Hamɓararren Shugaban Guinea-Bissau ya gudu Senegal

[ad_1]



Hamɓararren Shugaban Ƙasar Guinea-Bissau, Umaro Sissoco Embaló, ya isa ƙasar Senegal bayan da sojoji da suka kifar da gwamnatinsa a wannan makon suka sake shi.

Wannan ya biyo bayan tattaunawar ƙungiyar ECOWAS yayin da tashin hankali ke ƙaruwa a ƙasar sakamakon juyin mulkin.

Ma’aikatar harkokin wajen Senegal a cikin wata sanarwa ta ce Embaló ya sauka a cikin ƙasar “lafiya kalau” a jirgin sojoji da aka ɗauka a haya da yammacin Alhamis.


[ad_2]

Source link

Similar Posts

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *