Tinubu Ya Dawo Nijeriya Bayan Shafe Makonni A UAE Da Turai

[ad_1]

Shugaban ƙasa Bola Tinubu ya dawo Nijeriya a ranar Asabar bayan halartar taron Abu Dhabi Sustainability Week 2026 a Haɗaɗɗiyar Daular Larabawa (UAE).

Mai magana da yawunsa, Bayo Onanuga, ya ce Nijeriya ta sanya hannu kan yarjejeniyar Comprehensive Economic Partnership Agreement da UAE a yayin taron.

  • Hukumar Kwastam Ta Fitar Da Wasu Sabbin Ƙa’idoji Ga Kamfanonin Rabar Da Kaya
  • Shugaban Xi Ya Karbi Sabbin Jakadun Kasashen Waje A Kasar Sin

Yarjejeniyar na da nufin ƙarfafa cinikayya da zuba jari, bunƙasa fasaha, da faɗaɗa haɗin gwiwa a fannonin makamashi, noma, gine-gine da haƙar ma’adinai.

Shugaba Tinubu ya kuma sanar da cewa za a gudanar da taron haɗin gwiwa na Nigeria–UAE INVESTOPIA a Legas a watan Fabrairu domin jawo hankalin masu zuba jari daga sassa daban-daban na duniya.

Ya ƙara da cewa Nijeriya na shirin tara dala biliyan 30 a duk shekara domin ayyukan sauyin makamashi da kare muhalli.

Tun da farko a ranar Asabar, Onanuga ya wallafa wani bidiyo da ke nuna lokacin da Shugaba Tinubu ke barin otel ɗinsa a Abu Dhabi domin dawowa gida Nijeriya.

[ad_2]

Source link

Similar Posts

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *