Category: Latest News

  • Yadda Za A Gyara Gashi

    [ad_1]

    Gyaran gashi na daya:

    Wannan hadin shi ake cewa Anty Liyash domin kuwa gashinki ba shi ba karairayewa kuma zai rika laushi kuma ya kara tsawo. Za a sa mu Ganyen Magarya, a daka ganyen magarya a rika wanke gashi da shi, yana kara wa gashi karfi da kuma hana shi zubewa.

    Gyaran gashi na biyu:

    A samu  Man Zogale, Man Kwakwa, Man Zaitun. Za a hade su guri guda ki rika shafawa a kanki,

    Gyaran gashi ns uku:

    Za a sa mu Man zogale, Ganyen magarya, Kanunfari kadan. Sai a hade su guri guda a rika shafawa a kai, yana sanya tsayin gashi ya kuma yi laushi.

    Gyaran gashi na hudu:

    Za a sa mu Rowan tumatir, Sabulun salo. Za ki matse ruwan tumatir, sai ki zuba sabulun salo a ciki ki bar shi ya samu tsayin mintoci idan ya jika, sai ki shafa a kanki da daddare, idan kin tashi bacci, da safe sai ki sa ruwan dumi ki wanke.

    Gyaran gashi na biyar:

    Wanna hadin shi ake cewa Anty Liyash shima domin kuwa gashinki bashi ba karairayewa kuma zai rika laushi kuma ya kara tsawo. Za a sa mu Man Zaitun shitta, Man Alayyadi, Man zaitun, Mankwakwa, Man albasa, Man Hulba, Man Ridi.

    Za ki hada Hulba da lalle guri guda ki tafasa, sai ki tace ki wanke kai da shi, sannan ki nemi sauren mayamayenki rika shafawa a kai, Za ki sha mamaki in sha Allah.

    Gyaran gashi na shida:

    Za a sa mu danyen kwai, Sabulun salo, Garin Shammar, A fasa kwai, amma ban da gwaiduwar farin kadai za ki yi amfani da shi, ki zuba sabulun salo a ciki, ki matse ki zuba garin shammar a ciki, sai ki wanke kai da shi. Yana da kyau sosai.

    [ad_2]

    Source link

  • Warware Batun Taiwan Lamari Ne Da Ya Shafi Kasar Sin Ita Kadai

    [ad_1]

    Kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin Lin Jian, ya ce Taiwan yanki ne na kasar Sin da ba za a iya balle shi ba, kuma batun Taiwan lamari ne na cikin gidan kasar Sin, kana warware batun Taiwan ya shafi kasar Sin ne ita kadai.

    Lin Jian, wanda ya bayyana hakan a jiya Jumma’a, yayin taron manema labarai na yau da kullum, lokacin da yake amsa tambaya dangane da tsokacin firaministar Japan da shugaban Amurka, game da muhimmancin wanzar da zaman lafiya da daidaito a zirin Taiwan, ya ce yayin da ake fatan cimma wannan buri, dole ne a bayyana matukar adawa da manufar ’yan a ware ta yunkurin neman ’yancin kan Taiwan. (Saminu Alhassan)

    [ad_2]

    Source link

  • Wang Yi Ya Yi Kira Da A Dauki Matakan Dakile Kara Tabarbarewar Yanayi A Gabas Ta Tsakiya

    [ad_1]

    Ministan harkokin wajen kasar Sin Wang Yi, ya ce daya daga abubuwan dake sahun gaba a yanzu, shi ne dakatar da yaduwar tashin hankali a yankin Gabas ta Tsakiya, da dakile shigar karin kasashe cikinsa.

    Wang, wanda memba ne a ofishin siyasa na kwamitin kolin JKS, ya yi tsokacin ne a jiya Jumma’a, yayin tattaunawa ta wayar tarho da mashawarci ga shugaban kasar Faransa kan harkokin siyasa Emmanuel Bonne, bisa gayyatar da mista Bonne din ya yi masa.

    Ya ce amfani da karfin tuwo ba zai warware matsalar da ake ciki ba, kana bai dace a kyale yakin rashin adalci ya ci gaba da wakana ba. Wang Yi ya kara da cewa, a yayin da ake fuskantar yanayi mai tsanani, ya dace Sin da Faransa a matsayinsu na membobin dindindin a kwamitin tsaron MDD, su karfafa tuntubar juna, da tsara matakai bisa matsayin koli, kana su goyi bayan kundin tsarin mulkin MDD da dokokin kasa da kasa, kuma su kare duniya daga tsunduma cikin yanayi na danniya da fin karfi.

    A nasa bangare kuwa, Bonne bayyana mahangarsa ya yi dangane da halin da ake ciki yanzu haka a Gabas ta Tsakiya, ciki har da abubuwan dake wakana a Iran da Lebanon. Ya ce Faransa a shirye take ta inganta tuntuba da hadin gwiwa tare da Sin, domin ingiza matakin cimma zaman lafiya da daidaito a Gabas ta Tsakiya. (Saminu Alhassan)

    [ad_2]

    Source link

  • Yakin Amurka/Israila Da Iran: MDD Ta Yi Gargadin Mutum Miliyan 45 Za Su Fuskanci Karanci Abinci

    [ad_1]

    Majalisar Dinkin Duniya ta yi gargadin cewa, ko shakka babu, miliyoyin mutane za su fuskanci matsananciyar yunwa, idan har yakin Amurka da Isra’ila a kan Iran ya ci gaba da kuma yadda Iran ta ke mayar da martani.

    “Idan rikicin Gabas ta Tsakiya ya ci gaba har zuwa watan Yuni, za a iya tura karin mutane miliyan 45 cikin matsananciyar yunwa ta hanyar hauhawar farashin kayayyaki,” in ji Carl Skau, Mataimakin Babban Daraktan Hukumar Abinci ta Majalisar Dinkin Duniya (WFP), wanda ya bayyana hakan a ranar Talatar da ta gabata.

    • Jajircewar Cardoso Wajen Bunkasa Tattalin Arzikin Nijeriya
    • Aikin Zamantar Da Tashoshin Jiragen Ruwan Nijeriya Zai Rage Wa Kasa Asasar Naira Tiriliyan Daya —Dantsoho

    “Wannan zai haifar  da wani mataki na karuwar yunwa a duniya fiye da kowane irin lokaci tarihi,” in ji Skau.

    Hare-haren da Amurka da Isra’ila suka kai kan Iran, wanda ya fara a ranar 28 ga watan Fabrairu, ya danne muhimman hanyoyin bayar da agajin jin kai tare da jinkirta jigilar kayayyaki na ceton rai zuwa wasu munanan rikice-rikice a duniya.

    Skau ya ce, farashin jigilar kayayyaki ya karu da kashi 18 cikin dari tun bayan da aka fara yakin, sannan kuma dole ne a samar da wasu hanyoyin.

    Ya kara da cewa, karin kudin na zuwa ne sama da raguwar kashe kudade da WFP ke yi, yayin da masu bayar da taimako suka fi maida hankali a kan tsaro.

    A Gaza, mazauna yankin na gaggawar tara kayayyaki a yayin da ake rufe kan iyaka da kuma yakin Iran da ke kara samar da karancin kayan masarufi, yayin da karancin kayayyaki ke kara ta’azzara a yankin da aka yi wa kawanya, yayin da Isra’ila ke ci gaba da yakin kisan kare dangi a can.

    Isra’ila za ta sake bude wani bangare na mashigar Rafah ta Gaza da Masar a ranar Laraba, wanda ya kawo karshen rufewar makwanni biyu da ta yi, wanda ya dada zurfafa rikicin jin kai a yankin da ya lalace.

    Isra’ila ta rufe mashigar a wannan rana, sannan kuma Amurka ta kai hare-hare kan Iran, saboda dalilai na tsaro.

    Daraktan yanki na Hukumar Lafiya ta Duniya na Gabashin Bahar Rum, ya yi gargadin a makon da ya gabata cewa, kusan manyan motoci 200 ne ke shiga Gaza a kowace rana, wanda ya yi kasa da kiyasin da ake bukata na yau da kullum na 600.

    A halin da ake ciki, sama da mutane miliyan 21 a Sudan, kusan rabin al’ummar kasar na fuskantar matsananciyar yunwa. An tabbatar da cewa, ana fama da yunwa a yankunan da aka kwashe watanni ana gwabzawa, ya sanya ba za a iya kai wa ga ma’aikatan agaji ba.

    A watan Janairu, Majalisar Dinkin Duniya ta yi gargadin cewa, agajin da ake bai wa Sudan zai iya karewa cikin ‘yan watanni, matukar ba a yi alkawarin karin daruruwan miliyoyin daloli ba.

    Tsawon shekara uku da aka kwashe ana gwabza kazamin yaki tsakanin gwamnatin mulkin soja da dakarun sa kai na gaggawa, ya yi sanadiyyar kisan dubunnan mutane tare da raba kimanin mutum miliyan 14 da muhallansu.


    [ad_2]

    Source link

  • 2027: An matsa min kan yin takarar Sanata — Gwamna Sule

    [ad_1]



    Gwamnan Jihar Nasarawa, Abdullahi Sule, ya ce zai iya tsayawa takarar kujerar Sanata a shekarar 2027.

    Ya bayyana hakan ne yayin wata ziyara da mambobin majalisar zartarwa ta jihar suka kai masa, ƙarƙashin jagorancin mataimakin gwamna, Dakta Emmanuel Akabe, a gidansa da ke Gudi, a Ƙaramar Hukumar Akwanga.

    Gwamnan ya ce shugabanni da masu ruwa da tsaki da dama suna matsa masa lamba ya tsaya takarar kujerar Sanata mai wakiltar Nasarawa ta Arewa.

    Saboda wannan matsin lamba, ya ce yana duba yiwuwar tsayawa takarar.

    “Duba da irin matsin da shugabanninmu ke yi, ba na son su ji kamar ban mutunta su ba. Zan iya musu alƙawarin zan tsaya takara idan lokaci ya yi,” in ji shi.

    Sule ya ce tun da farko yana da niyyar mara wa wani baya, amma daga baya ya sauya shawara bayan mutumin ya haɗa kai da wasu wajen roƙonsa da ya tsaya takara.

    Ya ƙara da cewa har yanzu yana tuntuɓar masu ruwa da tsaki, ciki har da sarakunan gargajiya da manyan ’yan siyasa daga yankin Nasarawa ta Arewa, kafin ya yanke hukunci na ƙarshe.

    Gwamna Sule na wa’adinsa na biyu a mulki, kuma zai sauka bayan kammala wa’adin.

    A jawabinsa, mataimakin gwamnan ya sake jaddada goyon bayan majalisar zartarwar jihar ga gwamnan, yana mai cewa za su ci gaba da mara masa baya har zuwa ƙarshen wa’adinsa.


    [ad_2]

    Source link

  • Wang Huning Ya Gana Da Wani Farfesan Jami’ar Harvard

    [ad_1]

    Shugaban majalisar bada shawarwari kan harkokin siyasar kasar Sin wato CPPCC a takaice, Wang Huning, ya gana da farfesan jami’ar Harvard Graham Allison, a jiya Jumma’a a nan birnin Beijing.

    Yayin zantawarsu, Wang ya ce, Sin za ta ci gaba da fuskantar yawaitar sauye-sauyen yanayin kasa da kasa cike da tabbaci game da ci gaban kanta, a daidai gabar da a bana ta shiga shekarar farko ta aiwatar da shirin raya kasa na shekaru biyar karo na 15.

    Wang, ya jaddada cewa batun Taiwan na kan gaba, cikin manyan moriyar kasar Sin. Kuma kamata ya yi Sin da Amurka su inganta tattaunawa da tuntuba, su shawo kan sabaninsu yadda ya kamata, su fadada hadin gwiwa na hakika, kuma su samar da hanya ingantacciya ta tafiya tare, da ingiza samar da tabbaci da kyakkyawan karsashi cikin duniya.

    A nasa bangare, farfesa Allison cewa ya yi a halin da ake ciki, an riga an yi matukar illata yanayin zama lafiya da odar duniya, kuma yana da matukar muhimmanci Amurka da Sin su zakulo hanya madaidaiciya ta yin tafiya tare.

    Allison, ya kara da cewa, fatan shi ne Amurka da Sin za su shawo kan batutuwa yadda ya kamata, ciki har da batun Taiwan, kana su tabbatar da samar da daidaitaccen ci gaban dangantakarsu, kasancewar hakan ya yi daidai da muradun dukkanin kasashen duniya. (Saminu Alhassan)

    [ad_2]

    Source link

  • Kano: Cikakken Dalilin Soke Ma’aikatar Ilimi Mai Zurfi

    [ad_1]

    Gwamnatin Jihar Kano ta soke ma’aikatar ilimi mai zurfi wadda ke karkashin kulawar mataimakin Gwamna Aminu Abdulsalam Gwarzo mutumin da ya ke fuskantar matsaloli masu yawa, ta hada da daya da ma’aikatar ilimi ta Jihar a matsayin tsarin ta na kawo gyara kan lamarin ilimi a Jihar.

    Gwamna Abba Yusuf shi ne ya amince da yin hakan, a matsayin wani mataki na kawo gyara kan lamarin ilimi da kuma rage yawan kudaden na yadda ake tafiyar da Shugabanci a Jihar.

    • Abincin Sallah
    • Kuncin Rayuwa: Jam’iyyun Adawa Da Kungiyar Kwadago Sun Caccaki Tinubu

    Wannan ci gaban an same shi ne ranar Lahadin da ta gabata daga bakin mai ba gwamnan shawara a kan harkokin yada labarai, Sunusi Bature.

    Ta hakan ne ita ma’aikatar ilimi mai zurfi wadda shi mataimakin Gwamnan ke kulawa da ita, ta daina zama ma’aikata mai zama mai irin wancan aikin, da yanzu ma’ikatar ilimi ta kasance mai yin aikin da take yi.

    A sabon tsarin kamar yadda gwamnatin ta bayyana, za’ a kirkiro wani sabon sashe ne na musamman da ya shahara kan lamurran ilimi mai zurfi,a cikin ma’aikatar ilimi, ya rika da harkokin ilimi mai zurfi a illahirin Jihar.

    Kamar dai yadda bayanin ya nuna, Babban Sakatare ne zai jagoranci da kulawa da shi sabon sashen, da taimakon ma’aikatan da suke da ruwa da tsakin kan lamarin Mkarantun ilimi mai zurfi.

    Hakanan kuma sauran Hukumomin da suke karkashin ma’aikatar ilimi mai zurfi, da suka hada da Hukumar bada taimakon kudade na yin karatu, yanzu za ta koma  a, karkahin ma’aikatar ilimi.

    Hakanan ma,duk Jami’oin Jihar da manyan Makarantu yanzu sabon sashen ne da aka hada da ma’aikatar ilimi zai rika kulawa da su.

    Gwamnatin ta ce gyaran da aka yi ya na karkashin tsarin da ake son yi domin kawo gyara na zummar gyara bangaren ilimi, ta hanyar sake kawo gyara akan ayyukan da suka kasance daya, da bunkasa tsare- tsare ga dukkan bangarorin ilimi, da kuma tabbatar da ana tafiyar da su tsare- tsaren kamar yadda ya dace.

    Gwamna Yusuf ya ce matakin an shirya shi ne domin a rage kudaden yadda ake tafiyar da ayyukan gwamnati da kuma inganta tsarin tafiyar da gaskiya, da kuma bunkasa a gaba daya inganci wajen tafiyar da tsarin ilimi a Jihar.

    Ya tabbatar da tsarin tafiyar da gwamnatin sa lamarin zai kasance ne wajen maida hankali wajen aiuwatar da su tsare- tsaren wadanda za su farfado da martabar ilimi, domin hakan zaman tamkar wata fitila ce da za ta rika haskewa matasa abubuwan da suka dace su yi domin bunkasar Jihar baki daya.

    Bugu da kari kuma, ya umarci Ofisoshin Sakataren gwamnatin Jihar da na Shugaban ma’aikata da cewar su tabbatar da duk an yi abubuwan da suka dace ayi da kuma tafiyar sabbin sassan wajen sake masu yadda za su kara inganta ayyukansu.

    [ad_2]

    Source link

  • Shugaban Al’ummar Turkmenistan Ya Ce Idan Sin Ta Yi Kyau Duniya Za Ta Kara Kyau

    [ad_1]

    Shugaban al’ummar Turkmenistan, kuma shugaban kwamitin jama’ar kasa na Halk Maslahaty na kasar, Gurbanguly Berdimuhamedov, ya ce dangantakar dake tsakanin kasashen Turkmenistan da Sin, ta riga ta kai wani babban matsayi na hadin gwiwa.

    Ya bayyana hakan ne a yayin da yake zantawa da wakilin babban rukunin gidajen rediyo da talibijin na kasar Sin ko CMG a kwanan nan, inda ya ce shekarar bana, shekara ce ta cika shekaru 34 da kafuwar huldar diflomasiyya a tsakanin kasashen biyu. Ya kara da cewa dangantakar dake tsakanin kasashen Turkmenistan da Sin na da kyakkyawar makoma a nan gaba.

    Hakazalika, ya jinjinawa nasarar da aka cimma yayin manyan taruka biyu na kasar Sin na shekarar nan ta 2026, wato taron majalisar wakilan jama’ar kasar Sin da na majalisar ba da shawarwari kan harkokin siyasa na jama’ar kasar. Kana ya yaba wa shirin shekaru biyar-biyar na bunkasa tattalin arziki da zamantakewar kasar Sin na 15, wanda ya ce zai bude sabon babi na samun ci gaba mai inganci a kasar.

    Baya ga haka, shugaba Berdimuhamedov ya bayyana cewa, kasar Sin ginshiki ne na tabbatar da tsaro, da samun dauwamamman ci gaban duniya. Ya ce, “Idan Sin ta yi kyau, duniya za ta kara kyau.” (Mai fassara Bilkisu Xin)

    [ad_2]

    Source link

  • Yadda Shigo Da Shinkafa Daga Kasashen Waje Ya Share Masana’antu 90 A Nijeriya

    [ad_1]

    Bangaren shinkafar Nijeriya, wanda ya jawo jari mai yawa na cikin gida da na waje, yana fuskantar gagarumin rugujewa saboda kara shigo da shinkafa da ayyukan fasa-kauri da rashin daidaiton farashi.

    Darakta janar na kungiyar masu sarrafa shinkafa ta Nijeriya, Dakta Andy Ekwelem, ya ce, “Daga cikin masana’antun shinkafa sama da 150 a fadin kasar nan, kusan 90 sun dakatar da ayyukansu. Masana’antun da suka rage a halin yanzu suna aiki tsakanin kashi 30 zuwa 70 na karfin da ya rage musu.”

    • Wang Yi Ya Zanta Ta Wayar Tarho Da Ministar Harkokin Wajen Birtaniya 
    • Aikin Zamantar Da Tashoshin Jiragen Ruwan Nijeriya Zai Rage Wa Kasa Asasar Naira Tiriliyan Daya —Dantsoho

    Rahotanni sun bayyana cewa manyan kalubalen da manoma da masu sarrafa kayan noma ke fuskanta, sun hada da yawan shigo da shinkafa da kuma fasa-kaurin kayan zuwa cikin kasar wanda ya haifar da rugujewar farashi.

    Kididdiga daga wasu hanyoyi daban-daban sun nuna cewa Nijeriya ta shigo da shinkafa tsakanin tan miliyan 2.4 da 3.2 a shekarar 2025, mafi yawanci a lokacin rangwamen haraji na wucin gadi da aka yi don rage farashin abinci.

    “An kiyasta shigowar shinkafa kasuwa a tsakanin shekarar 2024 zuwa 2025, tan miliyan 2.4, an samu karuwar kashi 60 cikin dari idan aka kwatanta da kiyasin watan Afrilu 2024 na tan miliyan 1.5. Wannan ba ya hada da yawan shinkafar da aka shigo da ita ba bisa ka’ida ba a cikin kasa,” a cewar bayanai daga Bestance, kamfani mai ba da shawara a fannin aikin gona.

    Duk da raguwar samar da shinkafar gida, shigowar shinkafar wanda aka kiyasta ta kusan naira tiriliyan 1, sun haifar da yawan kaya fiye da bukata tun shekarar da ta gabata, wanda ya sanya Hukumar Tsara Manufofin Kasuwancin Noma ta Kasa (NAPM) ta yi kira ga gwamnati da ta dakatar da shigowa da shinkafa don ceton manoma na cikin gida.

    Daraktan gudanarwa na kamfanin ‘Infinera Agribusiness Ltd’, Kolawale Oye a shafinsa na LinkedIn, ya ce ko a cikin bayanan ma’aikatar abinci ta kasa, Nijeriya ta samu karin shinkafa kusan tan miliyan 1.1 zuwa Disamba 2025. Amma wannan karin ba nasara ce ta gonaki da injinan gida ba, an samu shi ne ta hanyar shigowa da kaya.”

    Banciken shekara ta 2025 daga Hukumar Kididdiga ta Kasa (NBS) ya nuna karuwar kudin shigo da abinci a Nijeriya, wanda ya tashi daga naira tiriliyan 3.83 a shekarar 2023 lokacin da Shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu ya karbi mulki zuwa naira tiriliyan 7.65 a shekarar 2025.

    Yawancin manoma da suka yi magana kan lamarin, sun ambaci sassaucin gwamnatin tarayya kan harajin shigo da shinkafa da wasu kayayyaki (Yuli 2024 zuwa Disamba 2025) a matsayin babban abu da ya janyo yawan shigo da kaya sosai.

    Duk da haka, yayin taron hadin gwiwa na masu ruwa da tsaki a Abuja, ministan noma da samar da abinci, Sanata Abubakar Kyari, ya ce an shigo da tan 250,000 kawai a wannan lokacin. Ya ce wannan adadin ba shi da girma ga bukatar cikin gida ta kasar, wanda ke kaiwa kusan tan miliyan 11.

    Amma yayin da yake magana a wani taro ranar Litinin da ta gabata tare da kungiyar masu sarrafa shinkafa ta Nijeriya (RIPAN) a Abuja, karamin ministan masana’antu, Sanata John Owan Enoh, ya yarda cewa akwai matsala.

    “Lokacin da aka sayar da shinkafa da aka shigo da ita ko aka safarar ta ba bisa ka’ida ba a farashin da ya yi kasa sosai da na shinkafa da ake sarrafa a gida, hakan yana rage ingancin samar da kayayyakin ciki da kuma hana jari a wannan fanni.

    “Gwamnati ba za ta yi ja da baya ba wajen daukar matakan manufofi da suka dace don kare masana’antar cikin gida da kuma ci gaba da sarkar shinkafar Nijeriya,” in ji shi.

    Sanata Enoh ya amince cewa karuwar yawan shinkafar kasashen waje mai arha da ke shiga kasuwar Nijeriya na haifar da barazana mai tsanani ga masana’antu na cikin gida da kuma nasarorin da gwamnatocin baya suka cimma.

    Shigo da shinkafa ta kan iyakokin kasa an haramta shi a lokacin mulkin tsohon shugaba kasa, Muhammadu Buhari, wani ci gaba da ya kara yawan samar da shinkafar gida wanda ya sa kamfanonin sarrafawa su kashe miliyoyin daloli a baya.

    Saboda wannan manufofi, samar da shinkafar ya tashi daga tan miliyan 2.8 a shekarar 2010 zuwa tan miliyan 8 a shekarar 2021, wadda ta kasance shekarar da aka samu shinkafa mai yawa, wanda shirin ‘Anchor Borrowers’ ya jagoranta, tare da fitar da shinkafar da aka nika tan miliyan 5.3 a kowace shekara.

    Rahotanni sun bayyana cewa sakamakon ya haifar da raguwar gibin bukata wanda ya samar da shakku tare da samun karuwar tan 1.5 zuwa tan 3.5 a kowace hektar.

    Yawancin jihohi, wadanda suka samu shinkafa mai yawa, sun hada da Kebbi (tan miliyan 3.5), Jigawa (tan miliyan 2.1), Kano (tan miliyan 1.6), da Ebonyi (tan miliyan 1.5) bisa ga bayanai daga Babban Bankin Nijeriya a shekarar 2022.

    Tun daga shekarar 2017, an gina kimanin masana’antun noman shinkafa na matsakaici da manya guda 68 a fadin kasar, musamman a arewaci, tare da dubunnan masana’antun kanana da ke Kano, Kebbi, Kaduna, Katsina, Jigawa, Taraba, Benuwai, Nasarawa, Anambra, Ebonyi, da wasu wurare a sauran jihohi.

    Amma sanata Owan Enoh ya ce, “An tattauna da yawa daga cikin wadannan batutuwan sau da dama a cikin shekaru. Manufar wannan gwamnati ba magana ba ce, amma aiwatarwa ta gaskiya wanda ke kawo sakamako ga ‘yan Nijeriya.”

    Ministan ya jaddada cewa shinkafa ta ci gaba da kasancewa daya daga cikin manyan abincin yau da kullum na Nijeriya kuma tana da muhimmancin ga zaman lafiya kasar.

    Ana kiyasin cewa shinkafa a Nijeriya a kilo 32–33 ga kowane mutum a shekara, wanda ya kai tan miliyan 6.7 zuwa 7 na shinkafa mai tsabta a shekara.

    “Wani karfi a fannin shinkafa yana da muhimmanci ga samar da abinci, samar da aikin yi da kuma habaka ci gaban tattalin arziki,” in ji ministan.

    Shugaban RIPAN, Dakta Andy Ekwelem, ya ce shinkafar da ke shigowa Nijeriya ba bisa ka’ida ba ta hanyar iyakokin kasar sabada kaurace wa haraji da kudaden shigar hukuma, wanda ke sa tana arha fiye da shinkafar da aka sarrafa a ciki gida, kuma yana sanya masu samar da shinkafa na cikin gida cikin rashin daidaito mai tsanani.

    “Shinkafar da aka yi fasa-kauri tana shiga kasuwar Nijeriya a farashin da masu sarrafata a gida ba za su iya gogayya da su ba,” in ji Dakta Ekwelem. “Wannan gasa mara adalci ta yi mummunan tasiri ga masana’antar shinkafa a Nijeriya.”

    Ya ce wahalar da masu sarrafa shinkafa a fadin kasar ta kasance mai tsanani.

    Alhaji Usman Garba Badawa, wani mai masana’anta matsakaicin girma a Kano, ya shaida cewa kasuwancin sarrafa shinkafa yana kan samun matsala sosai saboda alamomi sun nuna cewa ba za su iya yin gogayya da kasuwa ba, saboda shinkafa ta waje ana sayar da ita da arha ko kuma daidai da farashin shinkafar gida amma za ta kasance zabi na farko ga masu saye ko da yaushe.

    Ya bayyana cewa, a halin yanzu, shinkafa daga kasashen waje yawanci tana samun damar shiga kasuwar Kano cikin sauki daga kan iyakar Babura a Jihar Jigawa da sauran iyakoki daga Jihar Katsina.

    “Ci gaban da shigowar shinkafar kasashen waje hakika alamar illa ce a gare mu, manufofin rufe iyakokin da gwamnatin tarayya ta sanya sun haifar da kafa masana’antu sama da 200 na shinkafa a Jihar Kano kadai, kuma an kirkiri dubban ayyukan yi a bangaren shinkafa. Duk da haka, da abin da muke gani a yanzu, akwai barazanar da ka iya tilasta rufe wadannan masana’antu gaba daya kuma ya sanya duk wadannan mutanen su rasa ayyukansu. Yanzu, a wannan lokaci mai muhimmanci na tattalin arziki, wannan lamari zai iya cutar da jama’ar Nijeriya,” in ji shi.

    Dakta Ekwelem ya kara bayyana cewa manoma da masu sarrafa kayan gona suna fuskantar hauhawar farashin samar da kayayyaki, kalubalen tsaro da rashin isasshen ababen more rayuwa.

    “Yawancin manoma ana tilasta musu sayar da amfanin gonarsu a asara saboda matsin lamba da shigawa da shinkafa ta haramtacciyar hanya mai rahusa. Wannan yanayi yana sanya aikin masu sarrafa shinkafa a cikin kasar ya zama mai wuya sosai a ci gaba da kasancewa mai dorewa.”

    Ya kuma ce raguwar farashin shinkafa da aka gani kwanan nan a wasu kasuwanni bai kamata a dauka kamar karin samar da shinkafa a cikin gida ba, wani abu da ministan noma, Sanata Kyari, bai yarda da shi ba, yana jayayya cewa karin samarwa a cikin gida ne saboda faduwar farashi.

    “Raguwar farashin ta kasance sakamakon ayyukan kungiyoyin masu fasa-kaurin kayayyaki da suke shigo da shinkafa ta hanyoyi na haram a iyakokin Nijeriya,” in ji shi.

    A Kano, wakilinmu ya ba da rahoto cewa yawancin masana’antar shinkafa sun dakatar da samarwa ko suna aiki da rabin karfinsu.

    Wani majiya a daya daga cikin manyan masana’antar shinkafa ta ce sun dakatar da aiki kusan watanni uku, ta kara da cewa wasu manyan masana’antar shinkafa da dama a jihar sun dakatar da samarwa, yayin da wasu kadan ke gudanar da ayyuka kadan don watan Ramadan.

    A Jihar Benuwai, masu sarrafa shinkafa da yawa sun rufe ayyukansu tun bara, bayan faduwar farashi, in ji wani rahoto.

    Wani dan kasuwa, Ichor Michael Tersoo, wanda ke gudanar da masana’antar shinkafa ta Wadata a Makurdi, ya shaida wa wakilinmu a Makurdi a ranar Alhamis cewa ya dakatar da kasuwancinsa saboda yana fuskantar asara.

    “Na rufe kasuwancina saboda wadannan kalubalen. Ban iya kimanta kudin da na yi asara ba, ko da yake farashin shinkafar gandun daji ya fara tashi bayan durkushewa a bara.

    “Yanzu ana sayar da shinkafa a tsakanin naira 50,000 da naira 55,000 idan aka kwatanta da naira 35,000 da naira 40,000 da aka saba sayarwa a shekarun ba. Amma har yanzu ban shirya yin sabon alkawari ba. Bugu da kari, hasashen wannan shekarar ya nuna cewa za a fara ruwan sama da wuri sannan kuma zai tsaya da wuri, wanda haka zai shafi noman shinkafa,” in ji shi.

    Adayi Joseph Unogwu, wanda ke da sarrafa shinkafa a Wurukum cikin birnin Makurdi, ya yi kuka kan faduwar farashin shinkafa, yana cewa ba zai iya amfani da cikakken karfinsa na sarrafa shinkafa. Duk da haka, Unogwu ya rufe masana’antarsa ta Makurdi.

    Ya yi kukan cewa, “Masu sarrafa shinkafa a Jihar Benuwai yana daidai da na fadin kasar. Yawancinmu ba ma aiki kamar yadda muke so, muna sarrafa shinkafa kasa da ikonmu, saboda farashin shinkafa na sauka. Wasu ma ba sa iya yin aiki gaba daya. Me ya sa? Saboda shigo da kaya ya rushe farashin shinkafar da aka sarrafa a gida.

    “Babu wasu abubuwan karfafawa gwiwa kan farashin shinkafa a yanzu, wanda hakan ba shi da dorewa. Saboda shigowa da shinkafa, hakan ya sa farashin shinkafa ya kasance kasa da abin da masu iya sarrafawa da masu sayarwa ke caji. Yanzu muna da masana’antar sarrafa shinkafa da yawa wadanda ba sa aiki. Gaskiya, wasu mutane suna sayar da masana’antar shinkafarsu yayin da wasu ke ci gaba da sarrafa amma ba yadda suka so ba.

    “An yi watsi da gonaki da dama, kuma manoma sun rage yawan amfaninsu saboda tsadar kayan aikin gona da kuma karancin farashin shinkafa. Don haka abin da za mu gani a cikin watanni masu zuwa shi ne rufewar masana’antu ko sarrafa kayan gona kasa da karfi da suke da shi.”

    Kazalika, Gwamna Hyacinth Alia, ya bayyana shirin farfado da wannan bangare.

    “A yau (Talata), na duba kayan aiki da aka samo domin farfado da masana’antun shinkafa na Jihar Benuwai a Wadata, Makurdi, wani wuri da aka yi watsi da shi tsawon shekaru amma yanzu an shirya zai ci gaba da sarrafa shinkafa.

    “Wannan shiri zai kirkiri damammaki ga mata, ya karfafa kananan kasuwanci, kuma ya habaka samar da shinkafa na cikin gida a Benuwai,” in ji gwamnan a shafinsa na Facebook.

    Rahotanni sun bayyana cewa dukkan manyan kamfanoni a Jihar Taraba sun rufe ayyukansu sai wasu ‘yan kanana kamfanonin sarrafa shinkafa.

    An ruwaito cewa a garin Jalingo, kamfanin sarrafa shinkafa na Gamzaki da ke yankin CBN a Jalingo, da kamfanin sarrafa shinkafa na Nabinu da ke Mile 6 da kamfanin sarrafa shinkafa na Rahama da Aminci da ke Yamusala da yankin Primary Board, duk a Jalingo, babban birnin Jihar Taraba, an rufe su saboda rashin masu saye.

    Mamallakin kamfanin sarrafa shinkafa na Gamzaki a Jalingo, Alhaji Aliyu Sarkin Noma, ya ce ya rufe kamfaninsa Gamzaki a Jalingo ne saboda rashin kwastomomi.

    Ya ce bayan an dage haramcin shigo da shinkafa ta kasashen waje, kamfanonin sarrafa shinkafa na cikin gida sun fara rasa abokan ciniki.

    Ya ce tsadar farashin dizal da na wutar lantarki da tsadar kaya sun sa kamfanoni sarrafa shinkafa rashi samun riba. Ya kara da cewa ya fara rage yawan ma’aikata a kamfaninsa kuma a karshe dole ya rufe kamfanin lokacin da babu kasuwa ga shinkafar da ake sarrafawa a gida.

    Sai dai masu sarrafa shinkafan sun bayyana cewa sake bude iyakokin Nijeriya ya kara ruruta wutar lamari.

    “Mutanen da ba sa noma sun yi imanin cewa bude iyakoki yana taimaka mana, amma yana cutar da samar da kayayyakin da ake sarrafawa gida fiye da amfaninsa. Shinkafa ta gida tana da karin sinadarai da dandano fiye da shinkafar da aka shigo da ita, amma da zarar shinkafar kasashen waje ta shiga kasuwa, sai a rage amfani da namu ta gida,” wani mai sarrafa shinkafa ya shaida hakan.

    Masu sarrafa shinkafa sun ce masana’antun shinkafa ba za su iya tsayuwa da kafarsu ba idan har gwamnati ba ta dauki matakan da ya dace ba. Yayin da manoma ke neman samun kayan aiki a araha, masu sarrafa shinkafa suna neman manufofi da za su kare samar da shinkafar gida.

    A cewar Yazid Adamu, “Mafi kyawun abin da gwamnati ya kamata ta yi shi ne, ta rage farashin kayan aikin gona. Idan aikin gona yana bukatar babban jari kuma farashin yana ci gaba da faduwa a kasuwa, mutane za su guji noma. Kuma bari in gaya muku, abin da gwamnati ba ta sani ba shi ne, lokaci zai zo da ake bukatar shinkafa ta yi yawa amma kuma samuwarta zai yi kasa sosai saboda babu wanda ke yin noma don asara.”

    A dukkan fadin kasar, rahotanni sun bayyana cewa manoma da yawa ba su zuba jari a noman rani a wannan kakar ba saboda farashin kayayyakin aiki sun tashi kuma farashin shinkafar ya yi kara.

    A Jihar Kano, manoman shinkafa sun ce tsadar kayan aikin gona da karancin tallafi daga hannun hukumomi, noma shinkafa ya zama abin gudu, saboda haka ma manoma da dama daga cikinsu suna tunanin barin aikin.

    Daya daga cikin manoman shinkafa, Alhaji Abba Ibraheem Kallah, ya ce ya yi asara mai yawa a lokacin damina ta bana bayan ya kashe makudan kudde wajen noman shinkafa. Ya kara da cewa tsadar kayan aikin noma da kuma faduwar farashin shinkafar gida a kasuwa sun sanya da dama daga cikinsu bashi ya masu katutu. Ya ce wannan shi ne dalilin da ya sa da yawa daga cikin manoma ba su damuwa da yi noman rani.

    Shugaban jiha na kungiyar manoman shinkafa ta Nijeriya (RIFAN), Alhaji Abubakar Haruna Aliyu, ya bayyana cewa fiye da kashi 50 na manoman shinkafa suna barin wannan fanni.

    A cewarsa, tun bayan dakatar da shirin bai wa manoma rance a jihar, manoman shinkafa sun kasance suna daukar nauyin kansu. Ya bayyana wannan lamari a matsayin abin damuwa sosai, idan aka yi la’akari da rawar da manoman shinkafa na asali suka taka wajen tallafa wa kasar a tsawon shekaru.

    “Muna da kwarin gwiwa cewa da dan taimako kadan, ‘yan kungiyarmu suna son bayar da gudunmawa ga masar da abinci a kasar nan, amma yadda abubuwa ke tafiya yanzu, na tabbata ba za mu iya shawo kansu su yi abin da ya dace ba. Duk matakan taimako sun tsaya. Manoma suna son yin haka, amma tsarin ba ya goyan bayan hakan. Dukkan batun ya canza zuwa wani abu daban. Iyakokin kasar nan da aka bude su sannan kuma aka ta shigo da shinka, yayin da samar da shinkafar gida yake mutuwa a hankali,” in ji shi.

    A Nasarawa, manoman da suka karbi rance suna jin radadin asar da suka tafka wajen kokarin biyan bashin da kudin da suka samu daga sauran amfanin gona.

    Manoma wadanda suka saba yin aikin gona a lokacin rani a gefen koguna da kowace fili da ake da ita kusa da ruwa sun bar noma irin wadannan gonaki.

    Wakilinmu a Kano shi ma ya ruwaito irin wannan yanayi a tsibirin ban ruwa na Kadawa a karamar hukumar Kura, wani wuri da yake cike da ayyukan ban ruwa.

    Wani kwararren masanin tattalin arzikin noma, Mamun Malam, ya dora laifin rikicin kan rashin tsari mai dorewa na manufofin noma na gwamnatin tarayya.

    Ya ce wadata kasa da abinci zai sami tasiri sosai daga shigo da abinci.

    A cewar hasashen Malam, samar da shinkafar paddy a Nijeriya zai ragu daga tan miliyan 10 a shekarar 2018 zuwa tan miliyan 4 a shekarar 2026. Ya ce saboda ambaliyar ruwa, rashin tsaro, da rashin kwarin gwiwa ga manoma, zai ragu ma fiye da haka.

    Ya kara da cewa tasirin zai kara shafar sarrafawa kuma zai kara matsa lamba kan naira, saboda shigo da kaya ba kyauta ba ne.

    “Masana’antar sarrafa shinkafar na rufe ayyukansu saboda wani lamari na daban da kuma rashin aiwatar da matakan noma da manufofinmu. Amma ba zai tsaya kawai ga rufe masana’antar sarrafa shinkafa ba kadai, har ma da samar da shinkafar hatsi zai ragu a wannan shekara, ba tare da daukar matakai da manufofin mulkin Tinubu ba.

    “Kamar yadda gwamnati ta aiwatar na cire tallafin man fetur ba tare da shiri ba, haka ma gwamnati ya kamata ta shiga harkar shigowa da abinci ba tare da la’akari da illolinsa ba. Kuma babban illa na ba ‘yan kasuwa izinin shigowa da abinci shi ne, rage kwarin gwiwar samarwa a gida. Kunka karafaf bai wa manoma na kasashen waje kwarin giwa wadanda gwamnatocinsu suka riga suka tallafa musu ta hanyoyi da dama.

    “Alhali abin da manomanmu ke bukata ko abin da tattalin arzikinmu ke bukata a kan irin wannan tallafi su ne, matakanmu na kare kanmu don dakile tallafin da masu samarwa na kasashen waje ke samu a cikin kasuwancin duniya wanda ya kamata ya zama kasuwanci kyauta. Yanzu masu samarwarmu ba su samu hakan ba, a maimakon haka ana matsa su fita daga kasuwanci.

    “Idan aka duba a cikin shekarun mulkin Buhari, tsawon shekaru uku, daga 2016 zuwa 2018, Nijeriya tana samar da fiye da tan miliyan 10 na shinkafa a kowace shekara, wanda ya ragu zuwa tan miliyan 8 a kowace shekara daga 2019 zuwa 2022 saboda rashin tsaro da ambaliyar ruwa. Samar da shinkafa ya ragu zuwa kimanin tan miliyan 4 a shekarar 2025 kuma zai iya raguwa fiye da haka a shekarar 2026, kawai saboda babu abubuwan karfafa samarwa. Kuma wannan zai kara shafar sarrafa abinci kuma zai kara matsa lamba kan faduwar darajar naira.

    “Babu ma’ana cewa gwamnati ta cire hannunta wajen tallafa wa bangaren samar da shinkafa, sannan ta juya ta ce bangaren ya rike kansa. Wannan lamari yana kara durkushe harkokin kasuwancin shinkafa.

    “A yanzu akwai wani tsari da ake kira habaka shinkafa a kasa 2020-2030. Tsari ne mai kyau, amma sai dai idan kun ba da karin kudi ga hanyoyin samar da shinkafa ta hanyar farashi mai kyau, wato, manoma ko masu samarwa suna samun farashi mai kyau bisa kokarinsu, ba za a samu wani abin da zai fito daga wannan tsari ba. Dole ne ku ba da karin kwarin gwiwa wajen samarwa, saboda sabanin ra’ayoyi da yawa da aka yi tsammani na dogon lokaci da noman gida duk hanyoyin tattalin arziki ne wadanda kuma ke yanke shawara ta hankali da ta hada da samun riba mafi yawa,” in ji shi.

    Wani rahoto a kwanan nan daga Hukumar Tsara Manufofin Kasuwancin Noma ta Kasa (NAPM) da wani kwamitin shawarwari ga shugaban kasa, sun nemi daukar mataki cikin gaggawa kan wannan al’amari.

    Rahoton ya bayyana cewa kimanin manoman shinkafa 3,500 suna barin noma ko rage yawan shinkafar da suke nomawa saboda asara mai yawa, da aka kiyasta na naira biliyan 93, da aka yi a lokacin noman rani na 2025.

    Binciken ya nuna cewa manoma 33,507 a jihohi 13 na gwaji kuma ya gano cewa kashi 10.6 cikin dari na manoman shinkafa suna da niyyar rage yawan amfanin gona a lokacin noman rani na shekarar 2025/2026.

    A cikin rahoton kwamitin da ke bai wa shugaban kasa rawara ya kuma bayyana cewa samar da shinkafa ya ragu da kashi 7.9 a cikin lokacin damina na bara, yayin da manoma suka koma ga noman amfanin gona na kudi irin su wake, citta da alkama, wanda a yanzu ke bayar da ribar mai yawa da kuma kashe kudi kadan.

    Yawancin manoman shinkafa da wakilanmu suka gana da su sun tabbatar da cewa sun kamala girbin shinkafarsu.

    Daya daga cikinsu, Alhaji Shehu Garun Malam, wanda ke ikirarin cewa ya shafe shekaru yana yin noman shinkafa, ya ce zai daina noman shinkafa gaba daya.

    “Sakamakon da muka samu kan shinkafa a kakar damina ta baya bai yi dadi ba kwata-kwata, har ma farashinta ya fadi duk da kashe kudi mai yawa a kayan aikin gona. Da dama daga cikinmu mun yi asara. Abin da ya kara muni, gwamnati ta ba da rangwame ga shigo da shinkafa. Shi ya sa muke shirin canzawa zuwa wasu kayan gona masu daraja domin ci gaba da kasancewa a wannan fanni. Mun gano cewa akasin shinkafa, samar da wake ya karu da kaso mai yawa a 2025, inda manoma suka samu kudin shiga fiye da na shinkafa a kowace hekta,” in ji shi.

    [ad_2]

    Source link

  • ’Yan bindiga sun sace sakataren ƙaramar hukuma a Kano

    [ad_1]



    ’Yan bindiga sun kai hari gidan sakataren Ƙaramar Hukumar Kibiya a Jihar Kano, tare da yin awon gaba da shi.

    Shugaban kansiloli na ƙaramar hukumar, Hon. Sabo Yusuf Usman, ya shaida wa BBC cewa lamarin ya faru ne a daren ranar Juma’a a gidan sakataren da ke garin Dinya.

    Ya ce harin ya faru da misalin ƙarfe 1 na dare, lokacin da sakataren ke barci a gidansa.

    A cewarsa, maharan sun fara tayar da ɗan sakataren da ke kwance a harabar gida, sannan suka tilasta masa ya buga ƙofa ya yi kamar yana fama da ciwon ciki.

    “Da yaron ya buga ƙofa, mahaifinsa ya tambaye shi ko wane ne. Yaron ya ce shi ne, ya ce yana fama da ciwon ciki ne.

    “Da mahaifin ya buɗe koda, sai ’yan bindigar suka tafi da su gaba ɗaya,” in ji shi.

    Ya ƙara da cewa daga baya maharan sun saki yaron, amma suka tafi da sakataren.

    Jami’an tsaro sun isa wajen bayan faruwar lamarin, amma ba su samu kowa ba domin sun tafi.

    Ƙaramar Hukumar Kibiya ba ta saba fuskantar irin waɗannan hare-hare ba.

    Sai dai, maƙwabtan ƙananan hukumomi irin su kamar Tsanyawa da Shanono, waɗanda ke maƙwabtaka da Jihar Katsina, sun sha fama da hare-haren ’yan bindiga a baya.


    [ad_2]

    Source link