Majalisar Dattawa Za Ta Tantance Sabon Ministan Tsaro Ranar Laraba

[ad_1]


A wani ɓangare na tabbatar da mahimmancin tsaro, Majalisar Dattawa ta bayyana cewa za ta tantance tsohon Babban Hafsan Tsaro, Janar Christopher Gwabin Musa, a matsayin sabon Ministan Tsaro, ranar Laraba.

Shugaban masu rinjaye na Majalisar Dattawa, Sanata Opeyemi Bamidele ya bayyana hakan a cikin wata sanarwa da mai taimaka masa kan harkokin yada labarai da hulda da jama’a ya fitar ranar Talata, yana mai jaddada muhimmancin aikin wajen tabbatar da tsaron rayuka da dukiyoyin al’ummar kasar nan.

Nadin Janar Musa (mai ritaya) da Shugaba Bola Tinubu ya yi ya biyo bayan murabus din tsohon Ministan Tsaro, Alhaji Mohammed Badaru, saboda rashin lafiya.

Saboda haka, Shugaba Tinubu ya nada tsohon shugaban tsaron a matsayin sabon Ministan Tsaro ta hanyar wata wasika da aka aika wa Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Godswill Akpabio ranar Talata.

[ad_2]

Source link

Similar Posts

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *