Mota ta afkawa jama’a ta kashe mutum 3 da raunata wasu
[ad_1]
Wani hatsarin mota da ya faru a ranar Laraba ya haddasa mutuwar mutane aƙalla uku, yayin da wasu kimanin 40 suka jikkata.
Hatsarin ya faru ne bayan da wata mota ƙirar kanta ta afkawa mutanen da ke zaune a gefen titi a kan hanyar Gombe zuwa Potiskum a Jihar Yobe.
Kamar yadda wata majiya ke cewa, hatsarin ya faru ne da misalin ƙarfe 2:30 na rana a ranar Laraba kusa da garin Badejo na ƙaramar hukumar Potiskum, wani yanki mai cike da jama’a akan wannan babbar hanya ta zuwa Gombe daga garin Potiskum.
Shaidu sun ce, direban motar yana tafiya ne sai motar ta ƙwace a hannunsa ta bar hanya da sauri ta buge waɗanda ke zaune a gefen titi.
Kwamandan Sashen Hukumar kiyaye haɗurra FRSC na Jihar, Paul Andrew, ya tabbatar da lamarin ga manema labarai a wata hira ta wayar tarho.
Andrew ya ce, “hatsarin ya faru ne da misalin ƙarfe 2:30 na rana kusa da garin Badejo a kan babbar hanyar Gombe zuwa Potiskum yadda ya shafi wata motar canter da ta afkawa mutanen da ke zaune a gefen titi, wanda ya yi sanadiyyar asarar rayukan mutane uku tare da jikkata wasu da dama.”
Ya ƙara da cewa, binciken farko ya nuna cewa, yawan lodin kaya da gudu a kan babbar hanyar su ne manyan abubuwan da ke haifar da hakan.
Ya ce, “Daga binciken da muka yi zuwa yanzu, hatsarin ya faru ne sakamakon yawan lodi da kuma yawan gudu.
“A cewarsa direban motar ya rasa ikon sarrafa motar yayin da yake tunkarar wani yanki mai cike da jama’a da ke gefen titin, kuma abin takaici, wannan ya haifar da mutuwar mutane uku da jikkata wasu.”
Masu alaƙa
[ad_2]
Source link