Mataimakin Shugaban Jam’iyyar APC Na Nasarawa, Aliyu Barde, Ya Rasu

[ad_1]

Mataimakin shugaban jam’iyyar APC, na Jihar Nasarawa, Hon. Aliyu Yakubu Barde, ya rasu.

Iyalan marigayin sun ce ya rasu ne a ranar Talata a Lafia bayan gajeriyar rashin lafiya.

Za a yi jana’izarsa a garinsu Wamba bisa tanadin addinin Musulunci.

Rasuwarsa ta jefa jam’iyyar mai mulki a Jihar cikin jimami.

Sakataren jam’iyyar APC na jihar, Cif Otaru Douglas, ya tabbatar da rasuwar tare da bayyana hakan a matsayin babban rashi ga jam’iyyar da jihar baki ɗaya.

Kafin ya zama mataimakin shugaban jam’iyyar APC, Barde ya taɓa zama Shugaban riƙo na Karamar Hukumar Wamba a zamanin tsohon Gwamnan Jihar Umaru Tanko Al-Makura.




Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp



[ad_2]

Source link

Similar Posts

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *