Mutane 4 Sun Rasu A Turmutsutsun Rabon Tallafin Ramadan A Katsina
[ad_1]
Akalla mutane huɗu ne suka rasu sakamakon turmutsutsu da ya faru yayin rabon tallafin Ramadan na shekara-shekara a unguwar Kofar-Guga da ke Katsina, kamar yadda Rundunar ‘Yan Sandan Jihar ta tabbatar.
A cikin wata sanarwa da kakakin rundunar, DSP Aliyu Abubakar, ya fitar, ya bayyana lamarin a matsayin abin takaici.
Sanarwar ta ce, “Rundunar ‘Yansandan Jihar Katsina tana mai alhinin sanar da faruwar wani turmutsutsu da ya afku yayin rabon tallafin Ramadan na shekara-shekara a unguwar Kofar-Guga, wanda ya janyo mutane da dama suka samu raunuka.”
A cewarsa, a ranar 26 ga Fabrairu, 2026, da misalin ƙarfe 9:00 na dare, an samu kiran gaggawa a Babban Ofishin ‘Yansanda da ke Katsina cewa wani taron jama’a mai yawa ya haifar da turmutsutsu yayin rabon tallafin Ramadan a gidan wani Alhaji da ke unguwar Kofar-Guga.
[ad_2]
Source link