Lokacin Cire Jar Hula Bai Yi Ba – Gwamnan Kano


Gwamnan Jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, ya sake tabbatar wa magoya bayansa cewa zai ci gaba da sanya hular ja ta Kwankwasiyya, duk da cewa ya koma jam’iyyar (APC).

An dade ana ta rade-radin a jihar kan kin barin hular da gwamnan ya yi, wadda ta shahara a matsayin alamar tafiyar Kwankwasiyya.

  • Iran Ta Musanta Ikirarin Trump Tare Da Zafafa Hare-hare Kan Isra’ila
  • Gwamnatin Tarayya Ta Yi Alkawarin Kawo Karshen Matsalar Tsaro A Zamfara

Sai dai lokacin da aka gan shi a Yola, Jihar Adamawa, sanye da wata shadda mai launin shudi mai dauke da tambarin Bola Ahmed Tinubu, wasu daga cikin magoya bayansa sun tambaya ko su ma za su iya ajiye hular ja.

Amma mai magana da yawun gwamnan, Sanusi Bature Dawakin Tofa, ya ce har yanzu ba a bayar da umarni a daina sanya hular ba, domin “lokaci bai yi ba tukuna.”

A wani sako da ya wallafa a shafinsa na Facebook a ranar Talata, Dawakin Tofa ya ce, “Har yanzu babu wani umarni da aka bayar na cire hular ja. Wannan fita ce ta musamman a Yola, Jihar Adamawa, inda manyan baki suka sanya kaya iri daya. Mu yi hakuri; komai yana da lokacinsa.”

Wannan karin bayani na zuwa ne yayin da muhawara ke kara zafi kan ci gaba da sanya hular ja da Yusuf ke yi, wadda aka dade ana danganta ta da tafiyar Kwankwasiyya karkashin jagorancin tsohon ubangidansa, Rabiu Musa Kwankwaso.

Duk da cewa Yusuf ya nesanta kansa daga cikin manyan ‘yan cikin tafiyar Kwankwasiyya, har yanzu yana rike da hular ja a matsayin wani bangare na siyasarsa. Masana na ganin hular ta wuce siyasar bangarori, ta zama wata alama ta al’ada a Kano.

Rahoton Daily Trust ya nuna cewa a baya-bayan nan, da dama daga cikin mabiya Kwankwasiyya da ma wasu magoya bayan gwamnan na kira gare shi da ya daina sanya hular, kamar yadda magabacinsa, Abdullahi Ganduje, ya yi lokacin da ya rabu da Kwankwaso a shekarar 2018.



Source link

Similar Posts

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *