Category: Latest News

  • El-Rufai ya shafe kwanaki 30 a tsare ba a gurfanar da shi ba

    [ad_1]



    Wata guda bayan da Hukumar yaƙi da cin da hanci da rashawa ta ICPC  ta tsare tsohon gwamnan jihar Kaduna, Nasir El-Rufai, har yanzu ba a gurfanar da shi a gaban kowace kotu ba, kamar yadda jaridar Daily Trust ta ruwaito.

    Wata guda bayan daHukumar yaƙi da cin da hanci da rashawa ta ICPC  ta tsare tsohon gwamnan jihar Kaduna, Nasir El-Rufai, har yanzu ba a gurfanar da shi a gaban kowace kotu ba, kamar yadda jaridar Daily Trust ta ruwaito.

    Tun da farko, El-Rufai ya shafe dare biyu a hannun Hukumar EFCC kan zargin almundahanar kuɗi lokacin yana gwamna, kafin jami’an tsaro na farin kaya (DSS) su tafi da shi, sannan daga baya aka miƙa shi ga Hukumar ICPC.

    A ranar 16 ga Fabrairu, tsohon Gwamnan ya amsa gayyatar da EFCC ta yi masa, inda jami’an bincike suka tuhume shi. Wannan ya biyo bayan gazawar jami’an tsaro wajen kama shi a filin jirgin saman Abuja lokacin da ya dawo daga ƙasar Masar.

    Abin da ya faru a kotu

    Lauyoyi sun bayyana cewa, kodayake kotu tana da ikon tsawaita lokacin tsare mutum, yin hakan ba tare da umarnin kotu ba ya saɓa wa doka a sashen 293 zuwa 296 na Dokar Shari’ar Manyan Laifuka (ACJA).

    Rahoton Daily Trust ya nuna cewa, ICPC ta samu umarnin tsare shi na kwanaki 14 daga wata Kotun Majistare da ke Bwari, Abuja, a ranar 19 ga Fabrairu, wanda aka sake sabuntawa.

    Sai dai lauyoyin El-Rufai sun shigar da buƙatar ƙalubalantar tsawaita tsare shi, inda suka bayyana hujjoji da dama waɗanda aka sanya jiya a matsayin ranar yanke hukunci kansu.

    Ana sa ran Alƙalin Majistare, Okechukwu Akweke zai yanke hukunci a ranar 19 ga Maris.

    A cikin buƙatar da aka shigar, El-Rufai ya yi zargin cewa jami’an ICPC sun buƙaci ya janye daga harkokin siyasa a matsayin sharaɗin sakin sa, inda ya bayyana hakan a matsayin take haƙƙinsa na kundin tsarin mulki.

    A cewar takardun ƙarar, ya fara kai kansa ga EFCC ne a ranar 16 ga Fabrairu inda aka ba shi beli, amma daga baya DSS ta kama shi ta miƙa shi ga ICPC ba tare da wata ƙwaƙƙwarar hujja ta shari’a ba, wanda hakan ya kai ga tsare shi ba bisa ƙa’ida ba.

    Karar ta zargi manyan jami’ai, ciki har da shugaban ICPC da Darakta Janar na DSS, da tsare shi ba tare da haƙƙi ba. Lauyoyinsa sun kuma kafa hujjar cewa, umarnin tsare shi ba shi da inganci kuma lokacin tsare shi ya wuce kima ba tare da wata hujja ba.

    Duk da haka, El-Rufai ya yi iƙirarin cewa an hana shi sadarwa da kowa, ciki har da iyalansa, lauyoyinsa, da kuma samun kulawar likita.

    Kararrakin da ake yi ne suka dakatar da mu – ICPC

    Da yake magana da ɗaya daga cikin wakilanmu a daren jiya, wani babban jami’i a ICPC ya bayyana cewa ƙararrakin da aka shigar a kan hukumar ne suka jinkirta gurfanar da shi. Ya ce dole ne a janye dukkan umarnin kotu da ke adawa da ICPC kafin hukumar ta iya gurfanar da tsohon gwamnan.

    “El-Rufai ne da kansa yake jinkirta gurfanar da shi. Ya shigar da ƙara daban-daban a kan hukumar. Saboda haka, wasu daga cikin waɗannan ƙararrakin ya kamata a janye su kafin mu ci gaba bin matakan shari’a,” in ji jami’in.


    [ad_2]

    Source link

  • El-Rufai ya shafe kwanaki 30 a tsare ba tare an gurfanar da shi ba

    [ad_1]



    Wata guda bayan daHukumar yaƙi da cin da hanci da rashawa ta ICPC  ta tsare tsohon gwamnan jihar Kaduna, Nasir El-Rufai, har yanzu ba a gurfanar da shi a gaban kowace kotu ba, kamar yadda jaridar Daily Trust ta ruwaito.

    Wata guda bayan daHukumar yaƙi da cin da hanci da rashawa ta ICPC  ta tsare tsohon gwamnan jihar Kaduna, Nasir El-Rufai, har yanzu ba a gurfanar da shi a gaban kowace kotu ba, kamar yadda jaridar Daily Trust ta ruwaito.

    Tun da farko, El-Rufai ya shafe dare biyu a hannun Hukumar EFCC kan zargin almundahanar kuɗi lokacin yana gwamna, kafin jami’an tsaro na farin kaya (DSS) su tafi da shi, sannan daga baya aka miƙa shi ga Hukumar ICPC.

    A ranar 16 ga Fabrairu, tsohon Gwamnan ya amsa gayyatar da EFCC ta yi masa, inda jami’an bincike suka tuhume shi. Wannan ya biyo bayan gazawar jami’an tsaro wajen kama shi a filin jirgin saman Abuja lokacin da ya dawo daga ƙasar Masar.

    Abin da ya faru a kotu

    Lauyoyi sun bayyana cewa, kodayake kotu tana da ikon tsawaita lokacin tsare mutum, yin hakan ba tare da umarnin kotu ba ya saɓa wa doka a sashen 293 zuwa 296 na Dokar Shari’ar Manyan Laifuka (ACJA).

    Rahoton Daily Trust ya nuna cewa, ICPC ta samu umarnin tsare shi na kwanaki 14 daga wata Kotun Majistare da ke Bwari, Abuja, a ranar 19 ga Fabrairu, wanda aka sake sabuntawa.

    Sai dai lauyoyin El-Rufai sun shigar da buƙatar ƙalubalantar tsawaita tsare shi, inda suka bayyana hujjoji da dama waɗanda aka sanya jiya a matsayin ranar yanke hukunci kansu.

    Ana sa ran Alƙalin Majistare, Okechukwu Akweke zai yanke hukunci a ranar 19 ga Maris.

    A cikin buƙatar da aka shigar, El-Rufai ya yi zargin cewa jami’an ICPC sun buƙaci ya janye daga harkokin siyasa a matsayin sharaɗin sakin sa, inda ya bayyana hakan a matsayin take haƙƙinsa na kundin tsarin mulki.

    A cewar takardun ƙarar, ya fara kai kansa ga EFCC ne a ranar 16 ga Fabrairu inda aka ba shi beli, amma daga baya DSS ta kama shi ta miƙa shi ga ICPC ba tare da wata ƙwaƙƙwarar hujja ta shari’a ba, wanda hakan ya kai ga tsare shi ba bisa ƙa’ida ba.

    Karar ta zargi manyan jami’ai, ciki har da shugaban ICPC da Darakta Janar na DSS, da tsare shi ba tare da haƙƙi ba. Lauyoyinsa sun kuma kafa hujjar cewa, umarnin tsare shi ba shi da inganci kuma lokacin tsare shi ya wuce kima ba tare da wata hujja ba.

    Duk da haka, El-Rufai ya yi iƙirarin cewa an hana shi sadarwa da kowa, ciki har da iyalansa, lauyoyinsa, da kuma samun kulawar likita.

    Kararrakin da ake yi ne suka dakatar da mu – ICPC

    Da yake magana da ɗaya daga cikin wakilanmu a daren jiya, wani babban jami’i a ICPC ya bayyana cewa ƙararrakin da aka shigar a kan hukumar ne suka jinkirta gurfanar da shi. Ya ce dole ne a janye dukkan umarnin kotu da ke adawa da ICPC kafin hukumar ta iya gurfanar da tsohon gwamnan.

    “El-Rufai ne da kansa yake jinkirta gurfanar da shi. Ya shigar da ƙara daban-daban a kan hukumar. Saboda haka, wasu daga cikin waɗannan ƙararrakin ya kamata a janye su kafin mu ci gaba bin matakan shari’a,” in ji jami’in.


    [ad_2]

    Source link

  • Mataimakin Gwamnan Kano Na Iya Yin Murabus Saboda Barazanar Tsige Shi

    [ad_1]

    Wasu majiyoyi sun bayyana cewar mataimakin gwamnan Jihar Kano, Aminu Abdulsalam Gwarzo, na iya yin murabus biyo bayan barazanar tsige shi.

    Majiyoyin sun ce yana duba yiwuwar yin murabus daga muƙamin ne domin kauce wa tsige shi da kuma kare makomarsa ta siyasa.

    • Trump Ya Ce Amurka Za Ta Ci Gaba Da Yaƙi Da Iran Ba Tare da Taimakon Kowa Ba
    • Sarkin Musulmi Ya Ba Da Umarnin Fara Duban Jinjirin Watan Shawwal Ranar Laraba

    Rahotanni sun ce dangantakarsa da Gwamna Abba Kabir Yusuf ta yi tsami bayan gwamnan ya koma jam’iyyar APC, yayin da Gwarzo ya ci gaba da zamansa a NNPP.

    Hakan na zuwa ne bayan gwamnatin jihar ta soke ma’aikatar da Gwarzo ke jagoranta.

    Majalisar Dokokin Jihar ta riga ta ba shi takardar sanarwar tsige shi bisa zarge-zarge da suka haɗa da amfani da muƙaminsa ba daidai ba, karkatar da kuɗaɗe, da sauransu.

    ’Yan majalisar sun ce ana zargin sa da sama da faɗi da kuɗaɗe masu tarin yawa.

    An bai wa Gwarzo kwanaki 14 ya kare kansa.

    Idan aka same shi da laifi, za a tsige shi daga muƙaminsa.

    Ba a samu jin ta bakinsa ba zuwa lokacin haɗa wannan rahoto.

    [ad_2]

    Source link

  • Tinubu ya bai wa masu neman muƙaman zaɓe wa’adin yin  murabus

    [ad_1]



    Shugaba Bola Tinubu ya buƙaci dukkan masu riƙe da muƙaman gwamnati da ke sha’awar tsayawa takara a zaɓen 2027 da su yi murabus tsakanin yanzu zuwa 31 ga Maris, 2026.

    Wannan umarni yana ƙunshe ne a cikin wata sanarwa da ofishin Sakataren Gwamnatin Tarayya (SGF) ya fitar a ranar Talata.

    Sanarwar ta ce: “Shugaba Bola Ahmed Tinubu, GCFR, ya umarci dukkan masu riƙe da muƙaman siyasa a ƙarƙashin gwamnatinsa waɗanda ke da niyyar tsayawa takarar muƙaman zaɓe a zaɓukan gama-gari na 2027 masu zuwa, da su yi murabus daga muƙaman su a ranar 31 ga Maris, 2026, ko kafin hakan.”

    “Wannan umarni ya biyo bayan tanadin doka ta Sashe na 88(1) na Dokar Zaɓe ta 2026, da kuma jadawalin da Hukumar Zaɓe Mai Zaman Kanta (INEC) ta fitar na gudanar da zaɓukan fidda gwani na jam’iyyu gabanin babban zaɓen 2027,” in ji sanarwar.

    A cikin wata wasiƙa da Sakataren Gwamnatin Tarayya, Sanata George Akume ya sanya wa hannu, wadda Babban Sakatare a Ofishin Ayyuka na Gwamnati, Dr. Ibrahim Abubakar Kana ya fitar, an bayyana cewa sharaɗin murabus ɗin ya shafi dukkan nau’ukan masu naɗin siyasa na shugaban ƙasa waɗanda ke son shiga zaɓukan fidda gwani na jam’iyyu ko neman takarar kowane mukamin zaɓe.

    Wadanda abin ya shafa sun haɗa da: Ministoci da Ministocin Jiha da Masu Ba Shugaban Kasa Shawara na Musamman, da Mataimaka na Musamman ga Shugaban Kasa (SSAs da SAs), da Mataimaka na ƙashin kai ga Shugaban Kasa da dukkan Shugabannin Hukumomi da Manyan Jami’an Gudanarwa  na rassan gwamnatin tarayya, hukumomi, da kamfanonin gwamnati, da kuma duk sauran masu naɗin siyasa na Shugaban Kasa.

    An umarci dukkan jami’an da abin ya shafa da su miƙa wasiƙunsu na murabus ta ofishin Sakataren Gwamnatin Tarayya kafin ranar 31 ga Maris, 2026.

    Shugaba Tinubu ya jaddada cewa wannan mataki ya zama dole domin tabbatar da bin dokokin zaɓe, kiyaye gaskiya a harkar siyasa, da kuma samar da daidaito ga dukkan masu neman takara gabanin zaɓe.


    [ad_2]

    Source link

  • Kashe Larijani ba zai taɓa tsarin siyasar Iran ba — Minista

    [ad_1]



    Ministan Harkokin Wajen Iran, Abbas Araghchi ya bayyana cewa kisan gillar da Amurka da Isra’ila ke yi ba zai taɓa “ƙwaƙƙwaran tsarin siyasar” Tehran ba.

    Ministan ya bayyana cewa kisan da Isra’ila ta yi wa Ali Larijani, babban sakataren majalisar ƙoli ta tsaron ƙasa na Iran, ba zai zama babban rauni ga shugabancin ƙasar ba.

    A wata tattaunawa da gidan talabijin na Al Jazeera ya yi da shi, wacce aka nuna bayan da Tehran ta tabbatar da mutuwar Larijani a safiyar ranar Laraba, Ministan Harkokin Wajen Iran, Abbas Araghchi, ya ce har yanzu Amurka da Isra’ila ba su gane cewa gwamnatin Iran ba ta dogara da mutum guda ba.

    “Ban san dalilin da ya sa har yanzu Amurkawa da Isra’ilawa ba su fahimci wannan gaɓar ba: Jamhuriyar Musulunci ta Iran tana da ƙwaƙƙwaran tsarin siyasa tare da kafuwar hukumomin siyasa, tattalin arziki, da na zamantakewa,” in ji Araghchi.

    Ya ƙara da cewa, “Kasancewa ko rashin mutum guda ba ya shafar wannan tsari.

    Tabbas, ɗaiɗaikun mutane suna da tasiri, kuma kowane mutum yana taka tasa rawar – wasu sun fi wasu, wasu kuma ƙasa da hakan – amma abin da ke da muhimmanci shi ne tsarin siyasar Iran tsari ne mai matuƙar ƙarfi.”

    Araghchi ya kafa misali da kisan jagoran addinin ƙasar, Ayatollah Ali Khamenei, wanda aka kashe a ranar farko na harin Amurka da Isra’ila a ranar 28 ga Fabrairu, inda ya lura cewa duk da gagarumin rashi da ƙasar ta yi, “tsarin ya ci gaba da tafiya.”

    “Ba mu taɓa samun wanda ya kai jagoran ƙasar muhimmanci ba, kuma ko da shi ɗin ma ya yi shahada, tsarin ya ci gaba da aikinsa kuma nan take aka samar da wanda zai maye gurbinsa,” in ji Ministan.

    Ya ƙara da cewa, “Idan wani daban ya yi shahada, haka ne zai faru. Idan har Ministan Harkokin Wajen ma ya yi shahada, tabbas za a samu wani wanda zai maye gurbinsa.”


    [ad_2]

    Source link

  • Trump Ya Ce Amurka Za Ta Ci Gaba Da Yaƙi Da Iran Ba Tare da Taimakon Kowa Ba

    [ad_1]

    Shugaban Amurka, Donald Trump, ya ce ƙasarsa ba ta buƙatar taimakon wasu ƙasashe wajen yaƙin da ta ke yi da Iran, musamman kan buɗe mashigar ruwan Hormuz.

    A wani saƙo da ya wallafa, Trump ya bayyana cewa sojojin Amurka sun samu nasara, don haka ba sa buƙatar taimakon ƙasashen NATO, Japan, Australia da Koriya ta Kudu.

    • CAF Ta Soke Nasarar Senegal, Ta Ayyaṇa Morocco A Matsayin Zakarar AFCON Ta 2025
    • Tinubu Ya Bai Wa Masu Riƙe Da Muƙamai Da Ke Son Yin Takara Wa’adin Yin Murabus

    Ya nuna rashin jin daɗinsa kan yadda wasu ƙawayen Amurka suka ƙi taimaka mata, duk da cewa Amurka na da dubban sojoji a ƙasashensu domin kare su.

    Wasu ƙasashe kamar Faransa, Jamus, Spain da Birtaniya sun ce ba za su shiga yaƙin ba, saboda ba yaƙin NATO ba ne.

    Wannan mataki ya fusata Trump, inda ya ce Amurka za ta ci gaba da yaƙin ita kaɗai, yana mai cewa tuni suka fara samun nasara.

    [ad_2]

    Source link

  • Sarkin Musulmi Ya Ba Da Umarnin Fara Duban Jinjirin Watan Shawwal Ranar Laraba

    [ad_1]

    Sarkin Musulmi, Muhammad Sa’ad Abubakar, ya buƙaci al’ummar Musulmi a faɗin Nijeriya da su fara duban jinjirin watan Shawwal, wanda ke nuna ƙarshen azumin watan Ramadan 1447 bayan hijira da kuma fara bukukuwan Sallah ƙarama.

    A cikin wata sanarwa da Majalisar Masarautar Sakkwato ta fitar, an bayyana cewa ranar Laraba, 18 ga watan Maris, 2026 (wadda ta yi daidai da 29 ga watan Ramadan), ita ce ranar da za a duba jinjirin watan.

    • CAF Ta Soke Nasarar Senegal, Ta Ayyaṇa Morocco A Matsayin Zakarar AFCON Ta 2025
    • Tinubu Ya Bai Wa Masu Riƙe Da Muƙamai Da Ke Son Yin Takara Wa’adin Yin Murabus

    Ya buƙaci Musulmi su duba jinjirin watan da yamma, sannan su kai rahoto ta hanyoyin da aka tanada.

    Duk wanda ya ga jinjirin watan ya sanar da hakimin unguwarsa ko ƙauyensa, wanda zai isar da saƙonn ga Sarkin Musulmi domin tabbatarwa da sanarwa a hukumance.

    Haka kuma, majalisar ta samar da lambobin waya domin sauƙaƙa isar da rahoton ganin watan.

    A addinin Musulunci, ganin jinjirin watan Shawwal ne ke nuna ƙarshen azumin Ramadan da kuma fara bikin Sallah, ɗaya daga cikin manyan bukukuwan da Musulmi ke yi duk shekara.

    [ad_2]

    Source link

  • DAGA LARABA: Dalilan Tashin Farashin Kayan Miya Gabanin Bikin Sallah

    [ad_1]

    Ƙarin Podcasts



    Yayin da sallah ya gabato, mutane da dama kan yi fadi tashi don biyan wasu bukatun su na bukukuwan sallah, kuma kamar yadda aka saba, a irin wannan lokaci ne iyalai da dama kan maida hankulan su don ganin sun biya wasu daga cikin bukatun su musamman wadanda suka jibanci bikin sallah.

    Siyayyan kayan kayan abinci na daya daga cikin wadannan hidindimu, sai dai kayan miya da suka zama dole ayi amfani dasu yayin bikin sallah sun yi tashin gwauron zabo inda alumma da dama ke ta bayyana damuwar su kan wannan batu.

    shirin Daga Laraba na wannan makon zai yi nazari ne kan dalilan da suka sa farashin kayan miya suka yi tashin gwauron zabo gabanin bikin Sallah.

    Domin sauke shirin, latsa nan


    [ad_2]

    Source link

  • CAF Ta Soke Nasarar Senegal, Ta Ayyaṇa Morocco A Matsayin Zakarar AFCON Ta 2025

    [ad_1]

    Babban kwamitin ɗaukaka ƙara na Hukumar Ƙwallon Ƙafa ta Afirka (CAF), ya amince da ƙarar da ƙasar Morocco ta shigar, inda ya soke nasarar da tawagar Senegal ta samu a wasan ƙarshe na gasar AFCON ta 2025.

    Kwamitin ya bayyana cewa, bayan duba ƙarar da aka shigar, an samu kura-kurai da laifuka daga ɓangaren Senegal a lokacin wasan na ƙarshe.

    • Tinubu Ya Bai Wa Masu Riƙe Da Muƙamai Da Ke Son Yin Takara Wa’adin Yin Murabus
    • Gwamnonin Arewa Sun Yi Allah-wadai Da Hare-haren Ƙunar Baƙin Wake A Maiduguri

    Saboda haka, an yanke hukuncin bai wa Morocco nasara da ci 3-0, tare da ayyana su a matsayin zakarun gasar a hukumance.

    Wannan hukunci ya soke na baya da kwamitin ladabtarwa na CAF ya yanke, bayan ƙungiyar kula da ƙwallon ƙafa ta Morocco (FRMF) ta ɗaukaka ƙara kan abubuwan da suka faru a wasan.

    CAF ta bayyana cewa wasu halaye da ‘yan wasan Senegal suka nuna, ciki har da barin filin wasa da kuma jawo tsaiko na wasu mintuna, sun saɓa dokokinta, musamman sashe na 82 da 84 na dokokin gasar AFCON.

    Saboda haka, hukuncin ƙarshe ya tabbatar da cewa Morocco ce ta lashe gasar AFCON a hukumance, bayan soke nasarar da Senegal ta yi.

    [ad_2]

    Source link

  • Sin Da Faransa Sun Yi Alkawarin Zurfafa Hadin Gwiwar Tattalin Arziki Da Hada-Hadar Kudi

    [ad_1]

    Mataimakin firaministan kasar Sin He Lifeng da ministan kudi na kasar Faransa Roland Lescure, sun yi shawarwari masu zurfi jiya Litini a birnin Paris, kan ci gaban da aka samu a fannin hadin gwiwar tattalin arziki da hada-hadar kudi na Sin da Faransa da kuma sauran batutuwan da suka shafe su.

    He, jagoran tawagar Sin ta tattaunawar tattalin arziki da hada-hadar kudi tsakanin Sin da Faransa a matakin koli, ya bayyana cewa, kasar Sin a shirye take ta hada kai da Faransa wajen aiwatar da matsayar da shugaban kasar Sin Xi Jinping da shugaban Faransa Emmanuel Macron suka cimma. Ya kuma yi kira da a kara zurfafa mu’amala da hadin gwiwa a fannonin tattalin arziki da hada-hadar kudi, da kuma karfafa dorewar ci gaban dangantakar tattalin arzikin kasashen biyu ba tare da tangarda ba.

    Kazalika, He ya yi wa bangaren Faransa bayani kan tattaunawar tattalin arziki da kasuwanci tsakanin Sin da Amurka da aka gudanar a farkon wannan rana.

    Shi ma da yake jawabi, jagoran tawagar tattaunawar ta Faransa Lescure ya bayyana cewa, kasar ta Faransa tana ba da fifiko sosai ga hadin gwiwa da kasar Sin, kuma tana son yin aiki tare da Sin wajen sa-kaimi ga yin hadin gwiwa a fannonin tattalin arziki da kudi, da kuma samun gagarumin ci gaba. (Abdulrazaq Yahuza Jere)

    [ad_2]

    Source link