NAJERIYA A YAU: Siyasa da tsare-tsaren gwamnati da suka dabaibaye 2025

[ad_1]

Ƙarin Podcasts



Yayin da muke bankwana da shekarar 2025, siyasar Najeriya ta kasance cike da sauye-sauye, rikice-rikice, da kuma manyan al’amura da suka shafi iko, jam’iyyu da shugabanci.

Shekarar ta shaida sauyin sheƙar ’yan siyasa, rikicin cikin gida a wasu jam’iyyu, da kuma fafutukar karɓar ragamar mulki a jihohi da matakin tarayya, lamarin da ya ƙara zafafa siyasar ƙasa.

A ɓangaren tsare-tsaren gwamnati kuwa, 2025 ta kasance shekara mai ɗauke da tsauraran manufofi da suka shafi tattalin arziki, tsaro da walwalar al’umma.

Gwamnati ta ɗauki matakai masu nauyi domin tunkarar matsalolin tsadar rayuwa, rashin tsaro da sauye-sauyen tattalin arziki, inda wasu tsare-tsaren suka samu karɓuwa, wasu kuma suka jawo muhawara mai zafi a tsakanin ’yan ƙasa.

Shirin Najeriya A Yau na wannan lokaci ya yi waiwaye ne kan siyasa da tsare-tsaren gwamnati da suka dabaibaye shekarar 2025 da muke bankwana da ita.

Domin sauke shirin, latsa nan


[ad_2]

Source link

Similar Posts

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *