su yi bikin cikin godiya ga Allah bayan kammala azumin Ramadan, su kula da yin sallar idi tare da kuma sanya kyawawan tufafi, haka kuma su rika bayar da Zakkah domin taimakon marasa galihu.

    Sunana Jibrin Yusuf Kaila, daga garin Hadejia, Jihar Jigawa:

    Zumunci wani muhimmin jigo ne mai babbar daraja da lada a addinin Musulunci, haka ma a al’adar Bahaushe. Zumunci ne ginshikin al’adar da muka gada daga iyaye da kakanni. Zumunci na nufin kula da dangantaka tsakanin ‘yan’uwa ta hanyar gaisuwa, taimako, da ziyara. Lokacin bikin Sallah Karama, lokaci ne na ziyara. Kuma lokaci ne da yake daga cikin lokuta mafi dacewar karfafa zumunci, domin mutane sukan samu damar komawa gida su gana da iyayensu, ‘yan’uwansu da makusanta, musamman wadanda suka yi nisa da ‘yan’uwansu, saboda wasu dalilai irin na aiki ko cirani. Sannan lokaci ne da yake kawo albarka da lada a addini. A koyarwar Musulunci, kula da ‘yan’uwa da ziyartar su ibada ce mai girma. Duk wanda yake kyautatawa danginsa yana samun lada, kuma hakan yana sa Allah ya sanya albarka a rayuwarsa da zaman lafiyar iyalinsa. Saboda haka ina mai karfafa mana gwiwa kan muhimmancin ziyara a lokacin bukukuwan sallah, kasancewarsa aiki mai dimbin ladan a addinin Musulunci.

    Sunana Sadik Abubakar Abdullahi, Rijiyar Lemo, Karamar hukumar Dala, daga Jihar Kano:

    Bayan dawowa daga sallar Idi, abincin da na fi sha’awar ci shi ne tuwon shinkafa da miyar taushe, tare da abin sha kamar kunun aya mai sanyi. Wannan lokaci ne na farinciki da iyalai ke taruwa su ci abinci tare. A wannan rana ta sallah in sha Allah zan ziyarci ‘yan’uwa da abokan arziki domin a gaisa, a yi wa juna fatan alheri don kara dankon zumunci. Zumunci yana da muhimmanci sosai a rayuwar al’umma, domin yana kara kauna, hadin kai da taimakon juna tsakanin mutane. Haka kuma addinin Musulunci ya yi umarni da kiyaye shi domin yana kawo zaman lafiya da fahimtar juna. Shawarata ga ‘yan’uwa Musulmi ita ce mu yi bikin sallah cikin nutsuwa da nuna godiya ga Allah, mu tuna da marasa galihu ta hanyar taimako, mu kuma guji almubazzaranci da duk wani abu da zai iya jawo sabani ko bata tarbiyyar matasa.

    Sunana Hassana Yahaya Iyayi (Maman Noor) daga Jihar Kano:

    Ai san samu a samu Sunasir da miyar taushe ko wainar shinkafa da miyar taushe gefe a samu Zobo mai sanyi ko lemon Ayya. Wurin zuwa dai san samu kwashi yara muje dan ziya gidanmu. Zumunci abu ne mai muhimmanci, Ubangiji da kansa ya ce tsagi ne daga jikin sunansa Arrahamanu, ayi komai cikin kiyaye dokokin ubangiji.

    [ad_2]

    Source link

  • Isra’ila ba za ta sake kai hari kan cibiyoyin makamashin Iran ba — Netanyahu

    [ad_1]



    Firaministan Isra’ila, Benjamin Netanyahu, ya sanar da cewa ƙasarsa za ta dakata da kai hare-hare kan cibiyoyin makamashin Iran.

    Wannan mataki ya biyo bayan gargaɗin da Shugaban Amurka, Donald Trump, ya yi wa Isra’ila na cewa kada ta sake kai irin wannan hari.

    A ranar Laraba, Isra’ila ta kai hari kan wata babbar cibiyar sarrafa iskar gas ta Iran mai suna South Pars, lamarin da ya sa Iran ma ta mayar da martani.

    Waɗannan hare-hare sun haddasa tashin farashin man fetur da iskar gas a kasuwannin Turai da ma duniya baki ɗaya.

    Yayin da yake jawabi ga manema labarai a ranar Alhamis, Netanyahu ya tabbatar da cewa: “Ba za mu sake kai hari kan cibiyoyin makamashin Iran ba.”

    Haka kuma, ya ƙaryata zargin da ake yi na cewa shi ne ya zuga Trump ya kai hari kan Iran.

    Ya bayyana cewa: “Babu wanda zai iya faɗa wa Shugaba Trump abin da zai yi. Shi kansa yana yanke shawara ne bisa abin da ya ga ya dace.”

    Ya ƙara da cewa: “Shugaba Trump yana ɗaukar matakai ne domin maslahar Amurka da kuma makomar duniya baki ɗaya.”


    [ad_2]

    Source link

  • Nazarin CGTN: Matakin Amurka Na Kaddamar Da Yaki Zai Rage Karfinta Na Babakere

    [ad_1]

    A lokacin da hare-haren Isra’ila da Amurka kan Iran suka koma kan kayayyakin samar da makamashi, yakin ya shiga wani sabon babi, inda Amurka ke gaggauta jefa kanta cikin tsaka mai wuya.

    Wani nazarin jin ra’ayoyin jama’a da kafar CGTN ta gudanar ta intanet ya nuna cewa, kaso 94.1 na masu bayyana ra’ayoyinsu sun yi imanin cewa, hare-haren soji kan Iran, zai gaggauta raguwar karfin Amurka na babakere.

    Cikin nazarin, kaso 90.9 na masu bayar da amsa sun ce hare-haren Amurka kan Iran na nuna dawowar ayyukan ta’addanci na Amurkar. Haka kuma, kaso 93.8 sun amince cewa, hare-haren kan Iran ba su halatta ba, kuma ba su da hujja. Har ila yau, kaso 89.1 na ganin matakin Amurka na kaddamar da yakin yunkuri ne na kare babakeren takardar kudi na dala da kuma sace albarkatun man Iran.

    Kafar CGTN ta wallafa nazarin ne a dandalolinta na harsunan Ingilishi da Sipaniyanci da Faransanci da Larabci da Rashanci, inda cikin sa’o’ 24, musu amfani da kafar intanet 18,906 suka bayyana ra’ayoyinsu. (FMM)

    [ad_2]

    Source link

  • Gwamnonin Arewa Sun Yi Tir Da Tashin Bama-bamai A Maiduguri

    [ad_1]

    Shugaban Kungiyar Gwamnonin Jihohin Arewa, Muhammadu Inuwa Yahaya, ya yi Allawadai da fashewar jerin bama-bamai masu muni da suka girgiza Maiduguri a ranar Litinin, inda ya bayyana harin a matsayin na rashin imani, na ta’addanci a kan fararen hula.

    Rahotanni sun nuna cewa tashin jerin bama-bamai wadanda wasu ‘yan kunar bakin wake suka aiwatar sun tashi ne a lokaci guda da yammacin ranar Litinin a kasuwar Maiduguri Monday Market, kofar shiga asibitin Koyarwa na Jami’ar Maiduguri (UMTH) da kuma Post- Office flyober dukka a Maiduguri babbar birnin jihar Borno.

    • Shettima Ya Ziyarci Waɗanda Harin Bam Ya Shafa A Maiduguri
    • Ana Neman Hankada Yankin Gabas Ta Tsakiya Cikin Mummunan Rami In Ji Wakilin Kasar Sin

    ‘Yansanda sun ce mutane 23 ne suka rasa rayukansu, yayin da wasu sama da 100 suka jikkata.

    A cikin sanarwar da ya fitar a matsayinsa na Shugaban Kungiyar Gwamnonin Jihohin Arewa, Gwamna Inuwa Yahaya ya bayyana matukar jimami da alhininsa kan wannan mummunan hare-haren, tare da mika sakon ta’aziyyarsa ga gwamnati da al’ummar Jihar Borno, musamman iyalan wadanda suka rasa ‘yan uwansu.

    Inuwa wanda kuma shi ne gwamnan jihar Gombe ya ce, “Wannan mummunan aika-aikar na tashin hankali ba wai kawai abin kyama ba ne, wani yunkuri ne na zalunci da nufin haifar da tsoro da kuma kawo cikas ga zaman lafiyar da ake kokarin dawo da shi a yankin Arewa maso Gabas.”

    Sanarwar da Isma’ila Uba Misilli, Darakta-Janar na harkokin yada labarai na gidan jihar gwamnatin Gombe ya sanya wa hannu, Gwamna Inuwa ya ce, dole ne a yi Allah-wadai da hare-haren.

    Shugaban Kungiyar Gwamnonin Arewa ya jajanta wa wadanda ke kwance a asibiti a halin yanzu domin samun kulawar likitoci sakamakon raunuka da suka samu a hare-haren, tare da yi musu addu’ar samun sauki cikin gaggawa.

    Kazalika, ya kuma yaba wa jami’an agajin gaggawa da hukumomin tsaro kan yadda suka gaggauta daukar mataki wajen shawo kan halin da aka shiga bayan fashe-fashen.

    Ya sake jaddada kudurin gwamnonin Arewa na ci gaba da aiki kafada-kafada da Gwamnatin Tarayya da kuma hukumomin tsaro domin yakar dukkan nau’o’in ta’addanci da ayyukan laifi da ke barazana ga zaman lafiya da kwanciyar hankali a shiyyar arewa maso gabas.

    Inuwa ya budaci mazauna al’ummar Maiduguri da sauran yankunan da suke shiyyar da su kwantar da hankulansu, su kasance masu ci gaba da bin doka da oda, tare da bada cikakken hadin kai da hukumomin tsaro ta hanyar bayar da sahihan bayanai da za su taimaka wajen binciken da ake yi da kuma taimaka musu a duk lokacin da bukatar hakan ta taso domin dakile ayyukan ta’addanci.

    “A halin yanzu fiye da kowane lokaci, wajibi ne mu tsaya tsayin daka tare domin yakar makiyan zaman lafiya. Ba za mu yi kasa a guiwa kan yunkurinmu na dawo da zaman lafiya a shiryar arewa maso gabas ba, tare za mu kawo karshen wannan matsalar tsaron,” ya jaddada.

    Gwamna Inuwa Yahaya ya yi addu’ar Allah ya jikan wadanda suka rasa rayukansu a wannan hare-haren, tare da kira ga hukumomin tsaron da su kara zage damtse domin ganin an kamo wadanda suka aikata wannan mummunan aika-aikar kuma a hukunta su cikin gaggawa.

    [ad_2]

    Source link