Ƴan Ta’adda Sun Kai Hari Kachia, Sun Kashe Mutum 8, Sun Sace Wasu Da Dama

[ad_1]

Ƴan ta’adda sun kai hari a ƙauyen Wake da ke ƙaramar hukumar Kachia, jihar Kaduna, inda suka kashe mutum takwas tare da yin garkuwa da wasu da dama.

Bayanan farko sun nuna cewa waɗanda suka samu raunuka a harin an garzaya da su Asibitin Katolika na Saint Gerard domin samun kulawar likitoci.

Duk da cewa cikakkun bayanai kan lamarin ba su fito fili ba tukunna, majiyoyi sun tabbatar da faruwar harin. Sai dai duk wani yunƙuri na jin ta bakin jami’an ƙaramar hukumar Kachia bai samu nasara ba, domin sun ce za su yi ƙarin bayani bayan an kammala kula da waɗanda suka jikkata.

Karin bayani zai biyo baya…




Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp



[ad_2]

Source link

Similar Posts

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *