Sojoji Sun Kashe Ɗan Fashi, Sun Kama Ɓarayin Shanu A Binuwe Da Nasarawa


Dakarun Operation Whirl Stroke (OPWS) sun ƙara zafafa ayyukan tsaro bisa sahihin bayanan sirri a jihohin Biniwe da Nasarawa, inda suka kashe wani ɗan fashi ɗauke da makami tare da kama wasu da ake zargi da fashi da satar shanu.

A cewar wata sanarwa da Laftanar Ahmad Zubairu Zubairu, muƙaddashin jami’in yaɗa labarai na OPWS ya sanyawa hannu, ayyukan da aka gudanar tsakanin 3 zuwa 5 ga Fabrairu, 2026, sun haɗa da sintirin haɗin gwuiwa tsakanin sojoji, da ƴansanda da rundunar kare fararen hula ta Jihar Binuwe domin daƙile barazanar tsaro a yankunan karkara.

  • Sin Ta Yi Imanin Karin Kamfanonin Mabambantan Kasashe Za Su Zo Hong Kong Don Zuba Jari Da Fara Kasuwanci
  • Amurka Ta Tura Sojojinta Zuwa Nijeriya Don Taimakawa Yaƙi Da ’Yan Ta’adda

A ranar 3 ga Fabrairu, dakarun sashi na 1 na OPWS sun yi artabu da makiyaya ɗauke da makamai a ƙauyen Ayamba da ke ƙaramar Hukumar Katsina-Ala ta Jihar Benue, inda aka kashe ɗan fashi guda ɗaya, tare da kwato bindigar AK-47, mujallu biyu da harsashi uku.

Haka kuma a Nasarawa, dakarun sashi na 2 da ke sansanin Agyaragu sun kama wani da ake zargi da fashi, Adam Paul mai shekaru 34, bayan samun bayanan sirri kan ayyukan da ake zargi da aikatawa a yankin Obi. A Binuwe kuma, dakarun bataliya ta musamman sun kama wasu mutane da ake zargi da satar shanu a Agagbe, tare da miƙa su ga ’yansanda domin bincike.

Kwamandan rundunar, Manjo Janar Moses Gara, ya yaba wa dakarun bisa jajircewa da ƙwazo, yana mai kira da a ci gaba da zafafa sintiri domin hana masu laifi samun damar aiwatar da ayyukansu. Ya kuma gode wa al’umma da sauran hukumomin tsaro kan goyon bayan da suke bayarwa.



Source link

Similar Posts

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *