Hotunan wuraren da Amurka ta kai wa hari a Sokoto

[ad_1]



Al’ummar garin Tangaza da Tambuwal a Jihar Sakkwato sun shiga cikin firgici a ranar Alhamis yayin da Amurka ta ƙaddamar da farmakin soji kan ’yan ta’adda a yankin Arewa maso yammacin Najeriya.

Shugaba Donald Trump ya sanar da matakin na soja a wani saƙon da ya wallafa a shafin sada zumunta da yammacin ranar Alhamis.

Mazauna Ƙananan hukumomin Tangaza da Tambuwal a Jihar Sokoto, sun tabbatar da hare-haren da jiragen yaƙi marasa matuƙa suka kai wa unguwanninsu, da sojojin Amurka suka kai.

Binciken da wakilinmu ya samu ya nuna cewa, ɗaya daga cikin hare-haren ya afku ne a gundumar Jabo da ke Ƙaramar hukumar Tambuwal, unguwar da a baya ta fuskancin rashin tsaro.

Ministan harkokin wajen Najeriya, Yusuf Maitama Tuggar, ya ce hare-haren da aka kai ta sama wani ɓangare ne na ayyukan haɗin gwiwa da ake yi tsakanin Najeriya da Amurka.

Ga hotunan wuraren:


[ad_2]

Source link

Similar Posts

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *