Category: Latest News

  • Wane ne Ali Larijani, babban jami’in tsaron Iran da Isra’ila ta kashe?

    [ad_1]



    A ranar Talata, 17 ga watan Maris, Ministan Tsaron Isra’ila Israel Katz, ya iƙirarin cewa an kashe Ali Larijani, daya daga cikin manyan shugabannin Iran, tare da Janar Gholamréza Soleimani, kwamandan rundunar Bassidj, bayan hare-haren da sojojin ƙasarsa suka kai a cikin daren jiya a Iran.

    A cikin wani saƙon bidiyo da ya wallafa Katz ya bayyana cewa shugaban rundunar sojin Isra’ila ya tabbatar masa da mutuwar Larijani, wanda shi ne sakataren Majalisar Tsaron Iran, da kuma Soleimani, shugaban rundunar Bassidj, wadda ake kallon ta a matsayin hukumar da ake amfani da ita don murƙushe.

    Tun bayan mutuwar Khamenei, Larijani ya kasance ɗaya daga cikin manyan ƙusoshi a gwamnatin Iran, kuma ana ɗaukar sa a matsayin wanda ke yanke manyan shawarwari tare da jagorantar hare-hare da ake kai wa Isra’ila da ƙasashen yankin Gulf.

    Sai dai hukumomin Iran ba su gaskata ko kuma musanta wannan labari ba, hasali ma an wallafa wata wasiƙa daga shufukan Ali Larijani na X da kuma Instagram domin girmama sojojin Iran da suka mutu a wannan yaƙi.

    Amma da yammacin nan, mahukuntan ƙasar Iran sun tabbatar da mutuwar Larijani.

    Wane ne Ali Larijani?

    Ali Larijani ya kasance ɗaya daga cikin fitattun ’yan siyasar Iran, wanda aka san shi da matsakaicin ra’ayi da kuma ƙwarewa a harkokin gwamnati.

    Sunansa Ali Ardeshir Larijani kuma an haife shi a shekarar 1958 a garin Najaf na ƙasar Iraƙi. Sunan mahaifinsa Ayatollah Hashem Amoli Larijani.

    Ya fito daga babban gida daga iyali mai ƙarfi daga yankin Amol. Mujallar Time ta taɓa kwatanta danginsu da “Kennedys na Iran” saboda tasirinsu a siyasa.

    Ya yi karatu a fannin lissafi da kimiyyar kwamfuta, sannan ya kammala digiri na uku a falsafar Yammacin Duniya, inda ya mayar da hankali kan falsafar Immanuel Kant.

    Bayan juyin juya halin Musulunci na 1979, ya shiga rundunar juyin-juya hali ta IRGC sannan ya riƙe muƙamai daban-daban a gwamnati, ciki har da ministan al’adu da kuma shugaban gidan talabijin na ƙasa IRIB.

    Ya kuma zama sakataren majalisar tsaron ƙasa da babban mai tattaunawa kan shirin nukiliyar Iran a 2005, kafin daga bisani ya zama kakakin majalisar dokoki na tsawon wa’adi uku, inda ya taka muhimmiyar rawa wajen amincewa da yarjejeniyar nukiliya ta 2015.

    A watan Agustan 2025 ne ya koma matsayin sakataren majalisar tsaron ƙasa, inda ya sake zama ɗaya daga cikin jiga-jigan shugabannin Iran.

    Me zai faru idan kisan Larijani ya tabbata?

    Idan har Iran ta tabbatar da kisan Ali Larijani, hakan zai zama ɗaya daga cikin manyan kashe-kashen shugabanni mafi tasiri tun bayan fara yaƙin da Amurka da Isra’ila suka ƙaddamar, wanda ya haɗa da harin da ya kashe marigayi jagoran addini Ayatollah Ali Khamenei.

    Bayan rasuwar Khamenei, an ce an naɗa ɗansa a matsayin sabon jagoran ƙasar, sai dai rahotannin Isra’ila na cewa sabon jagoran ya samu raunuka, kuma Larijani ne ke taka rawar jagoranci a matsayin babban jami’in tsaro.

    Masana na ganin cewa kashe Larijani, idan ya tabbata, zai bai wa ƙasashen waje wahalar samun wanda za su tattauna da shi daga cikin manyan shugabannin Iran, musamman a wannan lokacin rikici.

    Sai dai duk da haka, kisan nasa—ko da ya tabbata—ba yana nufin rugujewar tsarin mulkin Iran gaba ɗaya ba.

    Tsarin mulkin ƙasar ya dogara ne da cibiyoyi da dama, ciki har da rundunar juyin-juya hali ta Islamic Revolutionary Guard Corps (IRGC) da sauran hukumomin tsaro, waɗanda ke ci gaba da aiki duk da asarar manyan shugabanni.

    A ɓangaren Isra’ila kuwa, za a ɗauki mutuwarsa a matsayin babbar nasara ta dabarun yaƙi, kasancewar zai rage ƙarfin jagoranci da haɗin kai a ɓangaren Iran.

    Gani na ƙarshe da aka yi wa Larijani

    A ranar Juma’ar da ta gabata an ga Larijani a bainar jama’a a yayin da yake halartar gangamin Ranar Qudus a tsakiyar Tehran.

    Larijani ya kasance cikin manyan jami’an gwamnati da suka yi tattaki a gangamin na shekara-shekara, wanda ake gudanarwa domin nuna goyon baya ga Falasɗinawa.

    Bayyanar Larijani da shugaban ƙasar, Masoud Pezeshkian da ministan harkokin waje, Abbas Aragchi a jerin zanga-zangar sun musanta iƙrarin da shugaban Amurka, Donald Trump ya yi cewa jagororin ƙasar Iran suna gudu su ɓuya saboda tsoron hare-haren.

    Yayin da yake magana da kafafen yaɗa labaran gwamnati na Iran, ya bayyana harin bam da ya faru a lokacin gangamin a matsayin alamar “rauni da firgici” daga abokan gaban ƙasar.

    “Waɗannan hare-haren sun fito ne daga matsorata masu rauni. Wanda yake da ƙarfi ba zai kai hari kan masu zanga-zanga ba. Saboda haka wannan a bayyane take sun gaza,” in ji shi.

    Haka kuma ya soki shugaban Amurka, Donald Trump, yana mai cewa bai fahimci irin ƙarfin zuciya da jajircewar al’ummar Iran ba.

    “Trump bai fahimci cewa mutanen Iran ƙasa ce mai jarumtaka da ƙarfi da jajircewa ba. Duk wani ƙarin matsin lamba, zai ƙara wa al’ummar Iran ƙarfin zuciya,” in ji Larijani.

    Bayyanarsa a wannan gangami na zuwa ne kwanaki kaɗan kafin iƙirarin da Isra’ila ta yi cewa an kashe shi.

    Larijani ya nemi haɗin kan ƙasashen Musulmi a yaƙin Iran

    A bayan nan kuma Ali Larijani, ya bayyana damuwa tare da aika saƙo mai ɗauke da gargaɗi da kuma kira ga ƙasashen Musulmi, yana mai jaddada cewa ƙasarsa ba za ta ja da baya ba a yaƙin da take yi da Amurka da Isra’ila.

    A cikin saƙon da ya fitar, Larijani ya yi ƙoƙarin jan hankali ƙasashe da yawancinsu Musulmai ne, yana mai cewa, ban da kaɗan daga cikinsu, yawancin ƙasashen Musulmi sun gaza goyon bayan Iran kan abin da ya kira “muguwar hari na yaudara.”

    Ya ambato maganar Annabi Muhammad (SAW) inda ya ce: “Duk wanda ya ji ana kiran ‘Ya Musulmi!’ bai amsa ba, to ba Musulmi ba ne,” yana mai tambayar ko matakin wasu gwamnatocin Musulmi bai saɓa da wannan koyarwa ba.

    Larijani ya kuma kare hare-haren da Iran ke kaiwa a yankin, duk da cewa ƙasashen yankin Gulf na kallon hakan a matsayin keta huruminsu, inda ya nuna cewa babu tsaka-tsaki a wannan rikici.

    “Wane ɓangare kuke?” in ji shi, yana mai aika wani saƙo na gargaɗi ga ƙasashen da ke ƙoƙarin kaucewa rikicin.

    Sai dai ya jaddada cewa Iran ba ta neman mamaye maƙwabtan ta, yana mai cewa haɗin kan al’ummar Musulmi zai iya tabbatar da tsaro, ci gaba da ’yancin kai ga dukkan ƙasashe idan aka cimma shi yadda ya kamata.


    [ad_2]

    Source link

  • Kasar Sin Na Son Taimaka Wa Habasha Sake Gina Yankunan Da Ibtila’in Zaizayar Kasa Ya Shafa

    [ad_1]

    Rahotannin sun ruwaito cewa, mamakon ruwan sama da aka yi a kudancin kasar Habasha ya janyo ibtila’in zaizayar kasa tare da zabtarewar laka, al’amarin da ya yi ajalin mutane akalla 100, kuma akwai kimanin 60 da har yanzu ba a ji duriyarsu ba, kana, ya tilasta wa mutane kusan 3500 barin matsugunansu. Gwamnatin kasar ta sanar da zaman makoki daga ranar 14 zuwa 16 ga watan Maris da muke ciki, tare da saukar da tuta zuwa rabin sanda a duk fadin kasar.

    Game da wannan batu, mai magana da yawun ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin, Lin Jian ya bayyana a yau Talata 17 ga wata cewa, kasarsa ta yi alhinin wadanda suka rasa rayukansu, tare da jajanta wa iyalan mamatan. Kuma Sin tana da yakinin cewa, a karkashin jagorancin gwamnatin Habasha, mutanen da ibtila’in ya shafa za su iya shawo kan lamarin tare da sake gina matsugunansu. Haka zalika, kasar Sin na son samar da taimako gwargwadon iyawarta ga mutanen da ibtila’in ya shafa wajen sake gina matsugunansu, bisa bukatun kasar Habasha. (Murtala Zhang)

    [ad_2]

    Source link

  • Tinubu Ya Bai Wa Masu Riƙe Da Muƙamai Da Ke Son Yin Takara Wa’adin Yin Murabus

    [ad_1]

    Shugaban ƙasa Bola Tinubu ya umarci duk masu muƙaman gwamnati da ke son tsayawa takara a zaɓen 2027 su ajiye muƙamansu kafin ranar 31 ga watan Maris, 2026.

    An bayyana hakan ne a wata sanarwa daga Ofishin Sakataren Gwamnatin Tarayya, wadda George Akume ya sanya wa hannu.

    • Gwamnatin Tarayya Ta Ayyana Ranakun Hutun Ƙaramar Salla
    • El-Rufai Ya Zargi ICPC Da DSS Kan Tsare Shi Ba Bisa Ƙa’ida Ba Da Neman Ya Yi Ritaya Daga Siyasa

    Umarnin ya biyo bayan dokokin zaɓe da jadawalin zaɓe da INEC ta fitar.

    Umarnin ya shafi ministoci, masu bai wa shugaban ƙasa shawara, mataimaka na musamman, shugabannin hukumomi da sauran masu muƙaman siyasa da ke son tsayawa takara.

    Dukkanin waɗanda abin ya shafa dole ne su miƙa takardun murabus ɗinsu ta hannun ofishin sakataren Gwamnatin Tarayya kafin wa’adin da aka ƙayyade.

    Tinubu ya ce an ɗauki wannan mataki ne domin tabbatar da adalci, bin doka, da kuma bai wa kowa damar yin takara cikin gaskiya.

    [ad_2]

    Source link

  • Atiku ya soki tafiyar Tinubu Birtaniya ana tsaka da alhinin harin Maiduguri

    [ad_1]



    Tsohon mataimakin shugaban ƙasa, Atiku Abubakar, ya soki tafiyar shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu, zuwa Birtaniya, a daidai lokacin da aka kashe mutane a harin ta’addanci a Maiduguri, babban birnin Jihar Borno.

    A cikin wata sanarwa da ya wallafa, Atiku ya bayyana baƙin ciki kan harin, yana mai cewa bai dace shugaban na Najeriya ya fice daga ƙasar ba yayin da ake alhinin mutuwar jama’a.

    Ya zargi gwamnatin da rashin bai wa tsaron jama’a fifiko, yana mai cewa sojoji na fuskantar ƙalubale na tsoffin makamai, yayin da hare-haren ta’addanci ke ci gaba da ƙara tsananta.

    Atiku ya kuma ce, ya kamata Sarki Charles III wanda Tinubu zai kaiwa ziyara ya san halin da Najeriya ke ciki, inda a cewarsa ana binne waɗanda aka kashe, yayin da shugaban ƙasa ke gudanar da ziyarar aiki a ƙasarsa.

    Ya ƙara da cewa, duk da umarnin da aka bai wa jami’an tsaro, hare-haren ‘yan ƙunar baƙin wake na ci gaba, yana mai cewa hakan ya nuna akwai buƙatar sake duba dabarun yaƙi da ta’addanci.

    Tsohon mataimakin shugaban ƙasar ya zargi gwamnatin da mayar da sukar ta a matsayin cin amanar ƙasa, yana mai cewa hakan na hana a yi gyara mai ma’ana.

    Atiku ya shaida wa gwamnati mai ci cewar ba za ta yi kamfen na zaɓen shekarar 2027 a kan kaburburan jama’a ba, waɗanda ta gaza kare rayukan su, inda ya nanata buƙatar gwamnati ta mayar da hankali wajen kare rayuka da dukiyoyin al’umma.

    Duk da sukar da ya yi, Atiku ya jinjina wa jami’an tsaro da ke sadaukar da rayuwarsu wajen kare ƙasar.


    [ad_2]

    Source link

  • Gwamnatin Tarayya Ta Ayyana Ranakun Hutun Ƙaramar Salla

    [ad_1]

    Gwamnatin Tarayya ta ayyana ranar Alhamis, 19 ga watan Maris da Juma’a, 20 ga watan Maris, 2026 a matsayin ranakun hutu domin bikin ƙaramar salla, idan an kammala watan Ramadan.

    Ministan Harkokin Cikin Gida, Olubunmi Tunji-Ojo ne, ya sanar da hakan a madadin gwamnati cikin wata sanarwa da ya fitar a ranar Talata.

    • El-Rufai Ya Zargi ICPC Da DSS Kan Tsare Shi Ba Bisa Ƙa’ida Ba Da Neman Ya Yi Ritaya Daga Siyasa
    • Harin Maiduguri: Fadar Shugaban Ƙasa Ta Ƙaryata Saƙon Trump A Kan Tinubu

    Ya taya al’ummar Musulmi murna bisa kammala azumin watan Ramadan, tare da ƙarfafa su da su ci gaba da yin riƙo da halaye na gari kamar soyayya, taimako, zaman lafiya, haƙuri da sadaukarwa.

    Ministan ya kuma buƙaci dukkanin ’yan Nujeriya da su yi amfani da lokacin wajen yi wa ƙasa addu’ar zaman lafiya, haɗin kai da ci gaba.

    Ya ƙarfafi jama’a su yi bukukuwan cikin natsuwa tare da taimaka wa mabuƙata.

    Ya ƙara da cewa gwamnati na ci gaba da ƙoƙarin tabbatar da haɗin kai da zaman lafiya a tsakanin ’yan Nijeriya.

    [ad_2]

    Source link

  • Harin ’yan bindiga ya yi ajalin mutum 15 a Katsina

    [ad_1]



    ’Yan bindiga da ake zargin masu satar dabbobi ne sun kashe mutane 15 tare da jikkata wasu da dama a hare-haren da suka kai a ƙauyukan Kadobe da Falale da ke Ƙaramar Hukumar Jibiya a Jihar Katsina.

    Rahotanni sun ce maharan, waɗanda ba a tantance adadinsu ba, sun kai harin ne da rana tsaka a wannan Talatar, inda suka riƙa harbi kan mai uwa da wabi.

    An ce harin na iya kasancewa na ramuwar gayya, bayan zargin cewa wasu ’yan sa-kai a yankin sun kai wa maharan hari a baya.

    Kwamishinan tsaro da harkokin cikin gida na jihar, Nasiru Ma’azu Danmusa, ya bayyana cewa jami’an tsaro sun garzaya wurin domin ɗaukar matakin gaggawa, sai dai bai tabbatar da kama kowa daga cikin maharan ba a lokacin.

    Sai dai kakakin rundunar ’yan sandan jihar, Abubakar Sadiq Aliyu, ya ce an samu nasarar cafke mutane uku da ake zargin suna da hannu a harin, waɗanda aka ce sun fito daga birnin Gusau na Jihar Zamfara.

    Ƙaramar Hukumar Jibiya na daga cikin yankunan da aka taɓa ƙulla yarjejeniyar sulhu da ’yan bindiga a baya ƙarƙashin jagorancin Audu Lankai, lamarin da aka samu zaman lafiya na ɗan lokaci.

    Wani mazaunin yankin, Alhaji Salisu, ya ce tun bayan sulhun ba a sake samun irin wannan mummunan hari ba, lamarin da ya sa jama’a ke tambayar ko sulhun na neman rushewa ko kuma wasu sabbin ƙungiyoyi ne ke ƙoƙarin tada zaune tsaye.

    Harin na zuwa ne a daidai lokacin da ake ci gaba da fuskantar ƙalubalen tsaro a yankunan Arewa maso Yammacin Najeriya.


    [ad_2]

    Source link

  • Sin Ta Fadada Yawan Biranen Gwajin Cinikayyar Kasa Da Kasa A 2026

    [ad_1]

    Babbar hukumar kwastam ta kasar Sin ta ce a shekarar nan ta 2026, gwamnatin kasar Sin ta fadada adadin biranen gudanar da gwajin cinikayyar kasa da kasa zuwa 45 daga 25 da ake da su a shekarar 2025.

    Da take tsokaci dangane da hakan yayin taron masu ruwa da tsaki a jiya Litinin, shugabar hukumar Sun Meijun ta ce, birane 20 da aka kara cikin shirin sun hada da Hohhot, da Changchun, da Suzhou, da Jinhua, da Quanzhou. Sauran su ne Nanchang, da Yantai, da Wuhan, da Changsha, da Zhuhai, da Nanning, da Kunming da kuma Xi’an.

    Sun ta ce, karkashin wannan manufa, za a kaddamar da sabbin matakai, wadanda za su karkata ga daga matsayin cinikayyar hajoji, da fadada cinikayyar hidimomi, da ingiza ci gaban cinikayyar dijital da hajoji marasa gurbata yanayi.

    Kazalika, matakan za su kunshi na aiwatar da kirkire-kirkire a ayyukan kwastam, a fannin sanya ido ga ayyukan tantance kayayyakin shige da fice, da inganta hidimomi ga sabbin fannonin cinikayyar waje, da kyautata hidimomin safarar hajoji tsakanin kan iyakoki, da gina tashoshi na zamani, da inganta mizani zuwa matakin kasa da kasa, da kuma kyautata goya baya ga kamfanoni. (Mai Fassara: Saminu Alhassan)

    [ad_2]

    Source link

  • El-Rufai Ya Zargi ICPC Da DSS Kan Tsare Shi Ba Bisa Ƙa’ida Ba Da Neman Ya Yi Ritaya Daga Siyasa

    [ad_1]

    Tsohon gwamnan Jihar Kaduna, Nasir El-Rufai, ya shigar da ƙara a gaban kotun majistare da ke Abuja, inda yake zargin jami’an ICPC da DSS da tsare shi ba bisa ƙa’ida ba tare da ƙoƙarin tilasta masa yin ritaya daga siyasa.

    A cikin ƙarar, ya ambaci shugaban ICPC, Musa Adamu Aliyu, da Darakta Janar na DSS, Adeola Oluwatosin Ajayi, tare da wasu jami’ai.

    • Ramadan: Lokutan Buda-Baki Da Sahur Na Azumi Na 27
    • Harin Maiduguri: Fadar Shugaban Ƙasa Ta Ƙaryata Saƙon Trump A Kan Tinubu

    El-Rufai ya ce an tsare shi tun ranar 18 ga watan Fabrairu, 2026, ba tare da gurfanar da shi a gaban kotu ba.

    Ya bayyana cewa tun farko ya je ofishin EFCC a ranar 16 ga watan Fabrairu, inda ya bayar da bayani kuma ya haɗa kai da masu bincike, sannan aka ba da belinsa.

    Sai dai ya ce jami’an DSS sun ɗauke shi daga hannun EFCC suka kai shi wajen ICPC kafin ya cika sharuɗan belinsa.

    Ya kuma ce umarnin kotun da aka yi amfani da shi wajen tsare shi ba shi da inganci, kuma ya ƙare a ranar 4 ga watan Maris, 2026.

    Tun daga lokacin, ya ce babu wata hujja ta doka da ta bayar da damae tsare shi.

    Har ila yau, El-Rufai ya zargi jami’an ICPC cewa ba za su sake shi ba sai ya daina siyasa, abin da ya ce ya saɓa wa haƙƙoƙinsa na kundin tsarin mulki.

    Ya ƙara da cewa an hana shi samun cikakkiyar damar ganin iyalansa, lauyoyinsa da likitocinsa.

    A ƙarar, ya zargi jami’an da suka tsare shi ba bisa ƙa’ida ba da kuma taƙaita masa ‘yancin zirga-zirga, inda yake roƙon kotu ta ɗauki mataki.

    Har zuwa lokacin haɗa wannan rahoto, ICPC da DSS ba su yi wata magana kan zargin ba.

    [ad_2]

    Source link

  • Gwamnatin Tarayya ta ayyana ranakun hutun ƙaramar sallah

    [ad_1]



    Gwamnatin Tarayya ta ayyana ranakun Alhamis da Juma’a, wato 19 da kuma 20 ga watan Maris a matsayin ranakun hutun ƙaramar Sallah a Najeriya.

    Ministan Harkokin Cikin Gida, Olubunmi Tunji-Ojo ne ya bayyana haka a wata sanarwa da babbar Sakatariyar ma’aikatarsa, Dokta Magdalene Ajani ta fitar a ranar Talata.

    Sanarwar tana kuma yi wa Musulmi murnar kammala azumin watan Ramadan da zagayowar bikin ƙaramar sallah ta Eid-el-Fitr.

    Ya yi kira ga Musulmi da su kwaikwayi halayen Manzon Allah S.A.W da suka ƙunshin kyautatawa, nuna soyayya, haƙuri, juriya da kuma zaman lafiya.

    Kazalika, ya yi kira ga ɗaukacin ‘yan Najeriya da su yi amfani da lokacin bukukuwan domin yi wa ƙasar addu’ar samun ci gaba da zaman lafiya, haɗin kai, da wadata.

    Ministan ya ƙarfafa gwiwar ’yan kasa da su yi murna mai ma’ana cikin nutsuwa tare da sadar da ayyukan alheri ga mabuƙata a cikin al’umma.

    Ya ba da tabbacin cewa Gwamnatin Tarayya ta duƙufa wajen samar da haɗin kan ƙasa da zaman lafiya a tsakanin ‘yan Nijeriya baki ɗaya.


    [ad_2]

    Source link

  • Ramadan: Lokutan Buda-Baki Da Sahur Na Azumi Na 27

    [ad_1]

    Mota Sahur (Fajr/Imsak) Iftar (Maghrib)
    Abuja 05:06 AM 07:05 PM
    Idan 05:01 AM 06:59 PM
    Kano 05:02 AM 07:04 PM
    Kaduna 05:06 AM 07:07 PM
    Legas 05:20 na safe 07:24 PM
    Maiduguri 04:57 AM 06:44 PM
    Sokoto 05:19 AM 07:17 PM
    Fatakwal 05:11 AM 07:06 PM

    [ad_2]

    Source link