Da Ɗumi-Ɗumi: Chelsea Ta Raba Gari Da Koci Enzo Maresca

[ad_1]

Ƙungiyar kwallon kafa ta Chelsea ta raba gari da kocinta, Enzo Maresca, duk da kasancewar ƙungiyar a matsayi na biyar a gasar Firimiya. Ɗan ƙasar Italiya mai shekaru 45 ya bar aikin horar da ƙungiyar ne ƙasa da watanni shida bayan ya jagoranci Chelsea ta lashe Kofin Duniya na Ƙungiyoyi a ƙarshen kakarsa ta farko a filin Stamford Bridge.

Chelsea ta yanke wannan shawara ne a yayin da take ƙoƙarin gyara tafiyarta a kakar wasa ta bana, bayan da ta samu nasara ɗaya kacal cikin wasanni bakwai na baya-bayan nan a gasar Firimiya. A watan Disamba kaɗai, ƙungiyar ta tara maki shida daga wasanni shida, lamarin da ya bar tazarar maki 15 tsakaninta da Arsenal da ke kan gaba a teburin gasar.

  • Abinda Ya Kamata Kusani Akan Wasan Arsenal Da Chelsea
  • Tinubu Ya Soke Yin Jawabi Ga ‘Yan Kasa Na Ranar Dimokuradiyya, Zai Yi Daga Zauren Majalisa

Duk da ƙanƙancin lokacin da ya yi a kulob ɗin, Maresca ya samu yabo daga shugabannin Chelsea, ciki har da daraktocin wasanni Paul Winstanley da Laurence Stewart, da kuma mai hannun jari Behdad Eghbali. Ya jagoranci ƙungiyar zuwa matsayi na huɗu a teburin gasar tare da lashe gasar zakarun Turai da kuma Kofin Duniya na Ƙungiyoyi a bara, duk da cewa kwantiraginsa na gudana har zuwa shekarar 2029.

Sai dai rahotanni sun nuna cewa an samu rashin jituwa tsakaninsa da wasu manyan ƴan wasa, tare da rashin jin ɗaɗinsa kan gazawar kulob ɗin wajen sayen sabon ɗan baya bayan samun raunin Levi Colwill. Shugabannin kulob ɗin sun ce ɗaukar matakin sayen ɗan wasa zai iya sa matashin ɗan ƙaramar ƙungiyar Chelsea, Josh Acheampong, neman barin ƙungiyar. Waɗannan dalilai, da wasu batutuwa na cikin gida, sun sa ɓangarorin biyu suka amince da raba gari.

[ad_2]

Source link

Similar Posts

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *