Category: Latest News

  • Ƙasashen Afirka Sun Fara Neman Man Fetur Daga Nijeriya, Dangote Ya Ƙara Farashi

    [ad_1]

    Matatar man Dangote ta fara fuskantar buƙatar man fetur mai yawa daga ƙasashen Afirka. Hakan na zuwa bayan rikicin Amurka da Isra’ila kan ƙasar Iran ya katse hanyoyin samar da mai.

    Kamfanin ya ce ƙasashe kamar Afirka ta Kudu da wasu sun nemi kayayyaki a wurinsa, A lokaci guda, ya ƙara farashin Fetur daga N1,175 zuwa N1,245 kan kowace lita.

    • Dangote Da GCL Sun Ƙulla Yarjejeniyar Gina Masana’antar Taki A Habasha
    • Matatar Dangote Ta Sake Ƙara Farashin Fetur Zuwa ₦1,175

    A sanarwar da ya fitar, ya jaddada cewa tashin farashin ya biyo bayan matsin lambar siyasar duniya da bangaren makamashi ke fuskanta. Ya kuma tabbatar da cewa sabon farashin zai fara aiki daga tsakar daren 21 ga Maris, 2026.

    Rahoton ya nuna farashin mai a bakin teku ya tashi zuwa N1,606,518 kan kowace ton. Hakan ya biyo bayan hauhawar farashin ɗanyen mai da tsadar sufuri a duniya.

    Ana sa ran ƙarin zai shafi kasuwar cikin gida, inda masu sayarwa za su ƙara farashi. Wannan na nuna kasuwar mai a Najeriya na ci gaba da dogaro da yanayin duniya har yanzu wajen yanke farashi.

    [ad_2]

    Source link

  • Nazari A Kan Noman Agwaluma

    [ad_1]

    Ba a cika bai wa noman Agwaluma muhimmanci kamar yadda ake bai wa sauran amfanin gonar da ake shukawa a Nijeriya ba.

    A yaren Yarbanci, ana kiran ta da Agbalumo, da Iyamuranci; ana kiran ta da Udara, a Jihar Edo; ana kiran ta Otien, inda a yaran Hausa kuma ake kiran ta da Agwaluma.

    • Wang Yi Ya Zanta Ta Wayar Tarho Da Ministar Harkokin Wajen Birtaniya
    • Aikin Zamantar Da Tashoshin Jiragen Ruwan Nijeriya Zai Rage Wa Kasa Asasar Naira Tiriliyan Daya —Dantsoho

    Manoman da suka shiga cikin fannin, musamman a Nijeriya, na samar wa da kawunansu kudaden shiga masu yawa, haka a daukacin Nijeriya, babu wani  addini da ya haramta yin amfani da ita, haka nan kuma; tana kara samun karbuwa a kasuwannin kasar nan.

    Yadda Ake Shuka Irin Agwaluma:

    Za ka iya shuka Irin nomanta, inda ake bukatar kada Irin ya wuce  tsawon wata hudu, inda a lokacin da za ka yi shukar ake bukatar ka tabbatar da ka yi a lokacin rani.

    Har ila yau, nau’in Agwaluma na agbalumo ko kuma na Udara, na bukatar yi masa ban ruwa sosai, musamman don ya yi saurin nuna a cikin kasar noman da aka shuka shi.

    Bugu da kari, idan manomi zai sayo Irin nomansa, ya tabbatar da ya sayo a gurin da aka fi sani, musamman don ya samu ingantacce kuma mai lafiya.

    Ba Ta Kariya Daga Kamuwa Da Kwari Ko Sauran Cututtukan Da Ke Harbin Amfanin Gona:

    Ana bukatar manomi ya tabbatar da yana ba ta kariya daga harbin kwari ko cututtukan da ke yi mata illa bayan ana shuka ta, domin irin wadannan cututtukan ko kwarin na iya hana Irinta da aka shuka ruba a cikin kasar noman da aka shuka Irin.

    Zuwa Tsawon Wane Lokaci Agwaluma Ke Kammala Girma?

    Bayan an shuka Agwaluma, musamman Gona na fara fitar da ‘ya’yanta ne daga shekara biyar zuwa 10, inda kuma ake saran saiwar  jikinta, domin adana wa ta fi bukatar yanayin da ya kai ma’unin yanayi daga 60 zuwa 70.

    Har ila yau, wasu sun yi hasashen cewa, ba za a iya yin noman Agwaluma a Nijeriya ba, amma maganar ba haka take ba; domin ana iya yin nomanta kuma ta yi kyau sosai har dimbin wacce za a yi hada-hadar kasuwancinta abin da kawai ake bukata shi ne, mayar da hankali kan shuka ta da aka yi da nuna kwarin gwiwa da kuma ba ta kulawar da ta dace.

    Abubuwan Da Ya Kamata A Tanada Na Noman Agwaluma Don Samun Riba A Nijeriya

    Samar Da Kyakkyawan Tsari:

    Kafin ka fara yin nomanta, ka tabbatar ka tsara  yadda noman nata zai kasance, musamman domin kaucewa yin asara bayan ka  zuba jarinka a ciki.

    Gyaran Gonar Shuka Ta:

    Kafin ka shuka Irinta, ana bukatar ka tabbatar da kasar noman nata mai kyau ce.

    Zabo Nau’in Da Ya Dace:

    Na bukatar ka zabo daga cikin nau’ukanta biyu, wato na  Udara ko kuma na Agbalumo, inda ake iya gano su ta hanyar girmansu.

    Amfanin na kai wa tsawon shekara takwas kafin ta kammala girma, inda kuma aka kara habaka nau’insa wanda zai iya girma bayan shekara uku.

    Yadda Ake Girbe Agwaluma:

    Akasari, ana  girbe ta ne a watan Disamba, sai dai a wannan lokaci, ba ta yin dadi sosai; saboda haka, ana so a bar ta a gonar da aka shuka ta har wani ruwan saman ya kara dukan ta kafin a girbe ta, inda ake  yi mata girbin bayan Ganyen ta ya rikide zuwa ruwan dorawa.

    Tsara Dabarun Hada-Hadar Kasuwancinta:

    Bayan an shuka ta ta girma, za a iya kai ta kasuwa don sayarwa, domin ana nuna ci gaba da batan ta a kasuwa ganin cewa, ana yawan yin amfani da ita. Haka kuma manomi, zai iya wallafa tallan ta a kafar yanar gizo, don masu bukata su gani su kuma saya.

    [ad_2]

    Source link

  • Yadda Ake Samun Biliyoyin Daloli A Noman Zogale Da Kantu A Tekun Chadi

    [ad_1]

    Shirin samar da abinci na duniya (WFP), ya yi nuni da cewa; za a iya samun kudaden shiga na kimanin biliyoyin daloli a noman Zogale da Kantu a Tekun Chadi, matukar an kara inganta tsaro da zaman lafiya a wannan kasa.

    Mai wakiltar shirin a Nijeriya, Dabid Stebeson ya bayyana hakan ne a taron da aka yi karo na biyar na kungiyar gwamnonin yankin Tekun Chadi da aka gudanar a garin Maiduguri na Jihar  Borno.

    • An Gudanar Da Taron Tattaunawa Na Duniya Na “Sin A Yanayin Bazara” A Brazil
    • Aikin Zamantar Da Tashoshin Jiragen Ruwan Nijeriya Zai Rage Wa Kasa Asasar Naira Tiriliyan Daya —Dantsoho

    “Yarjejeniyar hada-hadar kasuwanci ta Afirka (AfCFTA), ta bayar da damar bunkasa hada-hadar kasuwanci tare da farfado da tattalin arzikin kasar, idan har aka bunkasa fannin aikin noma da kiwo.”

    Mai wakiltar shirin ya sanar da cewa, bisa hadin kai a yankin da kuma wanzar da kuduri irin na siyasa, yankin zai iya magance kalubalen rashin abincin da za a ciyar da al’ummar da ke yankin.

    Sai dai, Stebeson ya nuna takaicinsa kan cewa; duk da yawan sama da mutane miliyan bakwai da ke yankin, har yanzi al’ummar yankin na ci gaba da zama cikin karancin abinci.

    A cewarsa, sama da mutane miliyan uku rikice-rikicen ta’addanci ya tilasta wa yin kaura daga matsugunansu.

    Har ila yau, ya shawarci kungiyoyin da ke yankin; kan bukatar yin hadin kai mai karfi da samar da tsare-tsaren da za su habaka aikin noma da kiwon Kifi a yankin.

    [ad_2]

    Source link

  • Za mu ƙara ƙaimi wajen daƙile matsalar tsaro — Radda

    [ad_1]



    Gwamnan Jihar Katsina, Malam Dikko Umar Radda, ya jaddada aniyar gwamnatinsa na ƙara ɗaukar matakan da suka dace domin daƙile matsalar tsaro a faɗin jihar.

    Radda ya bayyana haka ne bayan kammala sallar Eid-el-Fitr a garin Batagarawa, inda ya ce gwamnatinsa ba za ta yi ƙasa a gwiwa ba wajen tabbatar da zaman lafiya da kare rayuka da dukiyoyin al’umma.

    Gwamnan ya kuma nuna alhininsa kan hare-haren ‘yan bindiga da suka auku a ƙauyukan Falale da Kadobe da ke ƙaramar hukumar Jibiya, tare da kira ga al’umma da su ƙara haɗa kai da juna.

    Ya buƙaci musulmi da su ci gaba da yin addu’o’i domin samun zaman lafiya mai ɗorewa a jihar da ma ƙasa baki ɗaya.

    Radda ya halarci sallar ne bayan dawowarsa daga ƙasar Birtaniya, inda ya kasance cikin tawagar da ta yi rakiyar Shugaba Bola Ahmed Tinubu, ziyarar aiki ta kwanaki biyu a ranar 18 da 19 ga watan nan.

    A halin yanzu, ana ci gaba da gudanar da shagulgulan Sallah a sassan jihar cikin kwanciyar hankali.


    [ad_2]

    Source link

  • Bayan Kwana 30, Har Yanzu ICPC Na Ci Gaba Rike El-Rufai

    [ad_1]

    Wata guda bayan Hukumar Yaki da Cin Hanci da Rashawa da Sauran Laifukan da Suka Shafi Rashawa (ICPC) ta kama tsohon gwamnan Jihar Kaduna, Nasir El-Rufai, har yanzu bai bayyana a gaban kotu ba, in ji rahoton Daily Trust.

    Hakan na zuwa ne yayin da Kotun Daukaka Kara da ke Kaduna jiya ta soke hukuncin da Babbar Kotun Kaduna ta yanke, wacce ta yi watsi da hakkin El-Rufai na kalubalantar binciken da Majalisar Dokokin Jihar Kaduna ta yi masa kan zargin cin hanci.

    • Wang Yi Ya Zanta Ta Wayar Tarho Da Ministar Harkokin Wajen Birtaniya
    • Tsayuwa Da Kafa Biyu Ya Fi Tsayuwa Da Kafa Daya

    El-Rufai ya yi kwana biyu a hannun Hukumar Yaki da Laifukan Kudi da Tattalin Arziki (EFCC) kan zargin aikata laifukan kudi lokacin da yake gwamna, kafin Hukumar Tsaro ta Kasa (DSS) da daga bisani ICPC su kama shi.

    A ranar 16 ga Fabrairu, tsohon gwamnan ya amsa gayyatar da EFCC ta yi masa, inda jami’an bincike na hukumar suka yi masa tambayoyi masu tsanani.

    Wannan ya biyo bayan rashin nasarar jami’an tsaro wajen kama shi a filin jirgin saman Abuja lokacin da ya dawo daga Masar.

    Abin da ya faru a gaban kotu

    Lauyoyi sun ce duk da cewa kotu na iya kara wa’adin tsare mutum, yin hakan ba tare da umarnin kotu ba ya keta sashe na 293–296 na Dokar Gudanar da Shari’ar Laifuka (ACJA).

    Rahoton Daily Trust ya nuna cewa ICPC ta samu umarnin tsare El-Rufai na kwanaki 14 daga Babban Kotun Magistrate da ke Bwari, FCT a ranar 19 ga Fabrairu, wanda daga bisani aka sabunta.

    Sai dai, lauyoyin El-Rufai sun shigar da kara suna kalubalantar karin wa’adin tsaron da ICPC ta nema, inda suka gabatar da dalilai da dama da aka shirya yanke hukunci a kansu jiya.

    Ana sa ran Mai Shari’a Okechukwu Akweke zai yanke hukunci a ranar 19 ga Maris.

    A cikin karar da aka gabatar a gaban kotun magistrate, El-Rufai ya zargi jami’an ICPC da cewa sun nemi ya daina shiga harkokin siyasa a matsayin sharadin sakinsa daga tsarewa, inda ya bayyana hakan a matsayin take hakkokin sa na kundin tsarin mulki.

    A cewar bayanan, ya fara bayyana kansa ga EFCC a ranar 16 ga Fabrairu, inda aka ba shi belin fitarwa, sai dai DSS ta kama shi sannan daga baya ta mika shi ga ICPC ba tare da izini na doka ba, wanda ya haifar da tsare shi ba bisa ka’ida ba.

    Karar ta zargi manyan jami’ai, ciki har da shugaban ICPC da Daraktan Janar na DSS, da tsare mutum ba bisa ka’ida ba da hana ’yanci. Tawagar lauyoyin sa ta kuma jaddada cewa umarnin tsaron da aka bayar ba shi da inganci kuma tsarewar sa ta wuce lokacin da doka ta kayyade ba tare da hujja mai karfi ba.

    Bugu da kari, El-Rufai ya yi ikirarin cewa an tsare shi ba tare da samun hulda da wani ba, an hana shi ziyartar iyali, lauyoyi, da samun kulawar lafiya, matakan da lauyoyinsa ke cewa sun saba wa tsarin shari’a da ’yancin mutum a karkashin dokokin Nijeriya.

    An takura mu da yawan kararraki – ICPC

    Yayin da yake magana da daya daga cikin ma’aikatanmu da yamma jiya, babban jami’i a ICPC ya bayyana cewa shari’o’i da dama da aka shigar kan hukumar suna jinkirta gabatar da tsohon gwamnan a gaban kotu.

    Ya ce duk wani umarnin dakatarwa da aka yi kan ICPC dole ne a soke kafin hukumar ta iya gabatar da tsohon gwamnan a kotu.

    “El-Rufai shi ne ke jinkirta gabatar da kansa a kotu. Ya shigar da shari’o’i daban-daban kan hukumar. Don haka, dole ne a soke wasu daga cikin wadannan shari’o’in kafin mu ci gaba bisa doka,” in ji jami’in.

    Kakakin ICPC, John Odey, a cikin wata sanarwa da ya fitar jiya, ya jaddada cewa matsayin tsarewar El-Rufai har yanzu yana bisa doka.

    Ya ce lauya ga tsohon gwamnan ne ya nemi tsawaita wa’adin shari’o’in da aka shigar kan tsawaita tsarewar El-Rufai.

    Odey ya ce: “Hukumar Yaki da Cin Hanci da Rashawa da Sauran Laifukan da Suka Shafi Rashawa (ICPC) na son fayyace matsayin doka na tsare tsohon Gwamnan Jihar Kaduna, Mallam Nasir Ahmad El-Rufai.

    “Wannan sanarwa ta zama dole ne domin gyara rahotanni marasa inganci daga wasu kafofin yada labarai da ke nuna cewa hukumar tana kotu a yau, 17 ga Maris 2026, tana neman sabuwar tsawaita tsarewar sa.”

    “Hukumar ta bayyana a kotu a yau don sauraron bukatar Mallam El-Rufai, wadda aka tsara kuma aka shigar a ranar 6 ga Maris, 2026, wadda ke neman soke umarnin kotu na tsawaita tsarewarsa da aka bayar a ranar 5 ga Maris, 2026.

    “Yayin zaman kotu na yau, lauya ga Mr. El-Rufai an mika masa martanin mu kan bukatarsa. Daga baya lauya ya nemi a dage zaman domin ya mayar da martani kan amsar hukumar.

    “Saboda haka, Mai Shari’a ya dage sauraron bukatar zuwa 31 ga Maris, 2026 domin ba tawagar Mr. El-Rufai isasshen lokaci don mayar da martani ga amsarmu.

    “Don sanar da jama’a, hukumar ta bayar da wannan jadawalin na tsarewar da kotu ta amince da shi.

    “An bayar da umarnin farko na tsarewa, wanda ya ba hukumar damar tsare wanda ake zargi na tsawon kwanaki 14 domin bincikar zargin yin watsi da kudi da kuma amfani da mukami ba bisa ka’ida ba.

    “Bayan karewar umarnin farko, hukumar ta nemi karin tsawon kwanaki 14 domin kammala bincikenta, wanda kotu ta amince da shi a ranar 5 ga Maris, 2026.

    “Lauya ga El-Rufai ya yi kokarin soke umarnin tsarewar da aka bayar a ranar 19 ga Fabrairu, 2026, amma an ki wannan bukata a ranar 9 ga Maris, 2026.

    “Mallam El-Rufai har yanzu yana hannun ICPC bisa doka karkashin umarnin tsarewar da aka bayar a ranar 5 ga Maris, 2026.”

    Kakakin ICPC ya ce hukumar na bin ka’idojin da kotu ta bayar a kan lokaci, ciki har da bukatar bayar da rahoton ci gaba.

    A cewarsa, ICPC na gudanar da ayyukanta cikin kwarewa ta musamman da girmama dokokin kasa.

    “Tsarewar Mr. El-Rufai an amince da ita ne ta hanyar kotu bisa ga Dokar Gudanar da Shari’ar Laifuka (ACJA) 2015.

    “Bugu da kari, ICPC tana tsaye tsayin daka wajen bin tsarin ta na kauce wa shari’a ta kafafen yada labarai. Muna ganin ya kamata a warware rikice-rikicen shari’a a kotu, ba a shafukan jaridu ko kafafen sada zumunta ba,” in ji shi.

    [ad_2]

    Source link

  • Kuncin Rayuwa: Jam’iyyun Adawa Da Kungiyar Kwadago Sun Caccaki Tinubu

    [ad_1]

    Jam’iyyar ADC ta caccaki gwamntin Shugaban kasa, Bola Tinubu kan kuncin rayuwa a Nijeriya tare da musanta cewa, jam’iyyar APC ta gudanar da sauye-sauyen tattalin arziki na Tinubu, da suka kawo saukin rayuwa.

    Sai dai kuma APC ta mayar da martini kan wannan lamari, ta zargi jam’iyyar adawa ta ADC da yaudarar ‘yan Nijeriya ta hanyar zargin Shugaba Tinubu kan kashi 63 na talauci a kasar kamar yadda bincike ya nuna a makon da ya gabata.

    • Ana Neman Hankada Yankin Gabas Ta Tsakiya Cikin Mummunan Rami In Ji Wakilin Kasar Sin
    • Rawar Da Sashen Ayyukan Hidimomi Da Biyan Bukatu Ke Kara Takawa A Kasar Sin

    Binciken masu ruwa da tsaki da aka shirya tattaunawa a Abuja, ya nuna cewa yawan talauci a kasa nan ya tashi sosai daga matsakaicin kaso kusan 49.8 cikin dari zuwa kusan 63 cikin dari bayan cire tallafin mai kafin ya dan ragu kadan bayan gabatar da matakai masu tsauri.

    Da yake magana kan lamarin, sakataren yada labarai na jam’iyyar ADC na kasa, Malam Bolaji Abdullahi, ya jaddada cewa bayanan sun nuna cewa matakin talauci a Nijeriya ya haura zuwa kashi 63 cikin dari, daga kusan kashi 50 cikin dari kafin a cire tallafin mai.

    Abdullahi ya tabbatar da cewa rahoton da ya nuna cewa kashi 93 cikin dari na ‘yan Nijeriya suna ganin kasar na tafiya a mummunan hanya ba batutuwan jam’iyyar adawa ba ne kan lamarin.

    Ya ce rahotannin sun nuna karara cewa manufofin gwamnatin APC kan tattalin arziki ba sa tafiya kan ceto rayukan ‘yan Nijeriya karkashin mulkin Tinubu.

    Mai magana da yawun ADC ya ce maimakon mayar da hankali kan magance talauci da kuncin rayuwa da ya dabaibaye ‘yan Nijeriya a karkashin wannan gwamnati, jam’iyyar mai mulki ta ci gaba da farmakan jam’iyyun adawa tare da yin watsi da ceto rayukan miliyoyin ‘yan kasa.

    Ya kara da cewa ba za a iya watsi da gaskiya ta hanyar bayanan jarida ba, yana jaddada cewa rahoton ‘yanci da ya haifar da muhawara yana nuna cewa yawan talauci a Nijeriya ya kai kashi 63 cikin dari, daga kusan kashi 50 kafin a cire tallafin man fetur.

    “Wannan na nufin cewa wasu karin miliyoyin ‘yan Nijeriya za a kara tilasta musu shiga cikin talauci a wannana lokacin da aka gabatar da manufofin tattalin arziki da gwamnatin APC ta gaza aiwatarwa.”

    ADC ta kara da cewa yayin da APC ke ikirarin cewa ‘yan Nijeriya suna goyon bayan sauye-sauyen da gwamnati Tinubu ta aiwatar a kasar nan, amma kuma bayanan sun nuna akasin haka.

    Mai magana da yawun jam’iyyar adawa ya ce binciken masu zaman kansu sun nuna cewa kashi 93 cikin dari na ‘yan Nijeriya suna ganin cewa kasar na tafiya a mummunan shugabanci.

    “Kashi tamanin da takwas cikin dari suna bayyana tattalin arzikin kasa a matsayin mara kyau, yayin da kashi 74 cikin dari ke suna rayuwa cikin kangin talauci. Wadannan ba maganganu ne na ‘yan adawa ba. Ra’ayoyin ‘yan Nijeriya ne da kansu ciki har da ‘yan APC.”

    ADC ta ce yayin da APC ke dagewa kan cewa wahalar da ‘yan Nijeriya ke sha ta kasance ta wucin gadi ne, said ai kuma alkaluma suna ba da wani labari daban.

    “Binciken baya-bayan nan ya nuna cewa kashi 82 cikin dari na ‘yan Nijeriya bas a samun isasshen abinci a kalla sau daya a cikin shekarar da ta gabata, kashi 82 cikin dari na fama da rashin kula da lafiya, kashi 79 cikin dari sun daina amfani da man girki, kashi 74 cikin dari na fama da rashin tsaftar ruwa, kuma kashi 95 cikin dari na fama da rashin samun kudade a wani lokaci cikin shekarar. Wadannan alkaluma ba su nuna rashin jin dadi na dan lokaci ba, amma suna nuna talauci da kuncin rayuwa mai tsanani,” in ji ADC.

    A yayin da take mayar da martani kan ikirarin APC game da matakan tattalin arziki, ADC ta ce ‘yan Nijeriya na rayuwa kuncin tattalin arziki, inda farashin man fetur ya karu kusan kashi 500 cikin dari, daga kusan naira 255 a kowanne lita a watan Mayu 2023 lokacin da Tinubu ya hau mulki, zuwa kusan naira 1,500 a kowanne lita a yau a wurare da dama na wannan kasa.

    “Wannan yana kara tsadar sufuri kuma yana kara farashi kayayyaki abinci fiye da abin da miliyoyin gidaje za su iya saya.”

    ADC ya kara sukar da’awar APC kan kudin da ake kashewa kan tallafin mai, wanda ya kamata ya kai kusan naira tiriliyan 6.4 a asusun ajiya a bara kadai, sai yanzu ne ake karkatar da shi zuwa wasu sassa masu muhimmanci kamar kiwon lafiya da ci gaban al’umma.

    Jam’iyyar adawa ta ce a rubuce yake cewa naira miliyan 36 kawai, kusan kashi 0.02 cikin dari na manyan ayyuka a cikin kasafin kudin, don ainihin ayyukan jari a shekarar 2025 ga dukkan sashen kula da lafiya na tarayya na Najeriya.

    “Saboda haka, ‘yan Nijeriya suna bukatar amsar wadanan tambayoyi masu sauki. Idan an tanadi kudaden tallafin mai tare da rarraba su zuwa muhimman sassan, to a ina dukkan kudin ke tafiya? Me ya sa aka kasa biyan ‘yan kwangiloli na cikin gida? Me ya sa jami’o’i har yanzu ba su da kayan aiki masu kyau?”

    [ad_2]

    Source link

  • Rikicin Mashigar Hormuz: Ƙasashen Afirka sun koma sayen fetur a matatar Dangote

    [ad_1]



    Wasu ƙasashen Afirka, ciki har da Afirka ta Kudu, Ghana da Kenya, sun fara dogaro da matatar man Dangote da ke Najeriya domin samun man fetur, sakamakon cikas wajen jigilar mai daga Gabas ta Tsakiya.

    Ƙarancin man ya samo asali ne daga rikicin da ke faruwa tsakanin Isra’ila, Amurka, da Iran, wanda hakan ya sa aka toshe hanyar jigilar mai ta Mashigar Hormuz, wadda ta ke muhimmiyar hanyar kasuwancin mai ta duniya.

    Shekaru da dama, ƙasashen Afirka sun dogara ne da matatun man Gabas ta Tsakiya.

    Amma yanzu da aka samu matsala, dole ta sa suka fara neman wasu hanyoyin na daban.

    A halin yanzu, matatar man Dangote, mallakar hamshaƙin attajirin nan Aliko Dangote, ita ce suka fara dogara da ita.

    Matatar wadda ke Jihar Legas, tana da ƙarfin tace ɗanyen mai har ganga 650,000 a kowace rana.

    Matatar mai darajar dala biliyan 20 ta fara aiki ne a shekarar 2024, kuma tana ci gaba da bunƙasa ayyukanta.

    Buƙatar man fetur daga ƙasashen Afirka na ƙaruwa, inda wasu ƙasashen ma suka fara tattaunawa don ƙulla yarjejeniyar sayen man.

    Wannan yanayi ya nuna yadda Afirka ta daɗe tana dogaro da shigo da tataccen mai daga ƙetare, har ma da ƙasashen da suke da ɗanyen mai a ƙasa.

    Misali, a baya Najeriya kan fitar da ɗanyen mai sannan ta sake sayen tataccen man da tsada daga waje.

    Duk da cewa matatar Dangote na taimakawa wajen magance wannan matsala, mafi akasarin man da take tacewa a halin yanzu ana amfani da shi ne a cikin gida, yayin da kaso ƙalilan ake fitarwa zuwa sauran ƙasashen Afirka.

    Masana na ganin cewa matatar ita kaɗai ba za ta iya biyan buƙatun ɗaukacin nahiyar Afirka ba, musamman ganin yadda ƙasashe da dama ba su da isassun wuraren adana man fetur.

    Wasu gwamnatoci sun riga sun fara ɗaukar matakan kariya; misali, ƙasar Habasha ta buƙaci ’yan kasar da su rage amfani da motoci su koma amfani da motocin sufurin jama’a.

    A Afirka ta Kudu kuwa, manyan kamfanoni na ƙoƙarin ganin sun tanadi man da zai ishi muhimman ayyukansu.

    Ana sa ran buƙatar man fetur za ta ƙara tsananta, wanda hakan zai haifar da gasa tsakanin ƙasashen Afirka, sannan ya ƙara yawan ribar matatar Dangote ta ke samu.

    Aliko Dangote ya bayyana cewa a halin yanzu babban ƙalubale ba batun farashi ba ne, face yadda za a samu man.

    Ya kuma yi gargaɗin cewa wannan ƙaranci na mai na iya ɗaukar lokaci.

    Yayin da rikicin Gabas ta Tsakiya ke ci gaba da ƙamari, ana sa ran ƙarin ƙasashen Afirka za su karkata ga matatun cikin gida irin na Dangote domin tabbatar da tsaron makamashinsu.


    [ad_2]

    Source link

  • Tsayuwa Da Kafa Biyu Ya Fi Tsayuwa Da Kafa Daya

    [ad_1]

    Lokacin da na karbi ragamar aiki a matsayin Ministan Tsaro, na yi alawarin karfafa tsarin tsaron kasar. Na jaddada cewa, da farko, a matsayinmu na ‘yan Nijeriya dole ne mu dauki alhakin daukar nauyin da kalubalen da kasarmu ke fuskanta.

    Wannan ba kawai magana ba ce, illa kira ne zuwa aiki. Ina kuma tsaye daram wajen tabbatar da cewa mun fuskanci kalubalen tsaronmu kai tsaye ta hanyar amfani da falsafar “hadin kai da manufa daya”, wadda ke nufin mu yi aiki tare a matsayin kungiya guda, maimakon kowanne bangare ya yi aiki shi kadai kamar rundunar da ke zaman kanta.”

    • Sarkin Musulmi Ya Bukaci A Sauya Fasalin Tsarin Tsaro A Yaki Da Ta’addanci
    • Rawar Da Sashen Ayyukan Hidimomi Da Biyan Bukatu Ke Kara Takawa A Kasar Sin

    “Wannan ita ce falsafar da na bi a duk tsawon aikina na hidimta wa kasa a mukaman jagoranci da na ma’aikata a cikin aikin sojin Nijeriya. Wannan tunani ya ci gaba da kasancewa tare da ni har zuwa yau.

    Na kuma saba da bai wa jami’ai kwarin gwiwa da ke karkashina su fahimci muhimmancin wannan tunanin na dabarun tsaro, tare da aiwatar da shi a duk inda suka tsinci kansu a cikin aikinsu.

    Matsayin da nake rike da shi a yau yana da nufin karfafa tsarin tsaron kasar, bisa ga umarnin da Bola Ahmed Tinubu, Babban Kwamandan Askarawan Nijeriya, ya ba ni.

    Ina da cikakken kuduri da himma wajen mayar da fata da burin ‘yan Nijeriya su zama gaskiya ta hanyar kawo karshen ta’addanci a kasar.”

    Daidaitawar Soji Da Farar Hula

    “A lokacin da nake hidima a matsayin jami’in soja, daya daga cikin kalubalen da na fuskanta shi ne daidaita tunanin soja da al’adun farar hula. Akwai lokuta da dama da dole ne mutum ya saurari ra’ayin farar hula wajen magance matsalolin tsaro yayin da suke faruwa.

    A lokutan da na bi ra’ayin farar hula, na ga sakamakon da na samu a matsayin kwamanda ya burge ni matuka. Duk da na san cewa wasu daga cikin shawarar da na yanke ba su yi wa wasu daga cikin sojojina dadi ba, amma a matsayina na kwamanda, dole ne su amince da hukuncin da na yanke.

    A koyaushe ni nake daukar alhakin wadannan shawarwari. Idan na waiwaya baya yanzu, ina farin ciki da na yanke wadannan matakai domin sun tabbatar da cewa suna da amfani sosai.”

    Haramtaccen Yaki Da Ingantacce

    Yakin da bai da daidaito ba za a auna shi da yawan ‘yan ta’adda da aka kashe a daji kawai ba, amma da yawa akwai mutanen da aka ‘yanto daga shiga ta’addanci ko aka fito da su daga daji. Wannan yana nuna juriya a yaki, wato daga kirga gawarwaki zuwa halastaccen mulki.

    Yakin da ‘yan ta’adda ke yi yana da wahala kuma sau da yawa yana taba yunkurin dakaru ne kawai, wanda hakan zai kai ga jama’a su gaji da jinkirin samun sakamako. Amma halattaccen yaki yana mai da hankali kan gano tushen matsalolin da ke haddasa rikicin. Saboda haka, dabarun aikina sun ginu ne a kan hada wadannan hanyoyi biyu domin samun sakamako mai dorewa.

    Nadin da aka yi min daga baya a matsayin Babban Hafsan Tsaro (CDS) ya ba ni damar fadada gano abin da ake kira “Tsarin Borno” a cikin ayyukan soji.

    Ina tuna cewa a lokacin da nake CDS, a taron Kwamandojin Rundunar Hadin Gwiwa na CDS mai taken Inganta hadin Kai A Sansanin Soji”, na jaddada muhimmancin hadin kai wajen aiki, amfani da dabaru, da kuma hada al’umma baki daya wajen magance matsalolin tsaro.

    Misali, canza sunan aikin hadin gwiwar soja a Jihar Filato daga ‘Operation Safe Haben’ zuwa ‘Operation Enduring Peace’ wanda an yi shi ne domin samar da sabon hangen nesa ga sojoji da al’ummomin yankin kan muhimmancin yin aiki tare domin samar da zaman lafiya mai dorewa a Jihar Filato.

    Ina alfahari da cewa wannan dabarar tana aiki a jihar da kuma a sauran wuraren da sojojin Nijeriya ke gudanar da ayyukansu a fadin kasar.

    Dabarun Hada Kan Al’umma

    Akwai wani abu da na fahimta wanda nake son jaddadawa. Ba kasafai ake ganin sa a fili a cikin al’umma. A halin yanzu muna yaki ne da rikici mai sassa da dama. Kungiyoyin ta’addanci kamar Boko Haram, ISWAP, da Lakurawa da wasu kungiyoyin masu tashin hankali sun hada kai, sun ajiye sabanin da ke tsakaninsu domin su yi aiki tare su kai hare-hare. A wasu lokuta ma suna musayar bayanan sirri a tsakaninsu.

    Wannan gaskiya ce, kuma shi ya sa ake bukatar abin da ake kira “tsayuwa da kafafu biyu”, wato hada dabarun karfi na soja da kuma dabarun da ba na soja ba a cikin ayyukan tsaronmu, domin samar da daidaito da ake bukata wajen kayar da ta’addanci.

    Idan kungiyoyin ta’addanci na iya hada kai, me zai hana jama’ar kasa su hada kai da sojoji? Ba za mu iya kayar da ta’addanci da bindigogi da harsasai kawai ba. Wannan shi ne ainihin sakon da nake son isarwa a wannan rubutu.

    Kwarewata a matsayin Kwamandan Yanki da Babban Hafsan Tsaro har yanzu tana da tasiri sosai a tunanina. Na kalli matsalolin daga matsayi na jagoranci da na ma’aikata. Misali, yanke shawarar bin ra’ayin farar hula ta hanyar yin hadin kai ba tare da tangarda ba da gwamnatin Jihar Borno ya haifar da gagarumar nasara a yaki da ta’addancin Boko Haram.

    Wannan kuma yana karfafa hujjata ta cewa tsaro nauyi ne da kowa ke dauka. Wannan shi ne tsarin aiki a kasashen da suka ci gaba. Ban yarda cewa tsarinmu ya kamata ya bambanta ba.

    Wannan shi ne tsarin da Ma’aikatar Tsaro ke aiwatarwa. Ina farin cikin ganin cewa dukkan sassan sojojin Nijeriya sun daidaita da wannan dabarar. Haka kuma ma’aikatar tana yin hadin gwiwa da masu ruwa da tsaki a cikin al’umma, cibiyoyin addini da na gargajiya, kafofin yada labarai, kungiyoyin farar hula, da sassan kasuwanci na musamman domin shiga cikin dabarar “Hadin Kan Al’umma Gaba daya” wajen magance kalubalen tsaro na kasa.

    Mun tsara wani samfurin aika sako wanda ya dace da kowane matsayi na al’umma, har ma da mazauna karkara. Manufar ita ce samar da wayar da kai cewa idan muka hada kai, za mu iya kai da ta’addanci kasa idan muka dage a kan hakan.

    Akwai abubuwa da dama da ke haifar da rashin tsaro, amma akwai hanya daya da za ta iya dakatar da shi. Kuma wannan hanya ita ce lokacin da ’yan Nijeriya suka dauki nauyin hakan, ba tare da la’akari da al’adu ko kabila ba. Wannan nauyi ne na tilas domin juya yanayi a kan wadanda ba sa fatan alheri ga kasarmu.

    ‘Yan Kallo Da Ba Sa Kawo Dauki

    Kwanan nan na gabatar da jawabi na musamman a taron shekara-shekara na Kungiyar Tsoffin Daliban Kwalejin Tarayya ta Kaduna a matakin duniya. Na jaddada cewa:

    “Tarihi yana koya mana cewa babu wata kasa da za ta kasance mai tsaro idan ’yan kasarta suna zama masu kallo  da ba sa shiga tsakani.”

