Category: Latest News

  • Harin Maiduguri: Fadar Shugaban Ƙasa Ta Ƙaryata Saƙon Trump A Kan Tinubu

    [ad_1]

    Fadar Shugaban Ƙasa ta ce saƙon da ya karaɗe kafafen sada zumunta, wanda ke iƙirarin cewa Shugaban Amurka Donald Trump ya soki Shugaba Bola Tinubu kan hare-haren Maiduguri, ba gaskiya ba ne.

    Mai bai wa Shugaban Ƙasa shawara kan harkokin yaɗa labarai, Sunday Dare, ya bayyana sakon a matsayin “ƙarya!!!” a wani rubutu da ya wallafa a shafinsa na X ranar Talata.

    • Gwamnonin Arewa Sun Yi Allah-wadai Da Hare-haren Ƙunar Baƙin Wake A Maiduguri
    • Manyan Ma’aunan Tattalin Arzikin Sin Sun Karu Daga Janairu Zuwa Fabrairu

    Ya kuma wallafa hoton saƙon domin gargaɗin jama’a kan yaɗa labaran ƙarya.

    A cikin saƙon an bayyana cewa Trump ya zargi Tinubu da gazawa wajen magance matsalar tsaro a Arewa maso Gabas, tare da sukar tafiyarsa zuwa Birtaniya a lokacin da hare-haren a ƙasar.

    Haka kuma saƙon ya ce Trump ya nemi Firaministan Birtaniya, Keir Starmer, da ya umarci Tinubu ya dawo Nijeriya.

    Sai dai bincike ya nuna cewa Trump bai fitar da wannan bayani a shafukansa ba.

    Wannan jita-jitar ta yaɗu ne a lokacin da ake cikin damuwa bayan hare-haren Maiduguri.

    Da yammacin ranar Litinin, wasu da ake zargi ‘yan ƙunar baƙin wake ne sun kai hare-hare a wurare daban-daban na birnin, ciki har da wuraren da jama’a ke taruwa.

    ‘Yansanda sun ce aƙalla mutane 23 sun mutu, yayin da sama da 100 suka jikkata.

    Hare-haren sun biyo bayan wani harin da aka kai wani sansanin sojoji a yankin Ajilari.

    Shugaba Tinubu ya bayyana hare-haren a matsayin “abin takaici matuƙa”, yana mai ɗora laifi kan ƙungiyoyin ta’addanci da ke fuskantar matsin lamba daga dakarun Nijeriya.

    Ya jajanta wa iyalan waɗanda suka rasu, ya kuma tausaya wa waɗanda suka jikkata, tare da tabbatar da cewa gwamnati za ta ci gaba da ƙoƙarin tabbatar da tsaro.

    Haka kuma ya umarci shugabannin tsaro su koma Maiduguri domin jagorantar ayyukan tsaro, yana mai cewa Nijeriya ba za ta yarda ta’addanci ya yi tasiri ba.

    [ad_2]

    Source link

  • A soma duban watan Shawwal ranar Laraba — Sarkin Musulmi

    [ad_1]



    Sarkin Musulmi, Alhaji Sa’ad Abubakar, ya umurci musulmai a Najeriya da su fara duban watan Shawwal daga gobe Laraba, 29 ga watan Ramadan 1447, wanda ya yi daidai da 18 ga Maris, 2026.

    Hakan na ƙunshe ne cikin wata sanarwa da fadar sarkin ta fitar a ranar Talata, 17 ga Maris, 2026, yayin da watan Azumi na Ramadan ke cika kwanaki 28 da kamawa.

    A takardar da Farfesa Sambo Wali Junaid, Waziri Sakkwato kuma shugaban kwamitin bai wa Sarkin Musulmi shawara kan harkokin addini, ya fitar, an shawarci duk wanda ya ga watan da ya sanar da hakimi ko uban ƙasa mafi kusa ko kuma ta hanyar kira ga majalisar Sarkin Musulmi a lambobin waya kamar haka: 08037157100, 08066303077, 08035965322.

    Watan Shawwal na cikin watannin Musulunci masu muhimmanci, inda ake ci gaba da ibadar azumi na wasu ƙayyadaddun kwanaki da da ake so musulmai su gudanar don samun rabo da tsira a gobe ƙiyama.


    [ad_2]

    Source link

  • Tinubu ya umarci hafsoshin tsaro su koma Maiduguri

    [ad_1]



    Shugaba Bola Ahmed Tinubu, ya bai wa hafsoshin tsaro umarnin komawa Maiduguri, babban birnin Jihar Borno, domin su jagoranci ayyukan tsaro kai tsaye a yankin.

    Wannan mataki ya biyo bayan hare-haren bama-bamai da suka yi sanadin mutuwar mutane sama da 20 tare da jikkata fiye da 100.

    Rahotanni daga Maiduguri sun bayyana cewa wasu da ake zargin ‘yan ta’addan Boko Haram ne suka kai hare-haren a lokaci guda a sassa daban-daban na jihar, da misalin ƙarfe 7:25 na yammacin ranar Litinin.

    Wani jami’in tsaro ya ce hare-haren sun janyo firgici da tashin hankali a cikin al’umma musamman a kasuwanni da wuraren taruwar jama’a.

    Shugaban ƙasa ya bayyana takaicinsa kan wannan lamari, inda ya ce gwamnatinsa tana da ƙudurin kawo ƙarshen matsalar tsaro a Arewa maso Gabas.

    Tinubu ya umarci jami’an tsaro su ƙara ƙaimi wajen kare rayuka da dukiyoyin al’umma, tare da tabbatar da zaman lafiya mai ɗorewa.


    [ad_2]

    Source link

  • Gwamnonin Arewa Sun Yi Allah-wadai Da Hare-haren Ƙunar Baƙin Wake A Maiduguri

    [ad_1]

    Shugaban Ƙungiyar Gwamnonin Jihohin Arewa (NSGF) kuma Gwamnan Jihar Gombe, Muhammadu Inuwa Yahaya, ya yi Allah-wadai da mummunan fashewar bama-bamai da ta girgiza Maiduguri a yammacin ranar Litinin, yana mai bayyana harin a matsayin barazana ga al’ummomin yankin.

    Rahotanni sun ce fashe-fashen sun faru kusan a lokaci guda a ƙofar Asibitin Koyarwa na Jami’ar Maiduguri, zagayen Kasuwar Litinin da kuma yankin Ofishin Wasiƙa, lamarin da ya yi sanadiyar mutuwar mutane da dama.

    • Zulum Ya Yi Allah-Wadai Da Fashewar Bam A Maiduguri, Ya Buƙaci A Ƙara Tsaro A Wuraren Ibada
    • Ko Za A Ga Sauyi Bayan Tattaunawar Tattalin Arziki Da Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka?

    A cikin wata sanarwa da mai magana da yawunsa, Isma’ila Uba Misilli, ya fitar a ranar Talata, Gwamna Yahaya ya nuna matuƙar alhini kan wannan mummunan lamari, tare da miƙa ta’aziyyarsa ga gwamnati da al’ummar Jihar Borno, musamman iyalan waɗanda suka rasa rayukansu.

    “Wannan mummunan lamari ba kawai abin ƙyama ba ne, har ila yau wata muguwar ƙoƙari ce ta jefa tsoro da kuma tarwatsa zaman lafiyar da ake ƙoƙarin dawo da shi a yankin Arewa maso Gabas. Hari ne ga ɗan’adam baki ɗaya, kuma dole ne a yi Allah-wadai da shi da kakkausar murya,” in ji gwamnan.

    Shugaban NSGF ɗin ya kuma jajanta wa waɗanda suka samu raunuka ke karɓar magani a asibitoci daban-daban, yana addu’ar samun sauƙi cikin gaggawa gare su, tare da yaba wa masu aikin agaji na farko da jami’an tsaro bisa gaggawar da suka yi wajen shawo kan lamarin bayan fashe-fashen.

    [ad_2]

    Source link

  • Gwamnonin Arewa sun yi Allah-wadai da harin da aka kai Maiduguri

    [ad_1]



    Kungiyar Gwamnonin Arewa (NSGF) ta yi Allah-wadai da mummunan harin ƙunar-baƙin-wake da ya auku a yammacin jiya na Litinin a Maiduguri, babban birnin Jihar Borno.

    Aminiya ta ruwaito yadda aka samu tashin bama-bamai kashi uku a kusan lokaci guda a Asibitin Koyarwa na Maiduguri da babbar kasuwar nan ta Monday Market da kuma yankin Gidan Waya da Aika Saƙonni, lamarin da ya yi sanadin mutuwar mutane da dama tare da jikkata wasu.

    A cikin wata sanarwa da shugaban ƙungiyar kuma Gwamnan Jihar Gombe, Muhammadu Inuwa Yahaya ya fitar, ya bayyana matuƙar alhini kan harin, tare da miƙa ta’aziyya ga gwamnati da al’ummar Jihar Borno musamman iyalan waɗanda suka rasa rayukansu.

    Ya ce babu shakka an kai harin ne da nufin jefa tsoro a zukatan jama’a da kuma kawo cikas ga ƙoƙarin dawo da zaman lafiya a yankin Arewa maso Gabas.

    “Wannan mummunan aiki cin zarafi ne ga bil’adama baki ɗaya, kuma dole ne a yi Allah-wadai da shi da kakkausar murya,” in ji shi.

    Gwamnan ya kuma jajanta wa waɗanda suka jikkata, yana mai yi musu fatan samun sauƙi cikin gaggawa, tare da yaba wa jami’an agaji da hukumomin tsaro kan gaggauta ɗaukar mataki.

    Ya jaddada ƙudurin gwamnonin Arewa na ci gaba da haɗa kai da Gwamnatin Tarayya da jami’an tsaro domin kawo ƙarshen ta’addanci da sauran miyagun laifuka.

    Haka kuma ya buƙaci al’umma da su kwantar da hankalinsu tare da bai wa jami’an tsaro haɗin kai ta hanyar bayar da sahihan bayanai domin taimakawa bincike.

    A ƙarshe, ya yi addu’ar Allah ya jiƙan waɗanda suka rasu, tare da kira ga hukumomi da su kamo waɗanda suka aikata wannan ta’asa domin gurfanar da su a gaban kuliya.


    [ad_2]

    Source link

  • Gwamnonin Arewa sun yi Allah-wadai da harin da aka kai Maiduguri

    [ad_1]



    Kungiyar Gwamnonin Arewa (NSGF) ta yi Allah-wadai da mummunan harin ƙunar-baƙin-wake da ya auku a yammacin jiya na Litinin a Maiduguri, babban birnin Jihar Borno.

    Aminiya ta ruwaito yadda aka samu tashin bama-bamai kashi uku a kusan lokaci guda a Asibitin Koyarwa na Maiduguri da babbar kasuwar nan ta Monday Market da kuma yankin Gidan Waya da Aika Saƙonni, lamarin da ya yi sanadin mutuwar mutane da dama tare da jikkata wasu.

    A cikin wata sanarwa da shugaban ƙungiyar kuma Gwamnan Jihar Gombe, Muhammadu Inuwa Yahaya ya fitar, ya bayyana matuƙar alhini kan harin, tare da miƙa ta’aziyya ga gwamnati da al’ummar Jihar Borno musamman iyalan waɗanda suka rasa rayukansu.

    Ya ce babu shakka an kai harin ne da nufin jefa tsoro a zukatan jama’a da kuma kawo cikas ga ƙoƙarin dawo da zaman lafiya a yankin Arewa maso Gabas.

    “Wannan mummunan aiki cin zarafi ne ga bil’adama baki ɗaya, kuma dole ne a yi Allah-wadai da shi da kakkausar murya,” in ji shi.

    Gwamnan ya kuma jajanta wa waɗanda suka jikkata, yana mai yi musu fatan samun sauƙi cikin gaggawa, tare da yaba wa jami’an agaji da hukumomin tsaro kan gaggauta ɗaukar mataki.

    Ya jaddada ƙudurin gwamnonin Arewa na ci gaba da haɗa kai da Gwamnatin Tarayya da jami’an tsaro domin kawo ƙarshen ta’addanci da sauran miyagun laifuka.

    Haka kuma ya buƙaci al’umma da su kwantar da hankalinsu tare da bai wa jami’an tsaro haɗin kai ta hanyar bayar da sahihan bayanai domin taimakawa bincike.

    A ƙarshe, ya yi addu’ar Allah ya jiƙan waɗanda suka rasu, tare da kira ga hukumomi da su kamo waɗanda suka aikata wannan ta’asa domin gurfanar da su a gaban kuliya.


    [ad_2]

    Source link

  • Tsayuwa Da Ƙafa Biyu Ya Fi Tsayuwa Da Kafa Ɗaya

    [ad_1]

    Lokacin da na karbi ragamar aiki a matsayin Ministan Tsaro, na yi alkawarin karfafa tsarin tsaron kasar. Na jaddada cewa, da farko, a matsayinmu na ‘yan Nijeriya dole ne mu dauki alhakin daukar nauyin da kalubalen da kasarmu ke fuskanta.

    Wannan ba kawai magana ba ce, illa kira ne zuwa aiki. Ina kuma tsaye daram wajen tabbatar da cewa mun fuskanci kalubalen tsaronmu kai tsaye ta hanyar amfani da falsafar “hadin kai da manufa daya”, wadda ke nufin mu yi aiki tare a matsayin kungiya guda, maimakon kowanne bangare ya yi aiki shi kadai kamar rundunar da ke zaman kanta. ”

    “Wannan ita ce falsafar da na bi a duk tsawon aikina na hidimta wa kasa a mukaman jagoranci da na ma’aikata a cikin aikin sojin Nijeriya. Wannan tunani ya ci gaba da kasancewa tare da ni har zuwa yau.

    Na kuma saba da bai wa jami’ai kwarin gwiwa da ke karkashina su fahimci muhimmancin wannan tunanin na dabarun tsaro, tare da aiwatar da shi a duk inda suka tsinci kansu a cikin aikinsu.

    Matsayin da nake rike da shi a yau yana da nufin karfafa tsarin tsaron kasar, bisa ga umarnin da Bola Ahmed Tinubu, Babban Kwamandan Askarawan Nijeriya, ya ba ni.

    Ina da cikakken kuduri da himma wajen mayar da fata da burin ‘yan Nijeriya su zama gaskiya ta hanyar kawo karshen ta’addanci a kasar.”

    Daidaitawar Soji Da Farar Hula

    “A lokacin da nake hidima a matsayin jami’in soja, daya daga cikin kalubalen da na fuskanta shi ne daidaita tunanin soja da al’adun farar hula. Akwai lokuta da dama da dole ne mutum ya saurari ra’ayin farar hula wajen magance matsalolin tsaro yayin da suke faruwa.

    A lokutan da na bi ra’ayin farar hula, na ga sakamakon da na samu a matsayin kwamanda ya burge ni matuka. Duk da na san cewa wasu daga cikin shawarar da na yanke ba su yi wa wasu daga cikin sojojina dadi ba, amma a matsayina na kwamanda, dole ne su amince da hukuncin da na yanke.

    A koyaushe ni nake daukar alhakin wadannan shawarwari. Idan na waiwaya baya yanzu, ina farin ciki da na yanke wadannan matakai domin sun tabbatar da cewa suna da amfani sosai.”

    Haramtaccen Yaki Da Ingantacce

    Yakin da bai da daidaito ba za’a auna shi da yawan ‘yan ta’adda da aka kashe a daji kawai ba, amma da yawa akwai mutanen da aka ‘yanto daga shiga ta’addanci ko aka fito da su daga daji. Wannan yana nuna juriya a yaki, wato daga kirga gawarwaki zuwa halastaccen mulki.

    Yakin da ‘yan ta’adda ke yi yana da wahala kuma sau da yawa yana taba yunkurin dakaru ne kawai, wanda hakan zai kai ga jama’a su gaji da jinkirin samun sakamako. Amma halattaccen yaki yana mai da hankali kan gano tushen matsalolin da ke haddasa rikicin. Saboda haka, dabarun aikina sun ginu ne a kan hada wadannan hanyoyi biyu domin samun sakamako mai dorewa.

    Nadin da aka yi min daga baya a matsayin Babban Hafsan Tsaro (CDS) ya ba ni damar fadada gano abin da ake kira “tsarin Borno” a cikin ayyukan soji..

    Ina tuna cewa a lokacin da nake CDS, a taron Kwamandojin Rundunar Hadin Gwiwa na CDS mai taken Inganta hadin Kai A Sansanin Soji”, na jaddada muhimmancin hadin kai wajen aiki, amfani da dabaru, da kuma hada al’umma baki daya wajen magance matsalolin tsaro.

    Misali, canza sunan aikin hadin gwiwar soja a Jihar Filato daga ‘Operation Safe Haben’ zuwa ‘Operation Enduring Peace’ wanda an yi shi ne domin samar da sabon hangen nesa ga sojoji da al’ummomin yankin kan muhimmancin yin aiki tare domin samar da zaman lafiya mai dorewa a Jihar Filato.

    Ina alfahari da cewa wannan dabarar tana aiki a jihar da kuma a sauran wuraren da sojojin Nijeriya ke gudanar da ayyukansu a fadin kasar.

    Dabarun Hada Kan Al’umma

    Akwai wani abu da na fahimta wanda nake son jaddadawa. Ba kasafai ake ganin sa a fili a cikin al’umma. A halin yanzu muna yaki ne da rikici mai sassa da dama. Kungiyoyin ta’addanci kamar Boko Haram, ISWAP, da Lakurawa da wasu kungiyoyin masu tashin hankali sun hada kai, sun ajiye sabanin da ke tsakaninsu domin su yi aiki tare su kai hare-hare. A wasu lokuta ma suna musayar bayanan sirri a tsakaninsu.

    Wannan gaskiya ce, kuma shi ya sa ake bukatar abin da ake kira “tsayuwa da kafafu biyu”, wato hada dabarun karfi na soja da kuma dabarun da ba na soja ba a cikin ayyukan tsaronmu, domin samar da daidaito da ake bukata wajen kayar da ta’addanci.

    Idan kungiyoyin ta’addanci na iya hada kai, me zai hana jama’ar kasa su hada kai da sojoji? Ba za mu iya kayar da ta’addanci da bindigogi da harsasai kawai ba. Wannan shi ne ainihin sakon da nake son isarwa a wannan rubutu.

    Kwarewata a matsayin Kwamandan Yanki da Babban Hafsan Tsaro har yanzu tana da tasiri sosai a tunanina. Na kalli matsalolin daga matsayi na jagoranci da na ma’aikata. Misali, yanke shawarar bin ra’ayin farar hula ta hanyar yin hadin kai ba tare da tangarda ba da gwamnatin Jihar Borno ya haifar da gagarumar nasara a yaki da ta’addancin Boko Haram.

    Wannan kuma yana karfafa hujjata ta cewa tsaro nauyi ne da kowa ke dauka. Wannan shi ne tsarin aiki a kasashen da suka ci gaba. Ban yarda cewa tsarinmu ya kamata ya bambanta ba.

    Wannan shi ne tsarin da Ma’aikatar Tsaro ke aiwatarwa. Ina farin cikin ganin cewa dukkan sassan sojojin Nijeriya sun daidaita da wannan dabarar. Haka kuma ma’aikatar tana yin hadin gwiwa da masu ruwa da tsaki a cikin al’umma, cibiyoyin addini da na gargajiya, kafofin yada labarai, kungiyoyin farar hula, da sassan kasuwanci na musamman domin shiga cikin dabarar “Hadin Kan Al’umma Gaba daya” wajen magance kalubalen tsaro na kasa.

    Mun tsara wani samfurin aika sako wanda ya dace da kowane matsayi na al’umma, har ma da mazauna karkara. Manufar ita ce samar da wayar da kai cewa idan muka hada kai, za mu iya kai da ta’addanci kasa idan muka dage a kan hakan.

    Akwai abubuwa da dama da ke haifar da rashin tsaro, amma akwai hanya daya da za ta iya dakatar da shi. Kuma wannan hanya ita ce lokacin da ’yan Nijeriya suka dauki nauyin hakan, ba tare da la’akari da al’adu ko qabila ba. Wannan nauyi ne na tilas domin juya yanayi a kan wadanda ba sa fatan alheri ga kasarmu.

    ‘Yan Kallo Da Ba Sa Kawo Dauki

    Kwanan nan na gabatar da jawabi na musamman a taron shekara-shekara na Kungiyar Tsoffin Daliban Kwalejin Tarayya ta Kaduna a matakin duniya. Na jaddada cewa:

    “Tarihi yana koya mana cewa babu wata kasa da za ta kasance mai tsaro idan ’yan kasarta suna zama masu kallo da ba sa shiga tsakani.”

    Na ba da misali cewa manomi a Sakkwato, mai kasuwanci a Legas, da malami a Enugu suna zama layin farko na tsaro a kasa. Wannan yana kama da motsa muhawara kan tsaro daga sansanonin soja zuwa tituna, yana nuna cewa tsaro nauyi ne da ke wuyan kowa. Sojoji ba za su iya kasancewa a ko’ina ba. Saboda haka, ya zama dole ’yan Nijeriya su kasance masu shiga tsakani cikin tsarin tsaro, ba masu kallo marasa shiga tsakani ba.

    Wannan rubutu na zaba masa take mai sauki wato “Tsayuwa da kafafu biyu ya fi tsayuwa da kafa daya”. Wannan dabara ce da ta dace da sabon tunani da muke kokarin gabatarwa.

    Ina son sakon ya kai ga kowa, daga mai POS a Ibadan, mai dinki a Kaduna, har zuwa ma’aikacin gwamnati a Port Harcourt. Wannan wajibi ne, kuma yana dauke da alkawari zuwa ga ’yan Nijeriya na “tsayuwa da kafafu biyu” a yaki da ta’addanci.

    Na dauki wannan alkawari ne a ranar 21 ga Satumba, 1991, lokacin da aka ba ni Kwamishinan Shugaban Kasa don aiki a Rundunar Sojan Nijeriya a matsayin jami’in soja na kasa. Dole ne mu hada kai don canza al’adar tsaro ta kasa.

    [ad_2]

    Source link

  • Indomie ta Gabatar Da Waƙoƙin Yabon Al’adu Na Farko Na Afirka Don Ranar Uwa ta duniya

    [ad_1]



    A wata rana mai cikin yanayi na zafi a wani falo a Legas, ‘yan’uwa su uku sun yi taɗi a waya, suna daidaita ƙarar wata waka da yanayin  murya mai ƙarfi ta cika sararin samaniya.

    Waƙar ta yi kama da ta irin tada, waƙa, cikin girmamawa. Duk da haka babu wani mawaƙin yabon da ya shigo ɗakin.

    Waƙoƙin yabon sun samo asali ne tun da daɗewa ta hanyar basirar wucin gadi.

    Cikin daƙiƙoki kaɗan, sunan mahaifiyarsu ta shiga cikin waƙar da ke yawo tana murna a matsayin mai renon yara, mai karevginshiƙin iyalinta.

    Ta ɗago kai cikin mamaki, tana dariya a hankali yayin da yabon ya ci gaba.

    Abin da ya fara  cikin farin ciki mai natsuwa ga ‘ya’yanta, da nufin ya zama abin mamaki.

    A gare ta, hakan ya yi kama da wanda aka saba da shi ba zato ba tsammani, kamar waƙoƙin yabon da ta ji suna mata.

    A cikin ƙasar da aka daɗe ana girmama iyaye mata a cikin karin magana, waƙoƙin yabon tun kafin a fara nuna yabo a kafofin sada zumunta, wani sabon kamfen ne na Indomie Kuma  ƙoƙari ne  mai ban mamaki, dake haɗa basirar da hulɗar ɗan adam don yin magana da harshe na al’ada.

    A cikin shirinta na Show Some Love To Mum na shekarar 2026, kamfanin taliya indomie  ya gabatar da abin da ya bayyana a matsayin dandamalin yabon al’adu na farko da ke amfani da fasahar AI a Najeriya. Dandalin yana bawa ‘yan Najeriya damar samar da waƙoƙin yabon jama’a na musamman da aka keɓe ga iyaye, don tabbatar da yada al’adun  da bada labari na asali.

    Akwai fahimta mai sauƙi da godiya  mai tasiri sosai idan aka bayyana ta hanyar al’adu da aka saba.

    A faɗin Afirka, girmama uwaye ya daɗe yana ɗaukar siffar waka.

    A tsakanin Yarabawa, al’adar Oríkì tana  yabon kyawawan halaye, da gadon kakanninsu.

    Sau da yawa ana kwatanta uwaye a matsayin  zinariya – kuma a matsayin masu kula da tunawa da iyali.

    A cikin al’ummomin Igbo, karin magana kamar “Nne bu ndu,” ma’ana uwa ita ce rai, tana ɗaukar zurfin girmamawa ga uwa, yayin da waƙoƙin biki ke girmama mata a matsayin ginshiƙan motsin rai na gida.

    A Arewacin Najeriya, mawaƙan yabon da ke yin Wakar yabo sun daɗe suna yabon mata a matsayin uwar gida, ginshiƙin gida.

    Tun kafin a fara amfani da hashtags da jadawalin dijital, waɗannan al’adu sun kasance a matsayin bayyana godiya.

    Indomie ta yi ƙoƙarin fassara wannan harshe zuwa zamanance don dacewa da aladunmu.

    Ta hanyar wani dandamali na musamman, masu amfani suna nuna hotunan mahaifiyarsu, suna shigar da sunanta, suna zaɓar harshen al’ada kuma nan take suna karɓar bidiyon waƙoƙin yabo na musamman wanda aka yi wahayi zuwa gare su daga harshen Yorubanci da  Oríkì, waƙoƙin bikin na Igbo, Dana al’adun waƙoƙin Arewa, da kuma yabo a cikin harshen Ingilishi matakai ne na nuna kauna ga uwa..

    Fasahar zamani, wacce za a iya saukewa na tsawon wata ɗaya ta  yanar gizo a wannan adireshi www.indomie.ng/showsomelovetomum, tana haɗa fasaha da ƙirƙirar ƙwaƙwalwa, tana sanya wani matsayin sabon abu don ci gaban  al’adu.

    jingina ga haɗin kai na iyali, wani shiri ne dake wakiltar juyin halitta da inganta al’adu.

    Ranar Uwa da AI ta fara ya sami karɓuwa da kyaututtuka, da bayyana abin da shugabannin kamfanoni suka bayyana a matsayin martani mai ƙarfi na habaka al’ada daga ‘yan Najeriya da ke sha’awar jin dadin waƙoƙin yabon uwa ta hanyoyin  zamani da na al’ada.

    Sigar wannan shekara ta faɗaɗa wannan ra’ayin ta hanyar sanya al’adu,  a tsakiya don samun cigaban kasa.

    A gidajen Najeriya, soyayya ba kasafai

    take yin shiru ba; ana rera ta, ana magana da ita, kuma ana yaba mata,”

    in ji Temitope Sule, Manajan Instant Noodles na Indomie.

    Nuna Soyayya ga uwa, ba wai kawai muna amfani da AI a matsayin kayan aiki ba; muna koyar da fasaha don ciyar da al’ada gaba.

    Lokacin da

    kirkire-kirkire ke nuna asali, yana zama dole ga ɗan adam, kuma a nan ne haɗin kai na gaskiya ke rayuwa.

    Da yake ba da ƙarin haske kan rawar da kamfen ɗin ya taka a birane, Ibrahim Isah, daga Legas, ya bayyana cewa shirin yana nuna yadda iyalai na zamani a Najeriya ke fuskantar al’adu a wurare na zamani ba tare da rasa zurfin motsin rai ba.

    Jihar Lagos tana wakiltar wurin haɗuwa da raya al’adu da kirkire-kirkire.

    Abin da muke gani shine matasan ‘yan Najeriya suna son bikin uwayensu ta hanyoyin da suke jin zamani amma har yanzu suna da tushe a cikin asali,” in ji shi.

    Wannan dandamali yana ba da damar al’adu su yi tafiya a cikin saurin fasaha yayin da suke kiyaye sharudda da ake dasu

    Lokacin da mutane suka ji sunan mahaifiyarsu da aka saka a cikin waƙoƙin yabo, yana daina zama talla kuma ya zama lokacin sirri.”

    Masu lura da tallace tallace sun ce kamfen ɗin yana nuna babban sauyi a cikin ba da labarin kyakkyawar alama.

    Maimakon watsa saƙonni, kirkire ƙirƙire akwai masu haɗin gwiwa inda masu sauraro ke taimakawa wajen samar da ma’ana da ake bukata.

    Ga Ebere, Manajan Yankin, Kudu maso Yamma, wannan shiri ya yi tasiri sosai ga al’adun gargajiya na yabo da bayar da labarai da suka daɗe a cikin tsarin zamantakewa na

    À yankinmu.

    “Musamman a Kudu maso Yamma, waƙoƙin yabo sun fi aiki da tuna baya.

    A Kudu maso Yamma, waƙoƙin yabo sun fi aiki da girmamawa, da kuma bayar da labarai tsakanin tsararraki,”

    in ji ta. “Abin da Indomie ta yi shi ne sake fassara wannan al’adar ga iyalai na yau, ta tabbatar da cewa ko da a zamanin dijital, yara za su iya magana da harshen godiya da iyayensu suka fahimta ta hanyar da ba ta dace ba.”

    A zamanin da basira ke bada gagarumin cigaba galibi ana danganta ta da sarrafa kanta da inganci da gwajin Indomie ya nuna wata dama ta fasaha a matsayin mai kula da al’adu maimakon maye gurbinta.

    Ta hanyar mayar da algorithms zuwa mawaƙan yabo da wayoyin komai da ruwanka zuwa tasoshin gado, Nuna kauna ga uwa ya sake tsara kirkire-kirkire ba a matsayin rikici ba amma a matsayin ci gaba –

    ƙungiyar mawaƙa ta zamani da ke ɗauke da ɗaya daga cikin tsoffin saƙonnin godiya na Afirka da girmamawa ga mahaifiyarka abune na farinciki.

    KARSHE


    [ad_2]

    Source link

  • Yanzu-yanzu: Tinubu Ya Umarci Shugabannin Tsaro Su Koma Maiduguri

    [ad_1]

    Shugaban ƙasa, Bola Tinubu, ya umarci shugabannin rundunonin tsaro su koma Maiduguri, babban birnin jihar Borno, domin su jagoranci magance matsalar tsaro a can.
    Wannan na zuwa ne bayan hare-haren bama-bamai da dama da suka yi sanadin mutuwar fiye da mutum 20 tare da jikkata sama da mutane 100.
    A jiya daren Litinin, mun rahoto muku yadda wasu jerin fashe-fashen bama-bamai suka faru a jihar, inda ake zargin ‘yan Boko Haram ne suka kai hare-hare a lokaci guda da misalin ƙarfe 7:25.
    Da yake mayar da martani kan wannan mummunan lamari kafin ya tashi zuwa ziyarar aiki mai tarihi zuwa birnin Landan, Tinubu ya ce Nijeriya ba za ta mika wuya ga tsoron ‘yan ta’adda ba.

    [ad_2]

    Source link

  • Mutum 23 sun mutu a hare-haren ƙunar-baƙin-wake a Maiduguri

    [ad_1]



    Rundunar ‘yan sanda a Jihar Borno ta tabbatar da cewa mutane 23 sun mutu yayin da 108 suka jikkata sakamakon fashewar bama-bamai guda uku a lokaci guda a sassan Maiduguri.

    Kakakin Rundunar, ASP Nahum Kenneth Daso, ya ce binciken farko ya nuna cewa waɗanda ake zargi da kai hare-haren ‘yan ƙunar bakin wake ne da suka yi amfani da na’urorin fashewa na gida.

    Jami’in hulɗa da jama’a na rundunar ‘yan sandan ya ce ana tunanin hare-haren ƙunar-baƙin-wake ne suka haddasa tashin bama-baman.

    Sai dai ya ce abubuwa sun koma yadda ake a da a wuraren, yana mai kira ga mutane su bai wa ‘yan sanda rahoton duk wani abu da ba su yarda da shi ba.

    Aminiya ta ruwaito cewa, an samu fashewar bama-baman ne jim kaɗan bayan buɗa-baki a wurare daban-daban na birnin ciki har da kasuwar Monday Market da ofishin kiran waya da aika sakonni na Post Office da kuma Asibitin Koyarwa na Maiduguri.

    Wani jami’in Hukumar NEMA mai ba da agajin gaggawa, Surajo Abdullahi, ya shaida wa Aminiya cewa mutum aƙalla 23 ne suka mutu sannan mutum 169 suka jikkata a hare-haren.

    “A halin yanzu mutum 108 suna samun kulawa a Asibitin Koyarwa na Jami’ar Maiduguri, kuma 20 suna Asibitin Tunawa da Umaru Shehu yayin da mutum 17 ke Asibitin Ƙwararru na Maiduguri,” in ji shi.

    Mazauna Maiduguri da dama sun ce a shekarun baya birnin ya fara mantawa da hare-haren bama-bamai da harbe-harben bindigogi amma yanzu lamura sun soma dagulewa.

    “Komai ya dawo sabo yanzu – muna cikin tsoro da fargaba. Waɗannan hare-hare sun nuna yadda birnin na Maiduguri ke sake fama da tashin hankula bayan sun lafa a shekarun baya,” in ji wani mazaunin birnin.


    [ad_2]

    Source link