Category: Latest News

  • Arsenal Na Tattaunawa Da Declan Rice Kan Tsawaita Kwantiraginsa A Ƙungiyar

    [ad_1]

    Ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Arsenal ta fara tattaunawa da ɗan wasanta, Declan Rice, kan yiwuwar sanya hannu kan sabon kwantiragi a ƙungiyar.

    Kwantiragin Rice na yanzu zai ƙare cikin shekaru biyu, amma tun da farko akwai zaɓin tsawaita wa’adin da ƙarin watanni 12.

    • Zaben 2027: Jam’iyyun Siyasa Na Kokarin Cika Wa’adin Dokar Zabe
    • Ramadan: Lokutan Buda-Baki Da Sahur Na Azumi Na 24

    Arsenal, wadda ke jan ragamar teburin gasar Premier League, na fatan ɗan wasan na tawagar Ingila ya sadaukar da shekaru masu yawa ga ƙungiyar.

    Sabon tayin zai haɗa da ƙarin albashi domin zama a matsayin ɗaya daga cikin ‘yan wasan da suka fi samun albashi mai tsoka a Arsenal.

    Kwanan nan, Bukayo Saka ya sanya hannu kan sabon kwantiragi na shekaru huɗu da rabi wanda zai sa ya karɓi aƙalla £300,000 a kowane mako.

    Ana hasashen kwantiragin Rice zai kai kimanin £240,000 a kowane mako, kuma tattaunawar da aka fara an bayyana ta a matsayin mataki na farko wajen ganin Declan ya amince da sabon kwantiragi.

    Tun bayan da ya koma Arsenal daga West Ham a yarjejeniyar da ta kai £105 miliyan a shekarar 2023, ɗan wasan mai shekaru 27 ya yi suna a matsayin ɗaya daga cikin ‘yan wasa masu kyau a Turai.

    Ya riga ya buga wasanni 102 a gasar Premier League da Arsenal.

    [ad_2]

    Source link

  • Yadda aka yi zanga-zangar goyon bayan Falasɗinawa a Kano

    [ad_1]



    Dubban Musulmi a Jihar Kano sun gudanar da zanga-zanga a ranar Juma’a domin nuna goyon baya ga Falasɗinawa tare da yin Allah-wadai da hare-haren da ake kai wa Iran.

    Yawancin masu zanga-zangar mabiya Shi’a ne.

    Sun taru ne bayan idar da sallar Juma’a a Masallacin Fagge da ke birnin Kano.

    Masu zanga-zangar sun yi tattaki a manyan tituna ɗauke da tutocin Falasɗinu, Iran da Najeriya.

    Sun yi zanga-zangar ɗauke da kwalaye masu rubuta kamar “Free Palestine,” “Death to Israel,” da kuma “We support Iran.”

    A yayin zanga-zangar, sun kuma nuna wasu akwatunan gawa guda biyu da aka lulluɓe da tutocin Amurka da Isra’ila.

    Sun ɗora hotunan Donald Trump da Benjamin Netanyahu a kan akwatin gawarwakin.

    Zanga-zangar ta gudana cikin lumana na kusan awa uku.

    Masu zanga-zangar sun fara daga masallacin, suka bi titin Ibrahim Taiwo Road, sannan ƙare a gadar da ke kusa da Ƙofar Nassarawa a titin Zariya.

    Da yake jawabi bayan kammala zanga-zangar, Sheikh Sidi Munir Mainasara, ya ce sun shirya zanga-zangar ne domin tunawa da ranar Ƙudus, wadda ake yin ta a ranar Juma’ar ƙarshen watan azumin Ramadan.

    Ya ce an shafe sama da shekaru 40 ana gudanar da wannan rana a ƙasashe daban-daban ta hanyar wayar da kai, laccoci da tattaunawa kan batun Falasɗinawa.

    A cewarsa, bikin na bana yana da muhimmanci saboda rikicin da ake yi a Falasɗinu, inda mutane da dama suka mutu, wasu suka jikkata, yayin da wasu kuma suka rasa matsugunansu.

    Mainasara, ya kuma yaba wa Jagoran addinin Iran, Ali Khamenei, inda ya ce yana daga cikin shugabannin da ke goyon bayan waɗanda ake zalunta a duniya.

    Malamin ya buƙaci ƙasashen duniya su ɗauki mataki kan zaluncin da Isra’ila ke yi, tare da sake jaddada buƙatar ’yantar da Falasɗinawa.


    [ad_2]

    Source link

  • Zaben 2027: Jam’iyyun Siyasa Na Kokarin Cika Wa’adin Dokar Zabe

    [ad_1]

    Bisa amincewa da dokar zabe ta 2026 da sabon jadawalin lokacin zaben 2027, jam’iyyun siyasa a Nijeriya suna cikin matsin lamba wajen kokarin cika ka’idoji na wa’adin da hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC), ta fitar.

    Ko da yake cibiyar hadakar jam’iyyun siyasa (IPAC), ta yi barazanar kin halartar zaben idan ba a gyara wasu tanade-tanaden doka ba, da yawan jam’iyyun siyasa sun fara daidaita hanyoyin cikin gida don ya dace da sabin abubuwan da ake bukata.

    • Sin Ta Himmatu Wajen Raya Ci Gaban Duniya Na Bai Daya
    • Kawar Da Dukkanin Haraji Kan Hajojin Da Ake Shigarwa Kasar Sin Daga Afirka Zai Bunkasa Cinikayyar Albarkatun Gona Na Afirka Ta Kudu

    Binciken shirye-shirye a tsakanin manyan jam’iyyun siyasa ya nuna cewa an samu mabambantan ra’ayoyi. Yayin da wasu jam’iyyun ke cewa sun shirya don tunkarar zaben, wasu na fama da kalubale na kudade da rikice-rikicen cikin gida da kuma gyare-gyaren gudanarwa da sabon tsarin zaben ya bukata.

    Bayan amincewa da kudirin dokar zabe na 2026, INEC ta saki sabon jadawalin zabukan 2027, ta saka ranakun zaben shugaban kasa da na majalisun kasa a ranar 16 ga Janairu, 2027.

    Daya daga cikin manyan sauyin da dokar ta tanada shi ne, ana bukatar jam’iyyun siyasa su fitar da ‘yan takara ta hanyar zaben fid da gwani na kai tsaye ko kuma ta hanyar yarjejeniya, wanda ya kawar da tsarin wakilai da ake amfani da su a jam’iyya a baya.

    Wani tanadin kuma ya hana kotuna dakatar da ayyukan zabe yayin da shari’o’i suke cikin jiran hukunci.

    Bugu da kari, ana bukatar jam’iyyun siyasa a yanzu su kiyaye cikakken rajistar mambobinsu ta intanet wanda ya kunshi bayanan sirri, ciki har da lambobin shaidar dan kasa (NIN).

    Dole ne a gabatar da rajistar ga INEC akalla kwanaki 21 kafin zabukan fitar da gwani na jam’iyyu da babban tarurrukan jam’iyyu.

    Wadannan sabbin bukatu sun tilasta wa jam’iyyun siyasa a Nijeriya sauye-sauyen cikin gida da shirye-shiryen gudanarwa.

    Jam’iyyar LP karkashin jagorancin, Sanata Nenadi Usman, tana kokarin samun kudade wajen sake gina tsarinta kafin zaben 2027.

    Bayan fitowar sabon jadawalin zabe da INEC ta fitar, jam’iyyar ta kara matsa kaimi wajen sake tabbatar da rajista mambobinta a fadin kasa nan. Sakamakon rikice-rikicen cikin gida da karancin kudade da jam’iyyar take fuskanta ya rage mata tagomashi cikin ayyukanta.

    Rahotanni sun nuna cewa yanayin ya kawo wa jam’iyyar cikas wajen shirya tarukanta a fadi kasar nan, inda wasu jami’ai ake cewa suna tallafa wa ayyukan jam’iyya daga dukiyoyinsu na kashin kai.

    Tsohon sakataren watsa labarai na wucin gadi na jam’iyyar, Mista Tony Akeni, ya nuna damuwa game da yanayin da jam’iyyar take ciki a wata sanarwar da ya fitar.

    “A matsayina na tsohon sakataren watsa labarai na wucin gadi na jam’iyyar LP, na tilasta wa kaina yin hijira daga Jihar Edo zuwa Abuja a ranar 7 ga Agusta, 2025.

    “Tun daga wannan lokaci, ina gudanar da dukkan ayyukana a ofis daga masaukin otel ba tare da samun kobo daga jam’iyyar LP ko masu ruwa da tsaki ba, sai dai kudi data da aka taba ba ni na naira 10,000,” in ji shi.

    Ya bayyana lamarin a matsayin wata manufar jam’iyya da ta samu kanta na kowa ya dauki nauyin kansa wadda ke raunana ayyukan jam’iyyar.

    Duk da wadannan tarin matsaloli, jam’iyyar LP ta riga ta mika jerin sunayen mambobin kwamitin gudanarwarta na jihohi 32 da Babban Birnin Tarayya Abuja, ga INEC a matsayin wani bangare na kokarin sake tsarin jam’iyyar.

    Sanata Nenadi-Usman ta kuma nuna amincewa da karfafa jam’iyyar a matakin kasa, ta lura cewa masu goyon bayan jam’iyyar suna karuwa a dukkan sassan kasar nan baki daya.

    Ita kuwa jam’iyyar APGA ta ce ta riga ta dauki matakai masu muhimmanci don bin sabon tsarin zabe.

    Mai magana da yawun jam’iyyar, Mazi Ejimofor, ya ce APGA ta fara rajistar mambobinta ta intanet tun daga ranar 1 ga Yuni, 2024, kafin cikar wa’adin dokar zabe.

    “Mun shirya sosai saboda idan ka duba abin da APGA ke yi, ko kafin yanzu, za ka fahimci cewa alama mun riga mun dauki matakin dokar zabe.

    “Mu ne jam’iyya ta farko da ta fara yin rajistar mambobita ta intanet tun ranar 1 ga Yuni, 2024,” in ji shi.

    APGA ta kuma bukaci INEC ta tabbatar da cewa ka’idojinta sun yi daidai da na dokar zabe, kuma ka da ta kirkiro wasu karin matsaloli ga kananan jam’iyyun siyasa.

    A halin yanzu, jam’iyyar APC mai mulki ta ce ta kara yin shiri domin zaben 2027 tare da amfani da bayanan mambobi na fasaha da sabon tsarin doka ya zo da shi.

    Shugaban jam’iyya APC ta kasa, Farfesa Nentawe Yilwatda, ya bayyana cewa APC yanzu tana da wani ingantaccen tsarin bayanai na intanet ga mambobita sama da miliyan 10 da aka hada da lambobin shaidar dan kasa.

    “Rijistarmu ta intanet tana ba mu damar samun bayanan mambobinmu. Mun san ko su wane ne, inda suke zaune da kuma yadda za mu isa gare su. Wannan yana ba mu damar tattarawa yadda ya kamata da kuma gudanar da zabukan fid da gwani mafi kyau,” in ji shi.

    Yilwatda ya kuma ce shawarar jam’iyyar ta yi aiki ba tare da kwamitin amintattu ba. Yana mai jaddada cewa APC na so mambobinta su dauki nauyin mallakar jam’iyyar.

    A matsayin wani bangare na shirin zaben 2027, jam’iyyar ta kaddamar da kwamitin shirya babban taronta na kasa, wanda tsohon shugaban majalisar wakilai, Aminu Bello Masari, ke jagoranta.

    Kazalika, jam’iyyar PDP ta kuma ce ta shirya sosai don tunkarar zaben 2027, duk da rashin jituwa da rikicin cikin gida da take fama a kotu.

    Mataimakiyar sakatariyar yada labarai ta PDP, Farida Umar, wadda ta nuna amincewa da shirin jam’iyyar, ta ce, “Mun shirya sosai. Mun kasance a shirye kuma a sahun gaba don karbar mulki daga wannan gwamnati mai rashin tabbas ta Bola Tinubu da jam’iyyar APC.

    “Mun gudanar da tarukanmu daga matakin karamar hukuma zuwa matakin jiha kuma mun dauki duk matakan da suka dace don kasancewar PDP.”

    Umar ya kuma ki amincewa da cewa raguwar yawan gwamnonin jam’iyya zai iya shafar karfinta na tara kudi.

    Sakataren yada labarai jam’iyyar PDP ta kasa, Ini Ememobong, ya tabbatar da cewa jam’iyyar ta fara yin rajistar ‘yan jam’iyya ta yanar gizo bisa bin sabon dokar zabe.

    Haka kuma jam’iyyar ADC ta yi gargadin kan jaddawalin da INEC ta fitar cewa dokokin sun yi wa jam’iyyun adawa tsauri.

    Mai magana da yawun ADC, Bolaji Abdullahi, ya ce bukatar yin rajistar mambobin jam’iyyu ta intanet a dan gajeren lokaci ba abu ne mai yiwuwa ba.

    “Kusan yana da wuya mu yi wannan a aikace. Abin da jam’iyyar gwamnati ta dauki fiye da shekara guda tana yi shi ne abin da suke sa ran mu yi cikin wata daya,’’ in ji shi.

    A cewarsa, yanayin na iya kawo rashin amfani ga jam’iyyun adawa.

    Duk da wannan yanayin, jam’iyyun siyasa a fadin kasar suna kara yin shiri wajen tunkarar zaben 2027.

    [ad_2]

    Source link

  • Duniya Ta Shaida Kokarin Sin Bisa Shirin Ci Gaban Tattalin Arziki Da Zamantakewar Al’Umma Na Shekaru Biyar-Biyar Karo Na 15

    [ad_1]

    An kammala taron majalisar NPC da CPPCC na 2026 cikin nasara, inda aka zartar da muhimman takardu, kamar na tsarin shirin ci gaban tattalin arziki da zamantakewar al’ummar Sin na shakaru biyar-biyar karo na 15, matakin da ya tabbatar da shirin a sabon zagaye. Wadannan manyan taruka 2 na Sin, ba wai kawai sun tanadi tsara aikin da Sin za ta aiwatar a nan gaba ba ne, har ma sun samar da alkibla ta samun wadata tare ga kasashen duniya, kuma kafofin yada labarai na kasa da kasa sun yaba da hakan sosai.

    Sin na amfani da shirin na shakaru biyar-biyar don rike makomarta mai kyau ta dogaro da karfin kai, tana kuma nacewa cikakken jagorancin jam’iyyar JKS, da tsare-tsare daga manyan fannoni a bangaren kimiyya, da mayar da kwarewar tsare-tsare zuwa doka, kana tana nuna fa’idodin tsari na tattara karfin kowa da kowa don gudanar da manyan ayyuka, wannan shi ne sirrin nasarar “tsarin Sin”.

    Har ila yau, Sin na mai da hankali kan samun ingantaccen ci gaba, tana kula da daidaiton karuwar adadi da ingancin ci gaba, kuma tana bunkasa sabon karfin samar da hajoji, da hidimomi masu karko, da kafa sabbin siffofin tattalin arziki na hikima, da kuma gaggauta karkata zuwa hanyar samun ci gaba ba tare da gurbata muhalli ba bisa dokar kare muhalli, da kuma gaggauta ci gaban tattalin arziki mai dorewa.

    Sin na ci gaba da inganta rayuwar jama’a, da mai da moriyar jama’a a gaban komai. Abubuwan dake shafar rayuwar jama’a a shirin karo na 15 ya wuce sulusi, wadanda suke mai da hankali kan kare lafiyar jama’a, da inganta tsarin inshorar zamantakewa da kiwon lafiya, da kuma inganta rayuwar jama’a.

    Sin na nacewa ga bude kofa da juriya, da samar da fa’idodin babbar kasuwa, da fadada bude kofa bisa manufofin kasa da kasa, ta yadda babbar kasuwar Sin za ta ci gaba da samar da damammaki ga duniya. Sin na tsayawa tsayin daka kan kare ra’ayin gudanar da harkokin duniya tsakanin mabambantan bangarori, da gaggauta gina kyakkyawar makomar bil Adam ta bai daya, wanda hakan ya sa ta zama amintaccen karfi mai inganci ga kwanciyar hankalin duniya. (Amina Xu)

    [ad_2]

    Source link

  • Ramadan: Lokutan Buda-Baki Da Sahur Na Azumi Na 24

    [ad_1]

    Mota Sahur (Fajr/Imsak) Iftar (Maghrib)
    Abuja 05:10 na safe 07:01 PM
    Idan 05:05 na safe 06:55 PM
    Kano 05:06 AM 07:00 PM
    Kaduna 05:10 na safe 07:03 PM
    Legas 05:24 AM 07:20 PM
    Maiduguri 05:01 AM 06:40 PM
    Sokoto 05:23 AM 07:13 PM
    Fatakwal 05:15 AM 07:02 PM

    [ad_2]

    Source link

  • Ministan Wajen Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Kawo Karshen Matakan Soji A Gabas Ta Tsakiya

    [ad_1]

    Ministan ma’aikatar harkokin wajen kasar Wang Yi, ya yi kira ga dukkanin sassa masu ruwa da tsaki a rikicin da ya barke a yankin gabas ta tsakiya, da su gaggauta dakatar da matakan soji a yankin, kana su himmatu wajen dakile kara tabarbarewar yanayin da ake ciki.

    Wang, ya yi kiran ne yayin tattaunawar da ya yi ta wayar tarho a jiya Alhamis, tare da takwaransa na Masar Badr Abdelatty, yana mai cewa tsawaitar tashin hankalin da ya barke zai haifar da karin illoli, da gurgunta tattalin arzikin yankin tare da illata tsaro. Ya ce Sin a shirye take ta yi aiki tare da Masar, da sauran kasashen yankin wajen tabbatar da zaman lafiya mai nagarta.

    A nasa bangare kuwa Badr Abdelatty, cewa ya yi Masar ta damu matuka da barkewar rikicin, ya kuma jinjinawa matsayar kasar Sin ta adalci, da aniyarta ta ci gaba da tuntuba da nufin yayyafawa wutar rikicin ruwa.

    A wani ci gaban kuma, Wang Yi ya zanta ta wayar tarho tare da takwaransa na Cuba Bruno Rodriguez, bisa bukatar hakan daga bangaren Cuba. Kuma sassan biyu sun amince da kara zurfafa gina dangantaka tsakanin sassan biyu. (Saminu Alhassan)

    [ad_2]

    Source link

  • Kotu ta ɗaure mutum 5 kan tone kabari a Gombe

    [ad_1]



    Babbar Kotun Jihar Gombe, ta yanke wa wasu maza biyar hukuncin ɗaurin shekaru daban-daban a gidan yari bayan an same su da laifin tone kabari da kuma wasu laifuka da suka shafi sihiri a garin Gadam, da ke Ƙaramar Hukumar Kwami.

    Alƙalin kotun, Abdulsalam Mohammed, ya yanke hukuncin ne bayan an gurfanar da mutanen.

    Daga cikin laifukan da ake tuhumar su har da haɗa kai wajen aikata laifi, lalata kabari, sata da kuma mallakar sassan jikin mutum ba bisa ƙa’ida ba.

    Waɗanda aka yanke wa hukuncin sun haɗa da Mohammed Isah (Chindo), Kawuni Sarki, Manu Saleh, Umar Jibrin (Daddy), da Adamu Nasiru.

    Akwai wani mutum mai suna Abdullahi Umar Dauda wanda har yanzu bai shiga hannun jami’an tsaro ba.

    Bayanin da aka gabatar a kotu ya nuna cewa a ranar 11 ga watan Satumban 2025, mutanen sun shiga maƙabartar Musulmai ta Gadam cikin dare.

    Sun tone kabarin wani mutum marigayi Malam Manu Wanzam.

    Ana zargin sun cire idanun mamacin domin amfani da su wajen yin sihiri.

    Lauyan gwamnati, Barista Ahmed Yakubu, ya shaida wa kotu cewa laifukan sun saɓa da dokar Penal Code.

    A lokacin shari’ar, wasu daga cikin waɗanda ake tuhuma sun amsa laifukan da aka karanta musu.

    Alƙalin kotun ya yanke wa Mohammed Isah da Kawuni Sarki hukuncin shekaru biyar a gidan yari.

    Manu Saleh da Umar Jibrin kuma za su yi shekaru biyu da watanni shida, yayin da Adamu Nasiru zai yi shekaru huɗu da watanni shida a gidan yari.

    Kotun ta kuma bayyana cewa za ta ci gaba da shari’a kan sauran mutanen da ake zargi da hannu a lamarin amma suka tsere.


    [ad_2]

    Source link

  • Yadda ‘Yan Boko Haram Suka Kashe Kwamandojin Soja 3 A Mako Daya

    [ad_1]

    Sojan Nijeriya sun rasa akalla manyan hafsoshin rundunar guda uku da ke kula da tashoshin ayyuka na gaba sakamakon hare-haren da Boko Haram da Kungiyar Islamic State West Africa Probince (ISWAP) suka kai a wurare daban-daban cikin kwana bakwai a Jihar Borno.

    Rashin rayukan na baya-bayan nan ya kawo adadin manyan hafsoshin da aka kashe cikin watanni uku zuwa guda bakwai, tare da wani brigediya janar daya.

    • Kudaden Shiga Na Masana’Antun Kimiya Da Fasaha Na Kasar Sin Ya Karu Da 16.1% a Watannin Janairu Da Fabrairun Wannan Shekara
    • Sojoji Sun Kashe ’Yan Ta’addan ISWAP 20 A Jihar Yobe

    Masu lura da lamuran tsaro sun ce hare-haren na baya-bayan nan sun nuna barazanar da ‘yan ta’adda ke ci gaba da haifarwa a Borno duk da ci gaba da ayyukan soji na rage karfinsu.

    A cikin ‘yan watannin da suka gabata, sojoji sun kara karfafa ayyukansu a wuraren da ke da hadari, ciki har da Dajin Sambisa, Yankin Timbuktu Triangle, Dutsen Mandara da Tafkin Chadi.

    Bayanan soji sun nuna cewa an kashe shugabannin ‘yan ta’adda da sojojinsu da dama yayin ayyukan da ake gudanarwa a fannoni da dama, tare da rusa sansanonin ‘yan ta’adda da yawa.

    Rahotannin kafofin yada labarai sun bayyana cewa manyan hafsoshin da aka kashe kwanan nan sun hada da Major U.I. Mairiga, wanda ke jagorantar tashar Mayenti; Laftanar Kanar Umar Faruk, kwamandan tashar Kukawa da Rundunar 101; da Lt-Col S.I. Iliyasu, wanda ya yi aiki a Konduga.

    A cikin watanni uku da suka gabata, an kuma ruwaito cewa manyan hafsoshin da ke Damasak, Kukawa da Bama sun rasa rayukansu yayin kare tashoshinsu.

    Bincike ya nuna cewa mafi yawan mutuwar ta faru ne yayin hare-hare a kan sansanonin soji ko kuma lokutan da ‘yan ta’adda suka kai farmaki yayin ayyukan tsarkakewa.

    Abin da ya faru na baya-bayan nan ya faru ne ranar Litinin, 9 ga Maris, lokacin da ‘yan ta’adda suka mamaye sansanin soja a Karamar Hukumar Kukawa ta Jihar Borno, inda suka kashe kwamandan sansanin, Laftanar Kanar Umar Faruk, tare da wasu sojoji da dama.

    Majiyoyin tsaro da na gida sun ce ‘yan ta’addan sun kai hari kan sansanin da misalin karfe 12 na tsakar dare.

    “Sun kutsa cikin garin daga hanyoyi da dama suka kai hari kan sansanin soji. Sun kore sojoji daga wajen, sun kone motocin soja kuma sun dauko makamai da alburusai,” in ji wata majiya daga tsaro.

    “Ba zan iya tabbatar da adadin wadanda suka rasa rayukansu ba, amma abin takaici mun rasa kwamandan sansanin ma,” in ji majiyar.

    Mai magana da yawun Hadin Gwiwar Sojoji (Arewa-Maso-Gabas), Operation Hadin Kai, Laftanar Kanar Sani Uba, ya tabbatar da cewa wani jarumin soja ya rasa ransa a harin, amma bai bayyana sunansa ba.

    A watan da ya gabata, ‘yan ta’adda sun kuma kai hari kan sansanin soja amma sojoji karkashin jagorancin marigayi Laftanar Kanar Umar Faruk sun fatattake su, inda aka kashe ‘yan ta’adda da dama.

    Ayyukan da ya yi a lokacin harin na baya sun samu yabo daga mazauna al’ummar, kuma an yi murnar hakan sosai a kafafen sada zumunta.

    A cikin wani bidiyo da ke yawo a Intanet, an ga dan majalisar da ke wakiltar Karamar Hukumar Kukawa a Majalisar Dokokin Jihar Borno, Karta Maina Ma’aji Lawan, yana murnar nasarar da aka samu a harin da ya gabata tare da sojoji.

    Sai dai dan majalisar, wanda ya tabbatar da harin na baya-bayan nan, ya ce an dawo da kwanciyar hankali a sauran sansanonin soja a yankin, duk da cewa sansanin da aka kai hari ya fada hannun ‘yan ta’adda.

    Sauran Hare-hare

    A ranar 1 ga Maris, 2026, wani babban jami’in soja, Manjo Umar Ibrahim Mairiga, ya rasu yayin da ‘yan ta’addan Boko Haram suka kai hari sansaninsa a Mayenti, Karamar Hukumar Bama.

    Wata majiyar tsaro ta ce jami’in ya yi kokari matuka wajen kare kansa daga harin, amma daga karshe ya rasa ransa.

    “Shugaban rundunar, Manjor U.I. Mairiga, ya yi gwagwarmaya sosai da ‘yan ta’addan, amma daga karshe an rinjaye shi bayan wasu daga cikin sojojinsa sun gudu zuwa daji.

    “Ya mutu a matsayin jarumin soja. Ya kashe da yawa daga cikinsu kafin a rinjaye shi. Lokacin da na iso don karin karfi, mun samu RPGs, makaman anti-aircraft kuma mun ga gawarwakin ‘yan Boko Haram da yawa,” in ji majiyar.

    Majiyar ta kara da cewa an tura jami’in zuwa sansanin ayyukan yaki kasa da watanni hudu da suka gabata bayan samun karin matsayi na musamman.

    Harin ya faru makonni bayan wasu sojoji da dama suka rasu a wani harin da aka kai sansanin soja a Jakana, Karamar Hukumar Kaga, inda ‘yan ta’adda suka kone motocin yaki kuma suka tafi da dimbin makamai.

    A ranar 6 ga Maris, Shugaban Rundunar 222 Battalion a Konduga,Laftanar Kanar S.I. Iliyasu, shima ya rasu tare da wasu sojoji yayin wani harin Boko Haram.

    An ce wasu ma’aikata da ke karkashin 21 Special Armoured Brigade ma sun rasu a harin, ciki har da wani mai mukamin Laftanar.

    Kafin wannan, a ranar 28 ga Janairu, ‘yan Boko Haram sun kai hari wani sansanin soja a Damasak, inda suka kashe sojoji bakwai, ciki har da babban jami’in sansanin, a wani tarkon da aka yi kusa da garin.

    An ce ‘yan ta’addan sun yi tarkon wata tawagar sintiri, inda suka kama babban jami’in kafin su kashe shi tare da wasu sojoji.

    A ranar 20 ga Oktoba, 2025, Sojan Nijeriya ya tabbatar da mutuwar Aliyu Saidu Paiko, babban jami’in 202 Battalion, da wasu sojoji yayin wata fafatawa da ‘yan ta’adda na Boko Haram a Karamar Hukumar Bama.

    Mai magana da yawun sojoji, Appolonia Anele, ta ce sojojin da ke karkashin 21 Special Armoured Brigade a karkashin Operation Hadin Kai sun yi kokari kafin su rinjayi ‘yan ta’addan a wani harin da aka kai a ranar 17 ga Oktoba a Kashimri, Karamar Hukumar Bama.

    A ranar Laraba da ta gabata, an ce an kashe sojoji goma sha hudu a wani hadin kai na harin da aka kai sansanin soja a Ngoshe, Karamar Hukumar Gwoza. Haka kuma, wani babban jami’in soja ya rasu, yayin da aka sace sama da mutum 100.

    Majiyoyi sun ce har yanzu ‘yan ta’addan suna mamaye garin Ngoshe, yayin da daruruwan mazauna suka tsere zuwa Pulka, wani gari da ke makwabtaka.

    A ranar Talata, ‘yan Boko Haram sun kuma kai hari Dalwa, wani gari da ke kusan kilomita 20 daga Maiduguri a Karamar Hukumar Konduga. “Wannan ya kamata ya zama babban abin damuwa idan aka yi la’akari da irin wahalar da ake sha wajen horar da jami’an soja,” in ji shi.

    Majiyoyi sun bayyana cewa mazauna sun yi kaura daga gidajensu yayin da wasu sassan al’ummar suka kone a harin.

    An ce al’ummar ta kwanan nan ne gwamnatin Jihar Borno ta sake maida su wurin zama.

    Harin ya biyo bayan hare-hare lokaci guda da aka kai kan sansanonin soja hudu a Konduga, Mainok, Jakana da Marte tsakanin karfe 10 na dare ranar Alhamis zuwa karfe 3 na safe ranar Juma’a.

    Tsokaci Kan Kisan Manyan Jami’an Soja.

    Yayin da yake tsokaci kan kisan manyan jami’an soja, masani kan harkar tsaro kuma tsohon Daraktan Hukumar Tsaron Kasa (DSS), Mike Ejiofor, ya bayyana lamarin a matsayin abin damuwa.

    “Wannan ya kamata ya zama babban abin damuwa idan ka yi la’akari da abin da ake bukata wajen horas da jami’an soja,” in ji shi.

    Ya bayyana cewa ‘yan ta’adda sau da yawa suna aiki ne ba bisa tsarin soja na al’ada ba, wanda hakan ke sanya da wahala a hango hare-harensu.

    Suna kai hari a ko’ina kuma ta kowace hanya. Amma dakarunmu tabbas za su shawo kan wannan,” in ji shi.

    Ejiofor ya ce ana bukatar matakai na gaggawa da na dogon lokaci don magance matsalolin tsaron kasar.

    “A matsayin mataki na gaggawa, ya kamata ‘yan kasa su bayar da sahihan bayanai ga hukumomin tsaro.

    “Ana bukatar muhimman gyare-gyare, ciki har da kafuwar ‘yansanda na jihohi,” in ji shi.

    Ya bayyana cewa kafa ‘yansanda na jihohi zai bukaci gyaran kundin tsarin mulki, amma ya ce ana iya kammala aikin cikin sauri idan Majalisar Kasa ta nuna jajircewar da ake bukata.

    “Wannan na daga cikin hanyoyi mafi tabbas na yakar ‘yan fashi, Boko Haram da ta’addanci,” in ji shi.

    Haka kuma ya nuna kyakkyawan fata cewa dakarun tsaro na samun ci gaba a yaki da ‘yan ta’adda.

    “Yayin da zabe ke karatowa, Boko Haram na kara hare-hare duk da ayyukan soja na ci gaba. Sau da yawa suna yin haka ne don nuna cewa har yanzu suna aiki,” in ji shi.

    Ya ce ‘yan ta’adda sau da yawa suna kai hari ne kan dakarun soja da fararen hula don haifar da tsoro da nuna cewa har yanzu suna nan. “Duk da haka, lokaci na zuwa, sojojinmu za su shawo kan matsalar,” in ji shi.

    Sojoji Sun Tabbatar da Hare-hare

    Dakarun Operation Hadin Kai sun tabbatar da hare-hare a ISWAP da Boko Haram suka kai kan wuraren soja da dama a jihohin Borno da Yobe.

    Hare-haren sun shafi al’ummomi da suka hada da Dalwa, Goniri, Kukawa da Mainok, da kuma matsugunan dakarun cikin dajin Sambisa.

    Tabbatarwar ta fito ne a cikin wata sanarwa da jami’in yada labarai na Rundunar Hadin Gwiwar Arewa-Maso-Gabas, Laftanar Kanar Sani Uba, ya fitar ranar Litinin.

    Sanarwar ta ce hare-haren da aka tsara sun faru tsakanin karfe 10 na dare ranar 8 ga Maris zuwa karfe 3 na safiya ranar 9 ga Maris, inda ‘yan ta’addan suka kai farmaki a lokaci guda daga fannoni da dama don mamaye matsugunan dakarun.

    A Yobe, majiyoyi sun ce ‘yan ta’addan sun kutsa cikin matsugunan Goniri a Karamar Hukumar Gujba ta Jihar Yobe kuma sun fafata da dakarun soja cikin tsananin yaki bayan sun karya iyakar kariya.

    Duk da tsananin hare-haren, dakarun sun yi amfani da dabarun tsaro mai karfi yayin da karin dakarun soja da sashin jiragen sama na Operation Hadin Kai suka ba da goyon baya a kan lokaci.

    Sojojin sun ce ‘yan ta’addan sun yi hijira bayan sun yi asarar rai da dama.

    Haka kuma, dakarun sun kwato makaman da ‘yan ta’addan suka bari yayin tserewa, ciki har da makaman PKT, bindigogi AK-47, bama-bamai masu harba roka, bam din morta da sauran alburusai.

    Sojojin sun ce wasu sassan iyakar Kariya a Goniri da Kukawa sun samu matsala ta dan lokaci, yayin da wasu gine-gine da motocin suka lalace a harin da ya faru.

    Duk da haka, rundunar ta ce duk wuraren suna karkashin kulawar dakarun Operation Hadin Kai.

    Sanarwar ta kara da cewa, dakarun, tare da goyon bayan jiragen sama, suna gudanar da ayyukan bibiyar wuraren harin, ciki har da kewaye da bincike a al’ummomin da ake zaton ‘yan ta’addan da suka raunana suna boya.

    “Abin takaici, wannan rikici ya yi sanadiyyar mutuwar wasu jaruman sojoji, ciki har da wani babban jami’i a Kukawa wanda ya nuna jajircewa domin kare kasa da kiyaye fararen hula,” in ji sanarwar.

    [ad_2]

    Source link

  • Wike Ya Bukaci Bangarorin PDP Su Hada Kai Kafin Zaben 2027

    [ad_1]

    Sakamakon gagarumin hukuncin da kotun daukaka kara ta yanke, wanda ya kara ruruta rikicin jam’iyyar adawa ta PDP, ministan babban birnin tarayya, Nyesom Wike, ya yi kira ga daukacin ‘ya’yan jam’iyyar, da su yi watsi da sabanin da ke tsakaninsu da kuma burinsu na sake gina jam’iyyar, gabanin babban zaben 2027.

    Da yake magana da manema labarai a Abuja ranar Litinin, Wike ya bayyana hukuncin da kotun daukaka karar ta yanke na tabbatar da hukuncin da babbar kotun tarayya ta yanke na soke babban taron jam’iyyar na kasa na 2025, a matsayin wani babban abu mai ma’ana ga PDP.

    • Sojoji Sun Kashe ’Yan Ta’addan ISWAP 20 A Jihar Yobe
    • ‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutum 15, Sun Jikkata Da Dama A Katsina

    Ya kuma bukaci bangarorin da ke rikici da juna da su kalli hukuncin ba a matsayin wani dalili na ci gaba da shari’a ba, a’a a matsayin wata dama ta sasantawa da sake sabunta jam’iyyar.

    “A gare ni, dama ce ga kowa ya sake dawowa, don ganin yadda za mu iya ceto jam’iyyar. Amma ga shi za a fara zaben fidda gwani daga watan Afrilu, yanzu kuma ga shi muna watan Maris.

    “Kowa ya bar son zuciyarsa, ka kuma bar abubuwan da kake so, ka dawo mu zauna mu sasanta, domin kuwa wannan dama ce muka sake samu,” in ji shi.

    Ministan, wanda bangarensa ke takun-saka da wasu shugabannin jam’iyyar, kan yadda aka gudanar da babban taron da ake takaddama a kai, ya yi gargadin cewa; garzayawa zuwa kotun koli, ba zai bai wa jam’iyyar dama tare da taimakon ta ba, a zabe mai zuwa.

    “Idan kun ce kuna son zuwa kotun koli, ku tuna za a yi zaben fidda gwani daga watan Afrilu zuwa na Mayu. Yanzu ku duba, a lokacin da kuka je kotun koli, kawai za ku cutar da kanku kawai, ku kuma cutar da jam’iyyar taku, wanda kuka ce kuna so kuma, wanda ba zai taimaka mana ba ne, “in ji shi.

    Wike ya jaddada cewa, shigar kotun ya zama dole, domin batun shugabancin jam’iyyar ya wuce gona da iri, ta hanyar saba ka’idojin tsarin mulki da kuma dokokin zabe.

    “Mutane da dama ba su fahimci inda matsalar take ba, ba batun shugabanci muke magana ba, idan kana maganar shugabanci, yanzu kana magana ne a kan harkokin cikin gida.

    “Amma lokacin da kuka ce kuna karya kundin tsarin mulki, kuna karya dokar zabe, kuna karya ka’idojin hukumar zabe da kuma kundin tsarin mulkin jam’iyyarku, wannan ba ya cikin harkokin cikin gida na jam’iyya, dole ne kotu ta tsoma baki,” in ji shi.

    Ministan babban birnin tarayya Abuja, ya bayyana gamsuwarsa da matakin da bangaren shari’a ya dauka, inda ya bayyana Juma’a a matsayin daya daga cikin ranakun farin ciki da ya samu a rayuwarsa.

    Ya kara da cewa, “Dole ne a koda-yaushe, mu bi ka’ida, a matsayinmu na jam’iyyar adawa, bai kamata mu ki amincewa da hukuncin da aka yi ba.

    Wike ya kuma yi amfani da damar wajen nuna mahimmancin jam’iyyar PDP a matsayin dandalin adawa na farko na kasar, inda ya bayyana sauran kananan jam’iyyu da cewa, ba su da wani tasiri.

    Da yake yin karin haske kan makomar shugabancin jam’iyyar, Wike ya bayyana cewa; kwamitin riko na jam’iyyar PDP, wanda aka kafa bayan karewar wa’adin jami’an da suka gabata, sun ne halastattun shugabannin da aka sani.

    Ya sanar da cewa, tuni kwamitin ya samu amincewar gudanar da sabon babban taron kasa a ranakun 29 da 30 ga watan Maris.


    [ad_2]

    Source link

  • Ƙarancin gas na iya ta’azzara rashin wuta a Najeriya

    [ad_1]



    Rashin wutar lantarki a Najeriya na iya ƙara ƙamari yayin da kamfanonin da ke samar da gas suka rage adadin gas ɗin da suke bai wa tashoshin samar da wuta masu amfani da gas.

    Tashoshin ne ke samar da mafi yawan wutar lantarkin da ake amfani da ita a ƙasar.

    Hukumar da ke kula da sarrafa wutar lantarki (NISO), ta ce tashoshin wutar lantarki na buƙatar adadin yawan gas miliyan 1,629 a kullum domin su yi aiki yadda ya kamata.

    Amma zuwa ranar 23 ga watan Fabrairu, 2026, adadin gas da ake samu ya kai kimanin miliyan 692 a kowace rana, wato ƙasa da rabin abin da ake buƙata.

    Wannan ya haifar da yawaitar katsewar wuta a jihohi da dama tare da shafar harkokin kasuwanci da rayuwar jama’a.

    Babbar Daraktar Ƙungiyar Kamfanonin Samar da Wutar Lantarki, Dokta Joy Ogaji, ta ce matsalar na da alaƙa da bashin da ya yi wa ɓangaren wutar lantarki ƙatutu.

    Ta bayyana cewa gwamnati na bin kamfanonin da ke samar da wutar lantarki bashin kusan Naira tiriliyan 6.8, mafi yawansa yana da alaƙa da tashoshin wutar lantarki masu amfani da gas.

    Ta ce: “An kafa kamfanin Kamfanin Sayen da Sayar da Wutar Lantarki na Najeriya domin ya riƙa sayen wuta daga kamfanonin samar da wuta sannan ya biya su gaba ɗaya.

    “Amma tun daga 2013 har zuwa yanzu ba su taɓa biyan cikakken kuɗin da ake bin su ba, wanda hakan ya sa bashin ya kai kusan Naira tiriliyan 6.8.”

    Ogaji ta ƙara da cewa kamfanonin da ke samar da gas yanzu sun fara ƙin bayar da gas sai an biya su kuɗinsu nan take, wanda hakan ka iya ƙara rage samar da wutar lantarkin da ake samu.

    Ta ce: “Masu samar da gas sun faɗa mana cewa idan muna buƙatar gas dole mu biya kuɗin da ake bi tun da farko. Muna binsu kuɗi da yawa, kuma wannan na ɗaya daga cikin manyan dalilan da ya sa ake fama da rashin wuta a Najeriya.”

    A sassa daban-daban na ƙasar, jama’a da ’yan kasuwa sun riga sun fara fuskantar koma baya sakamakon matsalar.

    Kamfanonin rarraba wutar lantarki da dama sun fara raba wuta na ’yan sa’o’i, wato raba wutar lantarki ta yadda wasu yankuna za su riƙa samun wuta na ’yan sa’o’i ko ma su kwashe kwanaki ba tare da wuta ba.

    A Jihar Legas, wasu mazauna jihar sun fito zanga-zanga saboda fama da rashin wuta da suke yi.

    Wata mazauniya jihar, Misis Oyinlola, ta ce matsalar ta jefa iyalinta cikin damuwa.

    Ta ce: “Yanzu kusan makonni uku kenan ba mu samu wuta mai kyau ba. Ba ma iya caja wayoyinmu, abincin da ke cikin firiji yana lalacewa, kuma yara suna shan wahala saboda zafi.”

    Haka kuma ƙananan ’yan kasuwa suna fama da matsalar.

    A Kano, wani sana’ar walda mai suna Musa Abdullahi, ya ce yanzu yana kashe dubbai a kullum wajen sayen fetur domin kunna janareta saboda rashin wutar lantarki.

    Kamfanonin rarraba wutar lantarki sun nemi afuwar jama’a, inda suka ce matsalar ta samo asali ne daga ƙarancin gas da sauran ƙalubale da ke hana tashoshin wutar lantarki samar da isasshiyar wuta a faɗin ƙasar.


    [ad_2]

    Source link