    Na ba da misali cewa manomi a Sakkwato, mai kasuwanci a Legas, da malami a Enugu suna zama layin farko na tsaro a kasa. Wannan yana kama da motsa muhawara kan tsaro daga sansanonin soja zuwa tituna, yana nuna cewa tsaro nauyi ne da ke wuyan kowa. Sojoji ba za su iya kasancewa a ko’ina ba. Saboda haka, ya zama dole ’yan Nijeriya su kasance masu shiga tsakani cikin tsarin tsaro, ba masu kallo marasa shiga tsakani ba.

    Wannan rubutu na zaba masa take mai sauki wato “Tsayuwa da kafafu biyu ya fi tsayuwa da kafa daya”. Wannan dabara ce da ta dace da sabon tunani da muke kokarin gabatarwa.

    Ina son sakon ya kai ga kowa, daga mai POS a Ibadan, mai dinki a Kaduna, har zuwa ma’aikacin gwamnati a Port Harcourt. Wannan wajibi ne, kuma yana dauke da alkawari zuwa ga ’yan Nijeriya na “tsayuwa da kafafu biyu” a yaki da ta’addanci.

    Na dauki wannan alkawari ne a ranar 21 ga Satumba, 1991, lokacin da aka ba ni Kwamishinan Shugaban Kasa don aiki a Rundunar Sojan Nijeriya a matsayin jami’in soja  na kasa. Dole ne mu hada kai don canza al’adar tsaro ta kasa.

    [ad_2]

    Source link

  • Jajircewar Cardoso Wajen Bunkasa Tattalin Arzikin Nijeriya

    [ad_1]

    Tattalin arzikin Nijeriya, kamar na yawancin sauran kasashe, yana fuskantar tangarda sakamakon sauye-sauyen da ke faruwa a kasuwannin duniya, wadanda suka samo asali daga rikice-rikicen siyasa da tattalin arziki da ba a hango su sosai ba a baya.

    Saboda haka, akwai wasu muhimman dalilai, Babban Bankin Nijeriya (CBN) ya dauki sabbin matakan manufofi domin tabbatar da amincewar jama’a ga tattalin arzikin kasa ta kasance mai karfi da dorewa.

    • Sarkin Musulmi Ya Bukaci A Sauya Fasalin Tsarin Tsaro A Yaki Da Ta’addanci
    • Shettima Ya Ziyarci Waɗanda Harin Bam Ya Shafa A Maiduguri

    Daga cikin wadannan manufofi akwai wadanda suka shafi harkokin kudi, wadanda ke da nufin karfafa ginshikan tattalin arziki tare da amfani da irin wadannan kayan aiki wajen karfafa ci gaban tattalin arziki da kuma tabbatar da daidaiton tsarin kudi gaba daya.

    Masana sun amince cewa wasu muhimman matakai da shugabancin babban bankin ya dauka, kamar rage kimar kudin ruwa na manufofin (MPR) zuwa kashi 26.5 cikin dari, za su taimaka matuka wajen kara zuba jari.

    Haka kuma CBN ya dauki matakan karfafa sashen bankuna ta hanyar dagewa kan sabon mafi karancin jarin da bankuna za su mallaka, tare da kaddamar da Dokar Canjin Kudin Waje ta Nijeriya domin tabbatar da gaskiya da rikon amana.

    Yana da muhimmanci a lura cewa Kwamitin Manufofin Kudi (MPC) ya rage kimar riba ta asali da maki 50 zuwa kashi 26.5 cikin dari daga kashi 27 cikin dari a farkon shekarar 2026, wanda ke nuna sauyi daga tsauraran matakan da ake dauka a baya.

    Haka kuma, manufar karfafa jarin sashen bankuna, wacce ta fara aiki daga Maris 2026, ta gabatar da sabbin ka’idojin mafi karancin jarin bankuna domin tabbatar da karfin sashen bankuna da kuma tallafa wa tattalin arziki da ake hasashen zai kai Dala tiriliyan 1.

    Kakakin babban bankin, Hakama Ali-Sidi, a cikin wata sanarwa, ta ba da bayani kan wannan aikin manufofi.

    “Tun daga 6 ga Maris, 2026, aikin karfafa jarin bankuna yana tafiya yadda ya kamata. Bankuna 30 sun cika sabbin ka’idojin mafi karancin jarin da suka shafi lasisin da aka ba su.

    “Gabadaya, bankuna 33 sun tara karin jarin kasuwanci ta hanyar sayar da hannun jari, sayar da hannun jari na farko (IPOs), da kuma sanya hannun jari na masu zaman kansu a matsayin wani bangare na wannan shiri.”

    Ta kara da cewa Babban Bankin Nijeriya zai ci gaba da gudanar da kulawar tsanaki tare da cibiyoyin da ake kula da su domin tabbatar da cikakkun bin ka’idojin tsaro da bukatun jarin bankuna.

    Kamar yadda aka ambata a baya, sashen canjin kudi na kasashen waje a cikin tattalin arzikin kudi ya ci gaba da zama jigon cece-kuce saboda muhimmancinsa a harkokin kasuwanci na yau da kullum, ciki har da shigo da kaya, fitar da kaya da sauran ayyuka da suka shafi zuba jari kai tsaye daga kasashen waje (FDI).

    An samu damuwa kan gaskiya da rikon amana wajen gudanar da wannan sashen da ayyukansa. Don magance wadannan damuwar, CBN ya kaddamar da Dokar Canjin Kudin Waje ta Nijeriya  domin karfafa gaskiya da inganci, yayin da take ci gaba da matsawa zuwa tsarin “mai saye mai so, mai sayarwa mai so” domin daidaita darajar naira.

    Duk da rage kimar riba, CBN na ci gaba da daukar mataki na taka tsantsan kan kudaden hannu, ta rike Babban Kason Ajiyar Kudi a kashi 45 cikin dari domin rage hauhawar farashin kayayyaki, yayin da yake karfafa mu’amaloli na dijital.

    Yana da muhimmanci a nuna cewa mayar da hankali kan ci gaban tattalin arziki da daidaito bai ragu ba. Babban manufar ita ce daidaita sarrafa hauhawar farashin kayayyaki tare da bukatar karfafa ayyukan tattalin arziki da habaka ajiyar kudaden waje, wanda ya kai matsayi mafi girma cikin shekaru 13, tare da karfafa daidaiton tsarin kudi.

    Masu sa ido kan tattalin arziki na da yakinin cewa rage kimar riba ta MPR zuwa kashi 26.5 cikin dari mataki ne mai kyau a hanya madaidaiciya, domin an tsara shi ne don saukaka samun bashi ga ‘yan kasuwa, inda ake sa ran farashin aro zai ragu sosai.

    Daya daga cikin manyan manufofin sabuwar Dokar Canjin Kudin Waje shi ne kara amincewar kasuwa da shigar kudade daga waje yayin da ake karfafa yawan kudaden canji a hannu. Bisa ga ka’idar bukata da wadata, gwamnatin Babban Bankin da Yemi Cardoso ke jagoranta tana ganin cewa bin ka’idojin kasuwar ‘yanci da barin karfin bukata da wadata su rarraba albarkatun canjin kudi zai kawar da matsalolin da ake samu a kasuwa sakamakon takunkumin da aka kirkira da hannu.

    Hauhawar farashin kayayyaki, musamman yadda yake shafar talakawan Nijeriya da yadda za a rage shi zuwa matakan da za a iya sarrafawa, ya kasance babban abin mayar da hankali a tattalin arzikin CBN. Don haka aka kafa Babban Kason Ajiyar Kudi (CRR) na kashi 45 cikin dari domin iyakance yawan kudaden da ke yawo a tattalin arziki. A baya ana ganin cewa yawan kudaden da ba a sarrafa su yadda ya kamata yana haifar da matsaloli wajen kokarin rage hauhawar farashin kayayyaki.

    A baya, Cardoso ya bayyana shirin gabatar da Tsarin Nufin Rage Hauhawar Farashin Kayayyaki, wanda ke nuna babban sauyi a tsarin manufofin kudi na Nijeriya. Wannan tsarin an tsara shi ne domin magance matsalar hauhawar farashin kayayyaki da ke ci gaba da tasiri sosai kan karfin sayen al’umma.

    Nufin rage hauhawar farashin kayayyaki, wanda shi ne ginshikin dabarunsa, wata hanya ce ta manufofin kudi inda babban banki ke sanya wani muhimmin matakin hauhawar farashi sannan ya daidaita kimar riba da sauran kayan aikin kudi don cimma wannan manufa.

    Wannan hanya tana samar da tsari mai kyau ta sarrafa hauhawar farashin kayayyaki, musamman a Nijeriya, inda hauhawar farashi ta dade tana zama babban cikas ga daidaiton tattalin arziki.

    Wannan yana bayyana a cikin matakin tsauraran manufofin kudi da yake dauka domin yakar hauhawar farashin kayayyaki da ke ci gaba da kasancewa a Nijeriya, wanda ya bayyana a cikin jerin kudurin da Kwamitin Manufofin Kudi (MPC) ya yanke.

    Har yanzu ana ci gaba da bin wannan hangen nesa, Babban Bankin na tilasta kayyade adadin kudaden da za a iya cirewa domin karfafa amfani da hanyoyin dijital da kuma dawo da ladabi wajen yawan kudaden da ke yawo a tattalin arziki da tasirin su na haifar da hauhawar farashin kayayyaki.

    [ad_2]

    Source link

  • ADC – Jafaru Sani Ya Mika Sakon Barka Da Sallah, Ya Soki Tsare El-Rufai

    [ad_1]

    Mataimakin Shugaban jamiyar ADC (Arewa maso Yamma) Mallam Jafaru Muhammed Sani, ya aika da sakon barka da Sallah ga Musulmai a fadin Nijeriya, yana kira da a ci gaba da zaman lafiya da juriya da fuskantar kalubalen kasa.

    A cikin sakon sa na barka da Sallah wanda ya zo bayan kammala Azumin Ramadan, Mallam Sani ya jaddada muhimmancin sadaukarwa, tausayi da hadin kai da wannan wata mai alfarma ya koyar.

    • An Gudanar Da Taron Tattaunawa Na Duniya Na “Sin A Yanayin Bazara” A Brazil
    • Manyan Darussan Kwaikwayo Daga Kyawawan Dabarun Ci Gaban Kasar Sin

    Ya yi addu’a ga ci gaba da zaman lafiya da kwanciyar hankali a Nijeriya, yana kira ga ‘yan kasa da su ci gaba da kasancewa masu fata yayin da ADC ke shirin tunkarar zabubbukan 2027.

    Baya ga sakon barka da Sallah, Sani ya yi karin suka kan abin da ya kira “tsarewar da ba ta dace ba” da aka yi wa Mallam Nasir Ahmad El-Rufai, tsohon Gwamnan Jihar Kaduna, kuma babban jigo a jam’iyyar ADC. Ya yi kira ga kotuna da hukumomin gwamnati da su tabbatar da adalci da bin doka, yana gargadin cewa tsare ‘yan adawa ba bisa ka’ida ba na iya lalata dimokuradiyya kuma ya nuna alamar karkata zuwa mulkin kama-karya.

    “ADC ta yi Allah wadai da wadannan ayyuka matuka,” in ji Sani, yana jaddada cewa dimokuradiyya tana bunkasa ne bisa girmama ‘yancin dan adam, bin doka da kuma jure ra’ayoyi daban-daban.

    Ya kuma karfafa ‘yan Nijeriya, musamman magoya bayan ADC, da su shiga cikin aikin rajistar mambobi da jam’iyyar ke gudanarwa, tare da tabbatar da cewa tarukan mazabu, kananan hukumomi da na jihohi za su gudana cikin lumana da gaskiya.

    “A yayin da muke bikin wannan Sallah, mu sabunta alkawarinmu ga adalci, dimokuradiyya da hadin kai,” in ji Sani. “Tare, za mu iya gina Jihar Kaduna da Nijeriya da za su nuna burin da fata na al’ummarta.”

    [ad_2]

    Source link