Sarkin Musulmi Ya Bukaci A Sauya Fasalin Tsarin Tsaro A Yaki Da Ta’addanci

[ad_1]

Kungiyar Jama’atu Nasril Islam (JNI), karkashin jagorancin sarkin Musulmi, Alhaji Muhammad Sa’ad Abubakar, ta bukaci gwamnatin tarayya da ta sake fasalin tsarin tsaro tare da kayyade lokutan gudanar da ayyuka, sannan ta rika gabatar da rahoton tsaro na kowane wata kan nasarori da akasinta.

A cikin wata sanarwa da sakatare janar na JNI, Prof. Khalid Abubakar Aliyu ya fitar, yayin da yake Allah-wadai da hare-haren bam guda uku da suka faru a Maiduguri, Sarkin Musulmi ya ce dole ne gwamnati ta dauki matakai masu tsauri kan ‘yan ta’adda.

Sanarwar ta kuma bayyana cewa, Sarkin Musulmi ya bukaci gwamnati da ta biya diyya ga iyalan wadanda suka rasu, tare da daukar nauyin jinya gaba daya ga wadanda suka jikkata.

[ad_2]

Source link

Similar Posts

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *