Muna bai wa ’yan Najeriya haƙuri kan ƙaranci wutar lantarki — Ministan Makamashi
Ministan Makamashi, Bayo Adelabu, ya nemi afuwar ’yan Najeriya bisa rashin isasshiyar wutar lantarki da ake fuskanta a halin yanzu.
Ministan ya bayyana hakan ne a wani taron manema labarai da aka gudanar a Abuja.
A cewar Ministan, matsalar wutar da ake fama da ita a kwanakin nan tana da nasaba ne daga wasu ƙalubalai da suka dabaibaye fannin samar da lantarki.
Ya ce matsalolin sun fi ƙarfin ma’aikatar tasa a magance su cikin ƙanƙanin lokaci, wanda hakan ya haifar da ƙarancin wutar lantarki a ƙasar.
Sai dai ya tabbatar wa ’yan Najeriya cewa nan ba da jimawa ba za a fara ganin sauyi a fannin samar da lantarki a faɗin ƙasar.
A cewarsa, kafin ƙarshen shekarar nan, gwamnati na da burin cimma samar da isasshiyar wutar lantarki ga ’yan Najeriya.