Hatsarin tirela ya laƙume rayukan mutum 6 a Yobe




Aƙalla mutane shida ne aka tabbatar da mutuwarsu bayan wani mummunan hatsarin mota da ya rutsa da wata tirela da wata babbar mota a hanyar Potiskum zuwa Damaturu ranar Alhamis.

Shedun gani da ido sun ce hatsarin ya faru ne bayan da motar da ake zargin ta yi kaca-kaca da wata tirela da ke zuwa.

“Motar kirar Canter na kan hanyar da ba ta dace ba lokacin da ta afka cikin tirelar,” in ji wani ganau.

Mutane huɗu ne suka maƙale a cikin tirelar inda daga bisani aka tabbatar da mutuwarsu a wurin, yayin da sauran biyun da suka mutun na cikin motar Canter.

Wasu ƙarin mutane biyu sun tsira daga haɗarin kuma an kai su wani asibiti da ke kusa domin yi musu magani.

Jami’in hulɗa da jama’a na rundunar ’yan sandan Jihar Yobe, SP Dungus Abdulkarim, a yayin wata tattaunawa ta wayar tarho, ya tabbatar wa jaridar PUNCH haɗarin.

Ya ce, “Hatsarin ya afku ne a kan babbar hanyar Potiskum zuwa Damaturu wanda ya haɗa da tirela da wata mota ƙirar Canter, mutane 6 ne suka rasa rayukansu, yayin da wasu biyu suka samu raunuka kuma suna samun kulawa.”

Ya ƙara da cewa, “A halin yanzu ana ci gaba da bincike don gano musabbabin hatsarin, kuma muna kira ga masu amfani da hanyar da su riƙa tuƙa mota a kodayaushe tare da bin ƙa’idojin hanya.”




Source link

Similar Posts

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *