Harin Maiduguri: Fadar Shugaban Ƙasa Ta Ƙaryata Saƙon Trump A Kan Tinubu
[ad_1]
Fadar Shugaban Ƙasa ta ce saƙon da ya karaɗe kafafen sada zumunta, wanda ke iƙirarin cewa Shugaban Amurka Donald Trump ya soki Shugaba Bola Tinubu kan hare-haren Maiduguri, ba gaskiya ba ne.
Mai bai wa Shugaban Ƙasa shawara kan harkokin yaɗa labarai, Sunday Dare, ya bayyana sakon a matsayin “ƙarya!!!” a wani rubutu da ya wallafa a shafinsa na X ranar Talata.
- Gwamnonin Arewa Sun Yi Allah-wadai Da Hare-haren Ƙunar Baƙin Wake A Maiduguri
- Manyan Ma’aunan Tattalin Arzikin Sin Sun Karu Daga Janairu Zuwa Fabrairu
Ya kuma wallafa hoton saƙon domin gargaɗin jama’a kan yaɗa labaran ƙarya.
A cikin saƙon an bayyana cewa Trump ya zargi Tinubu da gazawa wajen magance matsalar tsaro a Arewa maso Gabas, tare da sukar tafiyarsa zuwa Birtaniya a lokacin da hare-haren a ƙasar.
Haka kuma saƙon ya ce Trump ya nemi Firaministan Birtaniya, Keir Starmer, da ya umarci Tinubu ya dawo Nijeriya.
Sai dai bincike ya nuna cewa Trump bai fitar da wannan bayani a shafukansa ba.
Wannan jita-jitar ta yaɗu ne a lokacin da ake cikin damuwa bayan hare-haren Maiduguri.
Da yammacin ranar Litinin, wasu da ake zargi ‘yan ƙunar baƙin wake ne sun kai hare-hare a wurare daban-daban na birnin, ciki har da wuraren da jama’a ke taruwa.
‘Yansanda sun ce aƙalla mutane 23 sun mutu, yayin da sama da 100 suka jikkata.
Hare-haren sun biyo bayan wani harin da aka kai wani sansanin sojoji a yankin Ajilari.
Shugaba Tinubu ya bayyana hare-haren a matsayin “abin takaici matuƙa”, yana mai ɗora laifi kan ƙungiyoyin ta’addanci da ke fuskantar matsin lamba daga dakarun Nijeriya.
Ya jajanta wa iyalan waɗanda suka rasu, ya kuma tausaya wa waɗanda suka jikkata, tare da tabbatar da cewa gwamnati za ta ci gaba da ƙoƙarin tabbatar da tsaro.
Haka kuma ya umarci shugabannin tsaro su koma Maiduguri domin jagorantar ayyukan tsaro, yana mai cewa Nijeriya ba za ta yarda ta’addanci ya yi tasiri ba.
[ad_2]
Source link