EFCC Ta Gabatar Da Ƙarin Hujjoji A Shari’ar Tsohon Gwamnan Kogi, Yahaya Bello
[ad_1]
A yau ne Mai Shari’a Maryanne Anineh ta Babbar Kotun birnin tarayya da ke Maitama a Abuja, ta ci gaba da sauraron shari’ar tsohon gwamnan Jihar Kogi, Yahaya Bello, inda Hukumar EFCC ta gabatar da ƙarin bayanan banki a matsayin hujjoji. EFCC na tuhumar Yahaya Bello tare da Umar Shuaibu Oricha da Abdulsalami Hudu da laifuka 16 da suka shafi cin amana da halatta kuɗin haram da ake zargin sun kai Naira biliyan 110.4.
A zaman kotun, lauyan gwamnati Kemi Pinheiro, SAN, ya bayyana cewa an sake tsayar da shaida ta shida (PW6), Mashalia Arhyel Bata, jami’in bin doka da oda na Zenith Bank, domin ci gaba da yi masa tambayoyi. Shaidan ya bayyana wasu muhimman bayanai a kan shigar da kuɗi da fitarwa daga asusun, ciki har da biyan kuɗi ta cak da canja wurin kuɗi daga Hukumar Haraji ta Jihar Kogi da wasu kamfanoni, inda ya jaddada cewa ba ya iya tantance manufar kuɗaɗen da aka biya ko inda aka kashe su.
- Zargin Almundahanar ₦1.35bn: Kotun Ƙoli Za Ta Warware Taƙaddamar EFCC Da Lamiɗo
- Kotu Ta Sake Ci Gaba Da Shari’ar ‘Yan Bindiga Biyar Masu Alaka Da Bello Turji
Lauyoyin masu kare waɗanda ake tuhuma sun yi wa shaidan tambayoyi kan sahihancin takardun da aka gabatar, tare da nuna cewa wasu daga cikin waɗanda ke cikin lamarin na iya kasancewa suna aiwatar da ayyukansu ne kawai a matsayinsu na ma’aikata. Sai dai lauyan gwamnati ya yi ƙorafi kan wasu tambayoyi, wanda Mai Shari’a Anineh ta amince da su, tana mai jaddada cewa shaida ba zai iya bada ra’ayi kan matsayin ma’aikata a gwamnatin jihar ba.
A ci gaba da shari’ar, EFCC ta gabatar da wasu shaidu daga Keystone Bank, FCMB da Bankin Sterling, waɗanda suka kawo bayanan asusu da takardun bin doka da oda na kamfanoni da asusu daban-daban, inda aka nuna shigar kuɗi masu yawa da suka kai miliyoyin Naira. Bayan sauraron shaidu, kotu ta ɗage zaman zuwa Juma’a, 16 ga Janairu, 2026, domin ci gaba da shari’ar.
[ad_2]
Source link