Category: Latest News

  • An ɗaure dillalin miyagun ƙwayoyi shekara 15 a Kano

    [ad_1]



    An yanke wa Jonathan Nuhu, mai shekara 45 da ke ƙauyen Kanke da ke Jihar Filato, hukuncin zaman gidan yari na tsawon shekaru 15 sakamakon samunsa da laifin mallakar tabar wiwi.

    Wannan hukunci zai fara aiki ne tun daga ranar da aka yanke shari’ar.

    Kakakin Hukumar yaƙi da fataucin miyagun ƙwayoyi ta ƙasa (NDLEA), reshen jihar Kano, Sadiq Muhammad Maigatari, ne ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya fitar ranar Laraba.

    Ya bayyana cewa Babbar Kotun Tarayya da ke Kano, ƙarƙashin jagorancin Mai Shari’a MN Yunusa, ne ya yanke hukuncin a ranar 17 ga Maris, 2026.

    Ya bayyana cewa, jami’an NDLEA sun kama Nuhu ne a ranar 20 ga Yuli, 2023, kusa da gadar Wudil da ke ƙaramar hukumar Wudil a Jihar Kano, biyo bayan cafke buhunan tabar wiwi guda 116.

    Sanarwar ta ƙara da cewa, “An gaggauta gurfanar da shi gaban kotu. Bayan shafe shekaru uku ana bincike da shari’a, kotun ta same shi da laifin tare da yanke masa hukuncin zaman gidan yari.”

    Maigatari ya ƙara da cewa, akwai bayanan da ke nuna cewa a baya ma Babbar Kotun Tarayya da ke Jihar Jigawa ta taɓa yanke wa Nuhu hukuncin shekaru 15 a gidan yari ranar 22 ga watan Yuni, 2021, kan makamancin wannan laifi.

    A lokacin da aka kama shi da sabon laifin a Kano, yana waje ne a kan belin da aka ba shi yayin da yake jiran sakamakon ɗaukaka ƙara kan shari’arsa ta farko, lamarin da ya kai ga sake yanke masa wannan sabon hukuncin.


    [ad_2]

    Source link

  • An ɗaure dillalan miyagun ƙwayoyi shekara 15 a Kano

    [ad_1]



    An yanke wa Jonathan Nuhu, mai shekara 45 da ke ƙauyen Kanke da ke Jihar Filato, hukuncin zaman gidan yari na tsawon shekaru 15 sakamakon samunsa da laifin mallakar tabar wiwi.

    Wannan hukunci zai fara aiki ne tun daga ranar da aka yanke shari’ar.

    Kakakin Hukumar yaƙi da fataucin miyagun ƙwayoyi ta ƙasa (NDLEA), reshen jihar Kano, Sadiq Muhammad Maigatari, ne ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya fitar ranar Laraba.

    Ya bayyana cewa Babbar Kotun Tarayya da ke Kano, ƙarƙashin jagorancin Mai Shari’a MN Yunusa, ne ya yanke hukuncin a ranar 17 ga Maris, 2026.

    Ya bayyana cewa, jami’an NDLEA sun kama Nuhu ne a ranar 20 ga Yuli, 2023, kusa da gadar Wudil da ke ƙaramar hukumar Wudil a Jihar Kano, biyo bayan cafke buhunan tabar wiwi guda 116.

    Sanarwar ta ƙara da cewa, “An gaggauta gurfanar da shi gaban kotu. Bayan shafe shekaru uku ana bincike da shari’a, kotun ta same shi da laifin tare da yanke masa hukuncin zaman gidan yari.”

    Maigatari ya ƙara da cewa, akwai bayanan da ke nuna cewa a baya ma Babbar Kotun Tarayya da ke Jihar Jigawa ta taɓa yanke wa Nuhu hukuncin shekaru 15 a gidan yari ranar 22 ga watan Yuni, 2021, kan makamancin wannan laifi.

    A lokacin da aka kama shi da sabon laifin a Kano, yana waje ne a kan belin da aka ba shi yayin da yake jiran sakamakon ɗaukaka ƙara kan shari’arsa ta farko, lamarin da ya kai ga sake yanke masa wannan sabon hukuncin.


    [ad_2]

    Source link

  • Salla: Farashin kayan miya ya faɗi, na kayan abinci ya yi tashin gwauron zabi a Taraba

    [ad_1]



    Mazauna Jihar Taraba na fuskantar wani sabon yanayi yayin da ake shirin bikin Ƙaramar Salla, inda farashin kayan miya da man ja ya faɗi warwas, amma farashin kayan masarufi kamar shinkafa, wake, da masara ya yi tashin gwauron zabi.

    A kasuwar Tashan Lau da ke Jalingo ta nuna cewa farashin kayan miya ya ragu, akasin yadda aka saba gani a lokutan bukukuwa inda farashi kan tashi.

    Misali, kwandon tumatir da ake sayarwa a kan Naira 6,500 a baya, yanzu ya koma Naira 4,000.

    Farashin barkono ya ragu daga Naira 60,000 zuwa Naira 40,000, yayin da buhun albasa ya sauka daga Naira 64,000 zuwa Naira 45,000.

    Wani ɗan kasuwa, Mallam Ibrahim Dan Gombe, ya bayyana cewa saukar farashin ya faru ne sakamakon yawan kayayyakin da aka shigo da su daga maƙwabtan jihohi.

    Sai dai yayin da kayan miya suka yi sauƙi, farashin hatsi da sauran kayan abinci ya ƙaru.

    Mudun shinkafar gida ya tashi daga Naira 1,600 zuwa Naira 2,200, wake ya tashi daga Naira 1,200 zuwa Naira 2,000, yayin da buhun masara mai nauyin kilo 100 ya tashi daga Naira 18,000 zuwa Naira 27,000.

    Haka kuma, tsadar rayuwa na shafar harkar sufuri, inda aka samu ƙarancin fasinjoji a tashar mota ta Jalingo, duk da cewa kuɗin mota bai sauya ba sosai.


    [ad_2]

    Source link

  • Shettima Ya Ziyarci Waɗanda Harin Bam Ya Shafa A Maiduguri

    [ad_1]

    Mataimakin Shugaban Ƙasa, Kashim Shettima, ya ce Gwamnatin Tarayya ta ƙudiri aniyar kawo ƙarshen ta’addanci tare da ɗaukar mataki mai tsauri kan waɗanda ke da hannu a hare-haren da suka faru kwanan nan.

    Ya bayyana cewa gwamnati ba wai kawai tana bai wa jami’an tsaro umarni ba ne, har ma tana ƙara samar da kayan aiki da goyon baya domin ƙarfafa yaƙi da ta’addanci.

    • Ministan Harkokin Wajen Sin: Babakere Ba Ya Samar Da Mafita
    • Sojoji Sun Ƙwato Shanun Sata A Filato

    Shettima ya bayyana haka ne a ranar Laraba a Maiduguri yayin da ya ziyarci waɗanda suka jikkata sakamakon fashewar bama-bamai da suka faru ranar Litinin, a Asibitin Koyarwa na Jami’ar Maiduguri.

    Ya yi Allah-wadai da hare-haren, inda sama da mutum 100 suka jikkata, yayin da sama da 20 suka rasu.

    Ya bayyana masu aikata harin a matsayin azzalumai, yana mai cewa babu wani dalili da zai sa a kashe mutane marasa laifi.

    Mataimakin Shugaban Ƙasan ya ce ziyarar tasa domin jajanta wa waɗanda suka jikkata da kuma iyalan waɗanda abin ya shafa.

    Ya kuma ba su tabbacin cewa gwamnati za ta tallafa musu ta hannun hukumomi kamar NEMA, Hukumar Raya Yankin Arewa maso Gabas, da kuma Gwamnatin Jihar Borno.

    Ya samu rakiyar Mataimakin Gwamnan Jihar Borno, Usman Kadafur, da sauran manyan jami’an gwamnati a yayin ziyarar.

    Ga hotunan a ƙasa:

    Shettima
    Shettima
    Shettima
    Shettima

    [ad_2]

    Source link

  • Rawar Da Sashen Ayyukan Hidimomi Da Biyan Bukatu Ke Kara Takawa A Kasar Sin

    [ad_1]

    Ci gaban tattalin arziki yana kunshe ne da muhimman abubuwa guda biyu, na farko kasuwancin kayayyaki, na biyu kuma kasuwancin ayyukan kwadago ko gudanar da hidima ko kashe kudi don biyan wata bukata (ma’ana, kamar ka ziyarci wani wuri da ba zai yiwu ka shiga ko ka yi amfani da kayan wurin ba sai ka biya kudi irin su: cibiyoyin wasanni da na nishadi da sauransu). A dukkan wadannan sassan biyu, kasar Sin ta nace ga gudanar da gyare-gyare don habaka su a turbarta ta zamanantarwa.

    A kwanan baya, kasar ta fitar da wani tsari da zai gaggauta samar da sabbin ginshikai da za su karfafa samun ci gaba wajen kara yawan kashe kudade a bangaren hidimomi da kuma biyan bukatu. Dama dai tun a ’yan shekarun da suka gabata, tsarin ingiza sayayya ya sauya daga mayar da hankali ga bangaren sayayyar kayayyaki kawai, zuwa karfafa gudunmawar da bangaren ayyukan hidimomi da biyan bukatu zai bayar ga ci gaban tattalin arziki. A halin yanzu, za a iya cewa kwalliya tana biyan kudin sabulu domin an samu karin kason kudaden da al’ummar kasar Sin ke kashewa a bangaren hidimomi da biyan bukatu, inda hakan ya mayar da sashen a matsayin daya daga cikin sabbin ginshikan samar da ci gaban tattalin arziki mai inganci.

    Daga shekarar 2020 zuwa 2025, kiyasin kudaden da kowane mutum yake kashewa a bangaren hidimomi da biyan bukatu ya karu da matsakaicin ma’auni da kaso 8.5 a cikin dari a bisa mizanin shekara-shekara. Haka nan a 2025, kudaden da aka kashe a bangaren sayayya da gudanar da hidimomi da biyan bukatu a bisa kiyasin kowane mutum sun karu da kaso 46.1, inda kuma har ila yau aka samu karuwarsu da kaso 3.5 a cikin dari a mizanin shekara-shekara.

    Bari na ba da misali da gudunmawar da bangaren biyan bukatu ke bayarwa. A tsakanin 1 ga watan Nuwambar 2025 zuwa 31 ga Janairun 2026, adadin ziyarar da aka kawo cibiyoyin wasannin kankara a fadin kasar Sin ya kai miliyan 118, ciki har da adadin ziyarar bakin da suka zo daga waje da ya kai miliyan 1 da dubu 255.

    Kazalika, kudin da aka samu a tsakanin wannan lokaci a cibiyoyin wasannin kankara da harabobinsu ya kai RMB yuan biliyan 69.15. Wannan fa a bangare guda ke nan, wanda bai kunshi lissafin na bangaren wasannin gaba daya ba, da gidajen cin abinci, da na kallon sinima, da hayar ababen hawa, da sauran cibiyoyin harkokin rayuwa. Wannan yana daya daga cikin siffofin katafariyar kasuwar kasar Sin wacce take ci gaba da samun sabbin dabaru masu habaka ci gabanta da kuma karfafa juriyar tattalin arzikin kasar, duk kuwa da yanayi na rashin tabbas da ake fama da shi a fagen kasa da kasa. (Abdulrazaq Yahuza Jere)

    [ad_2]

    Source link

  • Amfani Da Wayewar Kai Shi Ne Mafi Dacewa Wajen Samar Da Zaman Lafiya A Duniya

    [ad_1]

    Idan aka yi magana kan wayewa, wani lamari ne da ya jibanci ci gaban al’umma ta fannin al’adu, shugabanci, fasaha, birane, da kuma tsarin zamantakewar al’umma.

    Bisa ga la’akari da yadda al’amurra a duniya suke cikin halin rudani da rashin tabbas, gami da yadda ake samun sauye-sauyen lamurra a cikin sauri a duniya, ya sanya shugaba Xi Jinping na kasar Sin, ya kaddamar da wata shawara ta inganta wayewar kai a duniya a matsayin wani yunkurin diplomasiyya da nufin samar da wata dama ta musayar al’adu tsakanin al’ummomi maimakon nuna kyama ko raini tsakanin al’umma, koyon darasi daga juna maimakon fito na fito da juna, da kuma rayuwar lumana da zaman lafiya maimakon nuna girman kai, gadara ko fifiko.

    A kwanakin baya, CGTN da jami’ar Renmin ta kasar Sin suka hada gwiwa suka gudanar da bincike kan ra’ayin jama’a game da muhimmancin wannan shawara ta yin amfani da wayewar kai wajen samar da daidaito cikin lamurran duniya. An kuwa gudanar da wannan bincike ne a kan mutane 12,302 daga kasashe daban daban har 41 na duniya, inda daukacin mutanen suka yabawa wannan shawara ta inganta wayewar kai a duniya, inda suka yi amanar cewa, muhimman ginshikan wannan yunkuri da suka hada da mutunta al’adu da wayewar kan al’ummomi daban daban, assasa mutunci da kimar bil adam suna da matukar muhimmanci a wannan yanayi da duniya take ciki a halin yanzu.

    Binciken ya nuna cewa, kashi 90.8 na mutanen sun yi amannar cewa, mutunta mabambantan al’adu na al’ummomi shi ne muhimmin tafarki da ya kamata a ce duniya tana kai. Kashi 77.2 kuwa suna da ra’ayin cewa babu wata al’umma da za ta dauki wayewarta a matsayin wadda ta fi ta sauran al’ummomin duniya. Yayin da kashi 93.1 na mutane daga nahiyar Afirka da kuma kashi 90.3 na mutanen yankin kudancin America suna da ra’ayi mai karfi ma cewa duk wayewa abu daya ne.

    Kome ke nan dai, muhimmin abin da ya kamata mu lura a nan shi ne duniya na kunshe da mutane iri iri da suka sha bamban da juna, ya Allah ko ta launin fata, ko jinsi, ko harshe da dai makamantan hakan, kuma suka watsu a doron kasa, ya kuma zama wajibi a yi cudanya da juna. Domin samun kyakkyawar cudanya tsakanin irin wadannan al’ummomi, ya zama wajibi a fahimci al’adu da wayewar kan juna domin samun kyakkyawar ma’amala tsakanin juna.

    Wannan shawara ta inganta wayewar kai a duniya da Sin ta kaddamar shekaru uku da suka gabata ta kara jaddada muhimmancinta a halin da duniya take ciki yanzu. Wayewar kai shi ne abu mai muhimmanci da zai samar da zaman lafiya a duniya. Da a ce America tana amfani da wayewar kai da ba ta haddasa fitina ba a yankin gabas ta tsakiya, ko muzgunawa kasashen ta hanyar harajin cinikayya, ko ta kai hari kan wata kasa ta kama shugaban kasar ta kuma daure shi, abin da ya karya dokar kasa da kasa. Sabo da haka wayewar kai ita ce hanya mafi a’ala wajen samar da daidaiton al’amurra da zaman lafiya a duniya. Matukar babu irin wannan wayewar kai, to babu shakka rashin daidaiton lamurra, rashin hakuri, girman kai, nuna fifiko da gadara da kama karya za su yawaita a cikin al’umma. (Lawal Mamuda)

    [ad_2]

    Source link

  • Sojoji sun hallaka ’yan ta’adda sama da 61 a Borno

    [ad_1]



    Rundunar Sojin Najeriya ta Operation Hadin Kai (OPHK), tare da haɗin gwiwar Rundunar Sojin Sama (NAF), sun kashe ’yan ta’addan ISWAP sama da 61 bayan sun yi yunƙurin kai hari yankin Malam Fatori da ke Ƙaramar Hukumar Abadam a Jihar Borno.

    Majiyoyin tsaro sun bayyana cewa ’yan ta’addan sun kai harin ne da safiyar ranar Laraba.

    Sun shiga garin da ƙafa sannan suka yi amfani da jiragen sama marasa matuƙa domin ƙoƙarin karya tsaron sansanin Bataliya ta 68.

    Rahotanni sun ce maharan sun shiga ta ɓangaren Kamfanin Bravo daga yankin Duguri, amma sojoji suka yi musu ɓarin wuta.

    A cewar majiyar tsaro, sojojin da suka samu goyon bayan hare-hare ta sama sun gwabza faɗa mai tsanani da ’yan ta’addan, lamarin da ya yi sanadin mutuwar mahara da dama.

    Majiyar ta ƙara da cewa haɗin kai tsakanin sojin sama da na ƙasa ya taimaka wajen gano wuraren da ’yan ta’addan suke.

    “Mun kai hare-hare ta sama sau huɗu kan wuraren da ’yan ta’addan suka taru, wanda hakan ya rage karfinsu sosai,” in ji majiyar.

    Ta ce wannan haɗin gwiwa ya hana ’yan ta’addan zirga-zirga, tare da tilasta musu janyewa cikin ruɗani zuwa yankin Arege bayan sun ruwan wuta.

    Hakazalika, majiyoyin sun bayyana cewa jiragen yaƙin Nijar sun bayar da gudunmawa wajen ƙara matsa wa ’yan ta’addan da suka tsere, kodayake ana ci gaba da tantance asarar da suka yi.

    “Rundunar haɗin gwiwa daga Jamhuriyar Nijar ta kai farmaki cikin gaggawa don tallafa wa wannan aiki, wanda ya ƙara tsananta matsin lamba ga ’yan ta’addan,” in ji majiyar.

    Dangane da ɓangaren sojoji kuwa, an ce sojoji huɗu sun ji rauni.


    [ad_2]

    Source link

  • Ministan Harkokin Wajen Sin: Babakere Ba Ya Samar Da Mafita

    [ad_1]

    Ministan harkokin wajen kasar Sin Wang Yi, ya halarci taron ministoci na farko na tsarin tattaunawa na dabarun “3+3” na harkokin waje, da na tsaron kasa, da na tsaron jama’a tsakanin Sin da Vietnam, wanda ya gudana jiya a birnin Hanoi na kasar Vietnam, tare da jagorantar taron kwamitin jagorancin hadin gwiwa na bangarorin biyu karo na 17, sannan ya zanta da kafafen yada labarai na Sin.

    Wang Yi ya gabatar wa manema labarai halin da ake ciki game da tsarin tattaunawa na dabarun “3+3” na Sin da Vietnam, inda ya nuna cewa, bayan taron majalisar NPC da CPPCC na Sin, da kuma taron jam’iyyar kwaminis ta Vietnam karo na 14, nan take bangarorin biyu sun gudanar da taron ministoci na farko na tsarin “3+3”, wanda ya bayyana ingantacciyar dangantakar jam’iyyu da kasashen biyu bisa masu hangen nesa, kuma ya fitar da wata alama cewa, Sin da Vietnam na hada kai don kare tsaron tsarin siyasa, da kuma neman ci gaban kasa tare.

    Wang Yi ya ce, a halin yanzu, tsarin kasa da kasa yana canzawa sosai, kuma rikice-rikicen yanki suna yaduwa. Wasu manyan kasashe suna yawan yin amfani da karfi yadda suke so, wanda ke kawo babbar matsala ga zaman lafiya da kwanciyar hankali a duniya.

    Ya ce, fin nuna karfin tuwo a bangaren siyasa ba ta da mafita, kuma babakre ba ya samun goyon bayan jama’a. Sin a matsayinta na muhimmiyar karfin tabbatar da zaman lafiya, da karfin kawo kwanciyar hankali, da kuma karfin nuna adalci a duniya, tana son yin hadin gwiwa da Vietnam da sauran kasashe don gaggauta gina al’ummar Asiya-Pacific ta bai daya, da kuma ba da misali kan gina kyakkyawar makomar bil-Adam ta bai daya. (Amina Xu)

    [ad_2]

    Source link

  • Harin Bam: Gwamnan Yobe Ya Bayar Da Tallafin ₦10m, Ya Jajantawa Al’ummar Borno

    [ad_1]

    Gwamnan Jihar Yobe, Mai Mala Buni, a ranar Laraba ya jajanta wa gwamnati da al’ummar Jihar Borno, da kuma iyalan waɗanda suka rasa rayukansu sakamakon hare-haren bama-bamai da suka afku a Maiduguri, waɗanda suka yi sanadiyyar mutuwar sama da mutane 23.

    Buni, wanda a halin yanzu yake Makka yana gudanar da aikin Umrah, mataimakinsa, Idi Gubana, ne ya wakilce shi yayin ziyarar jaje da aka kai babban birnin Jihar Borno.

    Gwamnan ya kuma jajanta wa waɗanda suka jikkata a hare-haren, yana mai nuna alhini cewa, mutanen da basu ji basu gani ba, su hare-haren ya rutsa da su.

    A cikin saƙon da mataimakinsa ya gabatar, Buni ya bayyana lamarin a matsayin abin takaici da rashin hankali, yana jaddada cewa Jihar Yobe tana tare da Jihar Borno cikin wannan alhini.

    [ad_2]

    Source link

  • Masanan Afirka: Shirin Shekaru Biyar-biyar Na Kasar Sin Karo Na 15 Ya Ba Da Sabbin Damammaki Na Ci Gaba Ga Afirka

    [ad_1]

    Shirin raya ci gaban kasa na shekaru biyar-biyar na kasar Sin karo na 15 da aka amince da shi a kwanan nan, ya samar da damammakin da kasashen Afirka za su iya amfani da su yayin da suke bin hanyoyinsu na samun ci gaba, kamar yadda manazarta suka bayyana a wani taron kara wa juna sani da aka gudanar a Kampala jiya Talata.

    Taron, wanda aka gudanar bisa taken “Dabarun daidaita sahu don samun wadata: Zurfafa alakar da ke tsakanin Sin da Uganda a cikin shirin shekaru biyar-biyar karo na 15,” ya samu halartar masu bincike, masana ilimi da kuma jami’an gwamnati. Cibiyar kwararrun masu nazari da ke sa-ido kan ci gaba, watau DWC da ke Uganda ce ta shirya taron.

    Wani mai bincike na cibiyar DWC Arthur Atuha, ya bayyana cewa kasashe kamar Uganda za su iya cin gajiyar zurfafan fasahohin kimiyya da kirkire-kirkire na kasar Sin wajen sarrafa kayayyaki cikin hanzari domin kaiwa kasuwar kasar Sin.

    Kazalika, shi ma wani mai bincike a cibiyar binciken kimiyyar dan Adam ta Afirka ta Kudu Vuyo Mjimba, ya bayyana cewa shirin na shekaru biyar-biyar na kasar Sin karo na 15 ya nuna muhimmancin yadda kasashen Afirka za su ci gaba da dagewa wajen ba da fifiko ga ci gaban kansu, maimakon dogaro da tsare-tsaren wasu daga waje.

    Har ila yau a nasa bangaren, wani jami’in bincike a cibiyar DWC Joshua Kingdom, ya bayyana cewa kasar Sin ta riga ta aza harsashi a yankin Afirka domin zurfafa cudanyar kasuwanci a yayin da take habaka zamanantarwa da kuma samun ci gaba mai inganci a matakin koli. Ya kara da cewa, a karkashin shawarar Ziri Daya da Hanya Daya, watau BRI a takaice, kasar Sin ta ba da goyon baya ga gina muhimman kayayyakin more rayuwa na makamashi da sufuri, wadanda za su iya taimaka wa kasashen Afirka wajen yin amfani da damammakin da suka samu.

    Sannan, Mai fashin baki a fannin tattalin arziki dan asalin kasar Guinea-Bissau Afonso Gomes ya bayyana cewa, manufar da kasar Sin ta sanar ta yafe harajin fito kan hajojin kasashen Afirka 53 da ake shigarwa kasar Sin, za ta haifar da wani sabon mafari na yaukaka alakar Sin da kasashen nahiyar Afirka, kuma hakan zai kara karfafa hadin gwiwa tsakanin kasashe masu tasowa. Mr. Afonso Gomes ya bayyana hakan ne yayin wata tattaunawar baya bayan nan da kamfanin dillancin labarai na kasar Sin Xinhua.

    Gomes ya ce, manufofin kasar Sin sun dace da aniyar kasar ta goyon bayan cudanyar mabambantan sassa, da zurfafa hadin gwiwa da kasashen Afirka. Ya ce hakan zai bude sabbin damammaki ga kasashen nahiyar Afirka na fitar da karin hajoji da aka karawa inganci, da samar da guraben ayyukan yi a gida da fadada kudaden shigarsu. Kazalika, manufar za ta taimakawa kasashen Afirka da damar rage fatara, da karfafa ikon nahiyar na cimma dogaro da kai ta fuskar tattalin arziki.

    Mista Gomes ya kara da cewa kasar Guinea-Bissau, wadda akasarin kayayyakin da take fitarwa na albarkatun gona ne, irinsu gyadar yazawa ko “cashew nuts”, na iya amfani da wannan zarafi wajen fadada, da ingiza sarrafa kayayyaki a cikin gida.

    A mataki na shiyya kuwa, Gomes ya yi kira da a karfafa, da tsara salon tattaunawa a hukumance, tsakanin kasashe membobin kungiyar raya tattalin arzikin yammacin Afirka ko ECOWAS da bangaren Sin, ta yadda hakan zai taimaka wajen daidaita mizanin ingancin hajoji da bunkasa cinikayya. (Saminu Alhassan, Abdulrazaq Yahuz Jere)

    [ad_2]

    Source link