Category: Latest News

  • Sallah: FRSC ta haramta wa ƙananan yara tuƙi a Gombe

    [ad_1]



    Hukumar Kiyaye Haɗura ta Ƙasa (FRSC) a Jihar Gombe, ta gargaɗi ƙananan yara kan yin tuƙi, yayin bukukuwan Sallah.

    Kwamandan hukumar a jihar, Samson Kaura, ya ce duk wanda bai kai shekara 18 ba bai kamata ya yi tuƙi ba, domin hakan na da haɗari sosai.

    Ya bayyana cewa daga cikin abubuwan da ke haddasa haɗura akwai gudun wuce ƙima, lodi fiye da ƙima, tuƙin ganganci, da kuma amfani da waya ko ƙwayoyi yayin tuƙi.

    Kaura, ya nuna damuwa kan yadda ake ganin ƙananan yara suna tuƙa motoci da babura a wasu sassan jihar, yana mai cewa hukumar ba za ta yarda da hakan ba.

    Ya ce hukumar ta fara sintiri na musamman domin tsaro a lokacin bukukuwan Sallah, inda aka tura jami’ai a manyan hanyoyi domin tabbatar da zaman lafiya.

    “Masu rai ne kaɗai ke yin biki, don haka a riƙa tuƙi a hankali tare da fifita tsaro,” in ji shi.

    Haka kuma, ya gargaɗi iyaye da kada su bar ’ya’yansu ƙanana su riƙa tuƙi, domin hakan na jefa rayuka cikin hatsari.

    FRSC ta kuma tura jami’ai sama da 620, tare da motoci 10 na sintiri, motoci huɗu na ɗaukar marasa lafiya, da kuma mota mai jan motoci domin taimakon gaggawa.

    A ƙarshe, Kaura ya taya Musulmi murnar Sallah, yana mai cewa hukumar za ta ci gaba da ba da kariya da taimakon gaggawa a duk lokacin da ake buƙata.


    [ad_2]

    Source link

  • Sarkin Musulmi Ya Bukaci A Sauya Fasalin Tsarin Tsaro A Yaki Da Ta’addanci

    [ad_1]

    Kungiyar Jama’atu Nasril Islam (JNI), karkashin jagorancin sarkin Musulmi, Alhaji Muhammad Sa’ad Abubakar, ta bukaci gwamnatin tarayya da ta sake fasalin tsarin tsaro tare da kayyade lokutan gudanar da ayyuka, sannan ta rika gabatar da rahoton tsaro na kowane wata kan nasarori da akasinta.

    A cikin wata sanarwa da sakatare janar na JNI, Prof. Khalid Abubakar Aliyu ya fitar, yayin da yake Allah-wadai da hare-haren bam guda uku da suka faru a Maiduguri, Sarkin Musulmi ya ce dole ne gwamnati ta dauki matakai masu tsauri kan ‘yan ta’adda.

    Sanarwar ta kuma bayyana cewa, Sarkin Musulmi ya bukaci gwamnati da ta biya diyya ga iyalan wadanda suka rasu, tare da daukar nauyin jinya gaba daya ga wadanda suka jikkata.

    [ad_2]

    Source link

  • Kasar Sin: Kashe Shugabanni Da Hare-Hare Kan Fararen Hula A Iran Abu Ne Da Ba Za A Lamunta Ba

    [ad_1]

    Ma’aikatar harkokin wajen Sin ta ce kashe shugabannin Iran da kai hare-hare kan fararen hula da kayayyakinsu, abu ne da ba za a taba lamunta ba.

    Kakakin ma’aikatar Lin Jian ne ya bayyana haka yayin da yake bayar da amsa a taron manema labarai na yau Alhamis, inda ya ce kasar Sin ta kasance mai adawa da amfani da karfi a harkokin da suka shafi dangantakar kasa da kasa. Kafin sannan, rahotanni sun sanar da mutuwar Ali Larijani, sakataren majalisar koli kan tsaron kasar Iran, sanadiyyar hare-haren Isra’ila.

    Ya kara da cewa, kasar Sin ta kadu da irin furucin da Isra’ila ta yi cewa, ta sahalewa sojojinta kai farmaki da kashe duk wani jami’in kasar Iran, ba tare da bukatar neman izini ba.

    Lin Jian ya ce kasar Sin na kira ga bangarorin da ke rikicin, su dakatar da farmakin soja nan take tare da kaucewa jefa yankin cikin yanayin da za a kasa shawo kansa.

    Har ila yau yayin taron manema labaran, Lin Jian ya yi bayani kan ziyarce-ziyarce na baya bayan nan da wakilin musammam na Sin kan yankin Gabas ta Tsakiya, Zhai Jun ya yi a wasu kasashen yankin, inda ya ce dukkan bangarorin sun yabawa matsayar rashin nuna bangaranci ta kasar Sin, da kokarinta na wanzar da zaman lafiya. Ya ce Sin babbar kasa ce da ta san ya kamata, kuma sahihiyar abokiya ga kasashen yankin Gabas ta Tsakiya. Bugu da kari, ya ce muddun rikicin ya ci gaba, to kasar Sin ma ba za ta yi kasa a gwiwa wajen ci gaba da shiga tsakani ta hanyar diflomasiyya da nufin kawo karshensa ba. (FMM)

    [ad_2]

    Source link

  • Wani abu kan Zakkatul Fidir da Sallar Idi

    [ad_1]



    A yayin da muka kammala azumin watan Ramadan, muna gabatar da wannan fadakarwa kan abubuwan da suka kamata mu yi da wadanda za mu guje musu a wannan rana ta farin ciki ta Sallah.

    Zakkar Fidir:

    Zakatul-Fitr ko Zakkar Fid-da-Kai, ita ce sadakar da ake fitarwa a karshen azumin watan Ramadan.

    Sunnah ce wajiba a kan kowane Musulmi namiji da Musulma mace, babba da yaro, da da bawa, ana so ya fitar da ita ko a fitar masa kafin zuwa Sallar Idi.

    Kuma ya halatta a fitar da ita kwana uku ko biyu ko daya kafin ranar Sallar Idi Karama don a ba fakirai da miskinadamar sarrafawa su yi farin ciki a ranar Idin.

    Mai gida zai fitar wa kansa da kananan ’ya’yansa da dukkan wadanda suke
    karkashinsa sai dai in suna da dukiyar da za su iya fitar wa kawunansu.

    Manzon Allah (SAW) ya wajabta ta a kan Musulmi kowa ya fitar da Sa’i daya (Mudun Nabiyyi hudu) na dabino ko alkama ko irin abincin da muke da su kamar shinkafa da masara da dawa da gero.

    Kuma ana raba ta ce ga miskinai (wadanda ba su mallaki abincin wuni ba) da fakirai (wadanda ba su mallaki abincin shekara ba) da sauran raunana da mabukata.

    Kuma duk wanda ya fitar kafin zuwa Idi shi ne ya yi Zakkar, wanda kuma bai fitar ba sai bayan Idi, ya yi sadaka ce kamar sauran sadakoki, hakan ya tabbata a Hadisi.

    Sallar Idi da ladubbanta:

    Malamai sun hadu cewa ta kowane hali a ranakun Idi biyu a hana yin azumi, koda na bakance ko kaffara kamar yadda Imam Annawawi ya nakalto a sharhinsa ga Sahihu Muslim. (8/15).

    Kuma sun ce, hikimar hanin ita ce idan aka yi azumin kamar an ki amincewa da liyafar da Allah Ya shirya wa bayinSa ne. (Nilul Audar, 4/262).

    Sannan Sunnah ce, a yi wanka a sanya sababbin kaya ko a wanke wadanda suka fi kyau a sa, kuma a fesa turare a fita Masallacin Idi, maza da mata manya da yara tare da tsare ladubban fitar, wato kada mata sun caba ado ko su sanya turare kuma kada a cakuda maza da mata da sauran abubuwan da shari’a ta hana.

    Ranar Sallah ranar ce ta murna da farin
    ciki da bukukuwa, to, sai dai kada wajen
    murna a wuce gona-da-iri. Kada murna
    ta sa a yi sabo. Kada murna ta sa a aikata bidi’o’in da za su vata kyawawan ayyuka.

    Wannan shi ne makasudin bijiro da wasu daga cikin ladubban da suka kamata mu yi don murnar wannan rana da masu biyo ta, kamar haka:

    1. Taya juna murna da duk lafazin da ya sauwaka, kamar “Allah Ya karba mana da makamancin haka.

    An ruwaito cewa wadansu daga magabatan kwarai suna aikata hakan. Misali Jubairu bin Nufair ya ce, “Sahabban Annabi (SAW) idan suka hadu da juna sukan ce, “Allah Ya karba mana, Ya karba muku.”

    Imam Ahmad ya ce Isnadinsa mai kyau ne, sannan Hafiz Ibn Hajar ya kyautata Isnadinsa a cikin Fathul Bari (2/517), a duba Tamamul Minnah na Albani don karin bayani.

    Kuma an ruwaito Imam Ahmad yana cewa: “Ba zan fara fada wa mutum haka ba, amma idan ya fada min zan amsa masa.”

    Shi kuma Shaihul Islam Ibn Taimiyya (Rahimahullah) ya ce, “Fara taya murna ba Sunnah ce da aka yi umarni da ita ba, kuma ba a hana ba, wanda ya aikata, ya yi koyi wanda ya ki, ya yi koyi.” Majmu’u Al Fatawa (24/253). Hakika irin wannan gaisuwa tana yin tasiri wajen karfafa zumunta da ruhin soyayya a tsakanin Musulmi.

    2. Ziyartar ’yan uwa da makusanta domin sada zumunta. Wannan mustahabbi ne a kowane lokaci, amma an fi karfafa shi a irin wannan lokaci, musamman ziyartar iyaye, domin ana sanya musu farin ciki, kuma haka cika umarnin Allah ne na a kyautata musu.

    3. Wadata abinci da abin sha: Babu laifi a wadata abinci da abin sha a wadannan ranaku ga iyalai ba tare da almubzzaranci ba, saboda Hadisin Anas a wurin Abu Dauda da Nisa’i bisa Isnadi ingantacce da ya ce: “Lokacin da Annabi (SAW) ya isa Madina, ya iske suna taruwa ranar idoji, sai ya ce, “Kuna da yini biyu da kuke wasanni a cikinsu, to, haqiqa Allah Ya musanya muku da mafiya alheri: Ranar Karamar Sallah da Ranar Layya.”

    Kuma kuyangi ko yara mata suna iya
    yin wake-waken da suka halatta, saboda Hadisin A’isha (RA) cewa, “Manzon Allah (SAW) ya shiga wurina ina tare da wadansu kuyangi biyu suna kida da waka (wadansu sun ce da shantu) sai ya kishingida a kan tabarma ya juya fuskarsa.

    Sai Abubakar (RA) ya shigo ya yi min fada ya ce “Shaidan a gidan Annabi (SAW)? Sai Manzon Allah (SAW) ya kalle shi ya ce “Kyale su-a wata ruwayar ya ce “Ya Abubakar ko wadanne mutane suna da Idi, wannan Idinmu ne.”

    Wasu bidi’o’i da ake yi lokacin bukukuwan Idi

    1. Wadansu kan kirkiro ayyuka na raya Daren Idi da ibada bisa dogaro da hadisan da ko dai masu rauni ne ko na karya.

    2. Ziyartar makabarta, wannan ya saba wa manufar Idi na nuna farin ciki da jin dadi, domin a cikin zuwa makabarta akwai nanata bakin ciki, kuma hakan ya saba wa shiriyar Manzon Allah (SAW) da ayyukan magabatan kwarai.

    3. Sai cudanya tsakanin maza da mata a lokutan bukukuwan. Wannan babbar fitina ce, mai hadari da ta wajaba shugabanni da malamai su hana, kuma ya kamata Musulmi manya da matasa su riqa jira mata su bar masallatai kafin su tashi bayan idar da Sallah.

    4. Fitar mata sanye da turare cikin ado: Abin da ya zamo wajibi shi ne mahaifa da waliyan mata su rika umartarsu da suturce jiki da sa hijabi da lizimtar ladubban fita daga gida tare da gargadinsu kan auka wa abin da zai fusata Allah. Idan ba za su tsare hukunce-hukuncen shari’a ba, to wajibi ne su hana su fita masallacin gaba daya.

    5. Sauraren kaxd-kade da wake-waken da suke haramta. Kila wadansu na iya fakewa da Hadisin kuyangi biyu su rika
    aikata abin da yake haram.

    Manzon Allah (SAW) ya ce, “Za a samu wadansu mutane a cikin al’ummata da za su rika halatta zina da alhariri da giya da wake-wake da kayayyakin kade-kade.” Wake-wake da kayayyakin kade-kaden da suka saba wa shari’a wajibi ne a guje musu.

    6. Wasa da Sallah. Babban abin bakin ciki shi ne mutane da yawa suna wasa da Sallah a cikin jama’a ko su yi barci ba su yi Sallar ba, saboda sun bata lokacinsu wajen hira ko wasanni sun gaji a ranakun Sallah.

    Allah Ka tabbatar da mu a kan imani
    da aiki nagari, Ka rayar da mu rayuwa mai tsabta, Ka riskar da mu ga salihai, Ka sanya iliminmu ya zamo don neman yadarKa da kusantarKa, mai amfanarwa ga bayinKa, Ka jibince mu a duniya da Lahira, Ka shiryar da mu zuwa ga gaskiya da izininKa, lallai Kai Kana shiryar da wanda Ka so zuwa ga tafarki madaidaici.


    [ad_2]

    Source link

  • Gwamna Bago, Ya Sha Alwashin Murƙushe ‘Yan Bindiga Da Masu Ba Su Bayanai

    [ad_1]

    Gwamnan Jihar Neja, Umar Bago, ya bayyana cewa gwamnatinsa a shirye take ta fuskanci ‘yan bindiga da masu ba su bayanai.

    Gwamnan ya bayyana hakan ne a ranar Alhamis a wani bidiyo da Gaskiya News Hausa ta wallafa, inda ya gargadi ‘yan bindiga, masu ba su bayanai da kuma masu ba su mafaka da su bayyana kansu ga hukumomin tsaro.

    • Yadda Kasar Sin Ke Tabbatar Da Babban Burinta A Aikace
    • Harin Bam: Gwamnan Yobe Ya Bayar Da Tallafin ₦10m, Ya Jajantawa Al’ummar Borno

    Kwanaki kadan da suka gabata, gwamnan ya ziyarci karamar hukumar Borgu a Jihar Neja, inda ya tattauna da Sarkin yankin kan yadda ‘yan bindiga ke kawo cikas ga harkokin ilimi da noma.

    Bago ya bayyana cewa gwamnatinsa ta samu goyon bayan gwamnatin tarayya da kuma abokan hulda na kasashen waje domin karfafa ayyukan yaki da ‘yan ta’adda.

    Ya yi takaicin yadda rashin tsaro ya yi mummunan tasiri kan ilimi da noma a jihar, yana mai cewa hare-haren ‘yan bindiga sun kawo tsaiko ga karatu da noma tare da mayar da jihar baya.

    [ad_2]

    Source link

  • An Gudanar Da Taron Tattaunawa Na Duniya Na “Sin a Yanayin Bazara” A Afirka Ta Kudu Da Jamus

    [ad_1]

    Babban rukunin gidan rediyo da talibijin kasar Sin wato CMG, ya gudanar da taron tattaunawa na duniya na “Sin a yanayin bazara: ci gaban Sin, dama ga duniya” a ranar Talata a birnin Cape Town na Afirka ta Kudu. Kuma shugaban CMG Shen Haixiong ya gabatar da jawabi ta kafar bidiyo.

    Cikin jawabin nasa Shen Haixiong ya bayyana cewa, tarukan majalisun NPC da CPPCC na kasar Sin, a matsayinsu na muhimmiyar tagar kallon kasar a sabon zamani, sun sake jawo hankalin duniya. Tarukan na bana sun zartas da muhimman takardu, kamar tsarin shirin ci gaban tattalin arziki da zamantakewar al’ummar Sin na shekaru biyar-biyar karo na 15.

    Kazalika, tsarin ci gaba mai inganci na Sin ya kuma ba da sabbin jerin damammaki ga duniya. Shugaban kasar Sin Xi Jinping, ya jaddada a lokacin wadannan taruka 2 cewa, ya kamata a kara bude kasuwar Sin ga ketare, da kuma fadada kasuwannin duniya, wanda hakan ya sake nuna cikakkiyar niyyar kasar ta “bude kofarta ga ketare bisa iyakacin kokarinta”.

    Shen Haixiong, ya kuma yi fatan CMG za ta yi amfani da karfinsa na kasancewar kafar watsa labarai ta zamani, dake sahun gaba a duniya mai hade fifikon yada labarai da kirkire-kirkire na fasaha, da kuma albarkatun kafafen yada labarai, wajen inganta sakamakon tsarin zamanantar da al’ummar Sin ta yadda zai fi amfanar da duniya baki daya.

    Ban da haka, a dai ranar ta Talata, kamfanin CMG ya gudanar da irin wannan taro a Jamus, tare da babban ofishin jakadancin Sin dake Düsseldorf, babban birnin jihar North Rhine-Westphalia. (Amina Xu)

    [ad_2]

    Source link

  • ’Yan bindiga sun kashe ’yan sanda 3 da mutum 5 a Taraba

    [ad_1]



    Wasu da ake zargin ’yan bindiga ne sun kashe ’yan sanda uku da wasu mutum biyar a Jihar Taraba.

    Harin ya faru ne a yankin Tor-Damisa, da ke Ƙaramar Hukumar Donga, inda maharan suka shiga yankin suka fara harbe-harbe.

    Mutane da dama sun tsere zuwa cikin dazuka domin tsira da rayukansu.

    ’Yan sanda sun ce sun samu kiran gaggawa, sannan suka tura jami’ai tare da sojoji zuwa wajen.

    An yi musayar wuta, kuma jami’an tsaro sun fatattaki maharan.

    Kakakin ’yan sandan jihar, ya ce jami’ai uku sun rasa rayukansu a lokacin harin, yayin da wasu suka jikkata.

    “Sun zo da yawa suka fara harbi. Mutane suka dinga gudu ta ko ina. Gaba ɗaya al’umma ta shiga cikin firgici,” in ji wani mazaunin yankin.

    ’Yan sanda sun kuma nuna alhininsu kan waɗanda aka kashe, tare da jajanta wa iyalansu.

    Har yanzu jami’an tsaro na yankin domin tabbatar da zaman lafiya.


    [ad_2]

    Source link

  • Yadda Messi Ya Jefa Kwallaye 900 A Tarihinsa Na Kwallon Kafa

    [ad_1]

    Fitaccen dan wasan kwallon kafa na kasar Argentina Lionel Messi ya zura kwallo ta 900 a tarihinsa na kwallon kafa a ranar Laraba, a wasan da Inter Miami ta buga canjaras da Nashville Fc a gasar CONCACAF, Messi mai shekaru 38, ya zura kwallo mai ban mamaki bayan mintuna bakwai kacal da fara wasan.

    Kwallon da dan wasan na Argentina ya ci itace ta 81 da ya ci tun bayan komawarsa Inter Miami daga PSG a shekarar 2023, Lionel Messi wanda ya lashe kyautar Ballon D’Or sau takwas a baya ya zura kwallaye 672 a zaman da yayi a kungiyar kwallon kafa ta Barcelona yayinda ya zura 32 ga Paris Saint-Germain ta Faransa, da kuma karin kwallaye 115 da yaci a matakin kasa da kasa da kasa ga kasar Argentina.

    • ADC Ta Buƙaci Gwamnatin Tarayya Ta Saki El-Rufai Ko Ta Gurfanar Da Shi A Kotu
    • Yadda Kasar Sin Ke Tabbatar Da Babban Burinta A Aikace

    Shekaru 21 da fara taka leda a matsayin matashin dan kwallo Messi ya buga wasanni fiye da 1000 a kungiyoyi 3 da ya zauna, wasan da Messi ya fara bugawa shine wanda Barcelona ta doke Albacete da ci 2-0 a shekarar 2005 a matsayin matashin dan wasa mai shekaru 17, duk da cewa har yanzu akwai kwallaye 65 tsakaninsa da babban abokin hamayyarshi Cristiano Ronaldo amma a matsayinsa na dan wasan tsakiya ana kallon wannan a matsayin abin burgewa.

    Ana sa ran Messi zai buga gasar cin kofin duniya na shida a wannan shekarar, lokacin da Argentina za ta kare kambunta a gasar ta bana wadda kasashe 48 za su fafata a kasashen Amurka, Kanada da Mexico, tauraron dan wasan na Argentina ya riga ya tsawaita kwantiraginsa a Inter Miami har zuwa karshen kakar wasa ta shekarar 2028.

    Messi ya zura kwallaye 672 a wasanni 778 da ya buga a tsawon shekaru 17 da ya shafe a Spain, a zaman da yayi a kungiyar PSG ta kasar Faransa, ya zura kwallaye 32 a wasanni 75, inda ya lashe kofuna uku ciki har da kofuna biyu na lig, a Inter Miami kuwa, kwallaye 81 da ya ci sun zo ne a wasanni 96 kacal, wanda ya taimaka wa kungiyar lashe Kofin League a shekarar 2023 da kuma kofin MLS na shekarar 2025, hakazalika ya zura kwallaye 115 a matakin kasa da kasa a wasanni 196, ciki har da kwallo biyu da ya zura a wasan karshe na Kofin Duniya na shekarar 2022 da aka buga a kasar Qatar.

    [ad_2]

    Source link

  • Yadda Kasar Sin Ke Tabbatar Da Babban Burinta A Aikace

    [ad_1]

    Kwanan nan, batun “yaya za a tantance nasarorin gwamnati” ya zama batu da ake yawan ambato a nan kasar Sin. Sinawa suna ta tofa albarkacin bakinsu a kan mene ne ainihin ma’anar “nasarorin gwamnati”?

    A kasar Sin, ma’aunin nasarorin gwamnati ba shi ne yadda aka furta maganganun fatar baka ba, sai dai ko an warware matsaloli.

    A lokacin zafi na shekarar 2017, Huang Ying, wacce ke rike da mukamin “shugabar kogi” watau mai kula da harkokin kogi a gundumar Qingshen da ke kogin Minjiang a lardin Sichuan dake kudu maso yammacin kasar Sin, ta kan fara aikin kowace rana da duba kogin, inda ta kan tsuguna ta shafa ciyayin cikin ruwa don tantance ingancin ruwa, sannan ta duba kowace magudanar fitar da gurbataccen ruwa da ke bakin kogin. Ba ita kadai ce ta yi wannan fafutukar ba, “shugabannin kogi” sama da miliyan 1.2 a duk fadin kasar wadanda suka fara tun daga kan shugabannin larduna har zuwa jami’an kauyuka, sun mai da babban burin “kare koguna” ya zama wasu hakikanan ayyuka kamar su “duba kogi sau daya a ko wace rana” da “tabbatar da kowace magudanar fitar da gurbataccen ruwa ta cika ma’auni”. A yanzu haka, sashen kogin Minjiang da Huang Ying ke kula da shi ba wai kawai ya kara tsabta ba, har ma an gina hanyar koren gandun daji na itatuwan gora mai tsawon kilomita 40, matakin da ya sa ya zama wurin shakatawa da jin dadin rayuwa ga mazauna wurin, kuma yana samar da kudin shiga yuan biliyan 1.6 a ko wace shekara a bangaren yawon shakatawa na al’adu. A hakika, ba a rasa samun irin labarai a kasar Sin ba.

    A takaice dai, a kasar Sin, nasarorin gwamnati ba su ne rahotanni a ofisoshi ba, a maimakon haka, sun kasance canje-canje da ke faruwa ga rayuwar jama’a, ciki har da sauya ruwan kogi daga mai datti zuwa mai tsabta, da fitowar tsirrai a cikin hamada, da kuma kara samun wadata a kauyukan da ke fama da talauci… Jama’ar kasar Sin suna bayyana ainihin “nasarorin gwamnati” ta hanyar gudanar da ayyukansu na zahiri, wanda hakan kuma ya shaida sirrin jam’iyya mai mulki a kasar wajen jagorantar jama’ar kasar don tabbatar da babban burin da ake son cimmawa. (Mai fassara Bilkisu Xin)

    [ad_2]

    Source link

  • Salla: Abba ya bai wa gidajen yari 13 kyautar shanu 14 da buhun shinkafa 82 a Kano

    [ad_1]



    Gwamnan Jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, ya bayar da tallafin shanu da kayan abinci ga fursunoni a gidajen gyaran hali 13 na jihar, domin ba su damar gudanar da shagulgulan bikin Ƙaramar Salla cikin farin ciki.

    Kayayyakin da aka raba sun haɗa da shanu 14, buhunan shinkafa 82, jarkoki 38 na man girki, da kayan miya.

    Wannan mataki an ɗauke shi ne da nufin tallafa wa walwalar fursunonin tare da sanya su jin daɗin lokacin bukukuwan salla.

    Hajiya Azumi Namadi Bebeji ce, ta miƙa kayan a madadin gwamnatin jihar.

    Ta bayyana cewa wannan tallafi shaida ce da ke nuna cewa gwamnati na kula da dukkanin ’yan ƙasa, har ma da waɗanda ke tsare a gidajen gyaran hali.

    Haka kuma, ta buƙaci fursunonin da su yi amfani da wannan lokaci na salla wajen gudanar da addu’o’in neman zaman lafiya, haɗin kai, da ci gaban Jihar Kano da ma Najeriya baki ɗaya.

    Ta kuma ƙarfafa musu gwiwa su kasance masu bin doka da oda tare da kyakkyawan fata na samun sauyi a rayuwarsu.

    Jami’in hulɗa da jama’a na Hukumar Gidajen Gyaran Hali ta Najeriya (NCoS) reshen Jihar Kano, ya bayyana cewa shugaban hukumar na jihar, Ahmed Yusuf Lakpene, ya miƙa godiyarsa ga gwamnatin jihar bisa tallafin da kuma kulawar da take nuna wa ga rayuwar fursunoni.

    Gwamnatin jihar ta sake nanata ƙudirinta na ci gaba da kula da walwalar fursunoni tare da tabbatar da adalci da jin-ƙai a gare su, musamman a lokutan bukukuwa.


    [ad_2]

    Source link