Jam’iyyar NNPP Tayi Ɓatan Dabo A Tarkadar Zaɓen Cike Gurbi Na Kano

[ad_1]

Yayin da mazauna Kano suka fita zaɓe domin zaɓen mambobi biyu na Majalisar Dokokin Jihar, an yi mamakin rashin ganin sunan jam’iyyar New Nigeria Peoples Party (NNPP) a takardar zaɓe. Rahotanni sun nuna cewa ana danganta cire jam’iyyar da rikice-rikicen shari’a da ke addabar shugabancinta, duk da cewa jami’an INEC ba su yi ƙarin haske kai tsaye ba.

An gudanar da zaɓen ne a mazaɓun Kano Municipal da Ungogo, inda aka ruwaito cewa an samu zaman lafiya a yawancin rumfunan zaɓe, saɓanin wasu zaɓukan baya da suka fuskanci tashin hankali. Jami’an tsaro da na zaɓe sun ce ba a samu manyan matsaloli ba a yayin gudanar da aikin.

  • NNPP Ta Yi Watsi DA Rahoton Hukuncin Amurka Kan Kwankwaso
  • Ɗan Majalisar NNPP Ɗaya Tilo A Bauchi Ya Sauya Sheƙa Zuwa APC

Sai dai halartar masu zaɓe ya yi ƙasa, inda wasu mazauna suka danganta hakan da rashin NNPP a takardar zaɓe, yayin da wasu suka ce gajiyawar siyasa da rashin sha’awa ne suka rage yawan fitowar jama’a.

Mai bai wa gwamna shawara kan kafafen sada zumunta, Salisu Yahaya Hotoro, ya yaba da yanayin zaman lafiyar, yana mai danganta shi da manufofin Gwamna Abba Kabir Yusuf na #KanoFirst. A cewarsa, matakan da gwamnati ta ɗauka sun taimaka wajen tabbatar da tsaro da kwanciyar hankali.

Rahoton fine News Nigerian ya bayyana cewa; Rashin NNPP a takardar zaɓe ya bai wa ‘yan takarar APC damar zama manyan ‘yan takara a zaɓen. Ƙoƙarin jin ta bakin Hashimu Dungurawa, shugaban wani ɓangare na jam’iyyar, bai yi nasara ba, yayin da wasu masu zaɓe suka nuna ra’ayoyi mabambanta kan lamarin duk da jin daɗinsu da zaman lafiyar da aka samu.

[ad_2]

Source link

Similar Posts

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *