Tinubu ya bai wa masu neman muƙaman zaɓe wa’adin yin murabus
[ad_1]
Shugaba Bola Tinubu ya buƙaci dukkan masu riƙe da muƙaman gwamnati da ke sha’awar tsayawa takara a zaɓen 2027 da su yi murabus tsakanin yanzu zuwa 31 ga Maris, 2026.
Wannan umarni yana ƙunshe ne a cikin wata sanarwa da ofishin Sakataren Gwamnatin Tarayya (SGF) ya fitar a ranar Talata.
Sanarwar ta ce: “Shugaba Bola Ahmed Tinubu, GCFR, ya umarci dukkan masu riƙe da muƙaman siyasa a ƙarƙashin gwamnatinsa waɗanda ke da niyyar tsayawa takarar muƙaman zaɓe a zaɓukan gama-gari na 2027 masu zuwa, da su yi murabus daga muƙaman su a ranar 31 ga Maris, 2026, ko kafin hakan.”
“Wannan umarni ya biyo bayan tanadin doka ta Sashe na 88(1) na Dokar Zaɓe ta 2026, da kuma jadawalin da Hukumar Zaɓe Mai Zaman Kanta (INEC) ta fitar na gudanar da zaɓukan fidda gwani na jam’iyyu gabanin babban zaɓen 2027,” in ji sanarwar.
A cikin wata wasiƙa da Sakataren Gwamnatin Tarayya, Sanata George Akume ya sanya wa hannu, wadda Babban Sakatare a Ofishin Ayyuka na Gwamnati, Dr. Ibrahim Abubakar Kana ya fitar, an bayyana cewa sharaɗin murabus ɗin ya shafi dukkan nau’ukan masu naɗin siyasa na shugaban ƙasa waɗanda ke son shiga zaɓukan fidda gwani na jam’iyyu ko neman takarar kowane mukamin zaɓe.
Wadanda abin ya shafa sun haɗa da: Ministoci da Ministocin Jiha da Masu Ba Shugaban Kasa Shawara na Musamman, da Mataimaka na Musamman ga Shugaban Kasa (SSAs da SAs), da Mataimaka na ƙashin kai ga Shugaban Kasa da dukkan Shugabannin Hukumomi da Manyan Jami’an Gudanarwa na rassan gwamnatin tarayya, hukumomi, da kamfanonin gwamnati, da kuma duk sauran masu naɗin siyasa na Shugaban Kasa.
An umarci dukkan jami’an da abin ya shafa da su miƙa wasiƙunsu na murabus ta ofishin Sakataren Gwamnatin Tarayya kafin ranar 31 ga Maris, 2026.
Shugaba Tinubu ya jaddada cewa wannan mataki ya zama dole domin tabbatar da bin dokokin zaɓe, kiyaye gaskiya a harkar siyasa, da kuma samar da daidaito ga dukkan masu neman takara gabanin zaɓe.
Masu alaƙa
[ad_2]
Source link