Category: Latest News

  • Ramadan: Gwamnan Jigawa Ya Yafewa Fursunoni 12 Kafin Sallah

    [ad_1]

    Gwamnan Jihar Jigawa, Umar Namadi, ya yafewa fursunoni 12 da aka yankewa hukunci a wani mataki na jin ƙai a cikin watan Ramadan da kuma shirin bikin Sallah.

    Sanarwar da Babban Lauyan Jihar kuma Kwamishinan Shari’a, Bello Fanini, ya fitar ta ce an dauki matakin ne bisa shawarwarin Kwamitin Ba da Afuwa na Jihar Jigawa, da kuma tanadin kundin tsarin mulki na shekarar 1999.

    • Gwamnatin Jigawa Na Ƙoƙarin Ganin DSS Ta Saki Walida — Umar Namadi
    • Zargi: Yadda Amarya Ta Kashe Mijinta Da Gubar Ɓera A Jigawa

    Daga cikin waɗanda aka yi wa afuwar akwai Ibrahim Adamu Isa, Sa’idu Umar, Adamu Musa, Habibu Musa, Yusuf Ahmed, Shu’aibu Adamu, Abdullahi Ya’u, Yahaya Jana’u, Abdul Hamisu, Garba Miko, Salisu Isa da Aliyu Ibrahim.

    Gwamnatin ta ce matakin na nuna ƙudirin ta na inganta zaman lafiya, sulhu da kuma haɗin kan al’umma, tare da bai wa waɗanda aka yafewa damar komawa cikin al’umma.

    Haka kuma an buƙaci waɗanda aka yi wa afuwar su kasance masu halin kirki, su guji aikata laifi a nan gaba, yayin da aka roƙi al’umma su karɓe su tare da taimaka musu wajen farfaɗo da rayuwarsu.

    [ad_2]

    Source link

  • Ban yi nadamar abubuwan da na yi lokacin da nake minista ba — Malami

    [ad_1]



    Tsohon Ministan Shari’a, Abubakar Malami, ya ce bai yi nadama kan duk abin da ya yi lokacin da yake riƙe da muƙami ba.

    Ya kuma bayyana cewa a shirye yake ya kare kansa a gaban kotu kan tuhumar da ake masa.

    Ana tuhumar Malami tare da matarsa Asabe da ɗansa Abdulaziz da laifuka guda 16 da suka shafi zargin almundahanar kuɗi.

    Hukumar EFCC cw ta gurfanar da su a gaban kotu kan tuhume-tuhumen, sai dai dukkaninsu sun musanta zarge-zargen.

    A wata hira da ya yi, Malami ya ce zamansa a tsare a hannun EFCC, da zaman gidan yarin Kuje, da kuma hannun DSS, wani ɓangare ne na rayuwarsa.

    Ya ce yana ganin komai yana cikin nufin Allah, amma duk da haka zai kare kansa a kotu.

    Idan ba a manta ba kotu ta bayar sa belinsa, amma daga bisani jami’an DSS suka sake kama shi a ranar 19 ga watan Janairu.

    Ya kuma koka cewa ba a ba shi damar ganin iyalansa da lauyoyinsa ba yayin da yake tsare.

    A ranar 27 ga watan Fabrairu, wata Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja ta ba da belinsa shi da ɗansa kan kuɗi Naira miliyan 200 kowannensu kan wasu zarge-zarge daban.

    Sun cika sharuɗan belin kuma yanzu haka an sake su.

    Malami, ya kuma zargi hukumomin tsaro da take masa haƙƙinsa.

    Ya ce sun binciki gidajensa da wuraren kasuwancinsa ba tare da sanar da shi ba, wanda ya ce hakan ya saɓa da doka.

    Duk da wannan shari’a da ake yi, Malami ya jaddada cewa yana tsaye kan ra’ayinsa a kan duk abin da ya yi a lokacin da yake minista, kuma bai yi wata nadama ba.


    [ad_2]

    Source link

  • Kotu Ta Yanke Hukuncin Shekara 15 Ga Wani Mai Safarar Miyagun Ƙwayoyi A Kano

    [ad_1]

    Hukumar NDLEA ta samu nasarar gurfanar da wani da ake zargi da safarar miyagun ƙwayoyi, Jonathan Nuhu, wanda wata Babbar Kotun Tarayya da ke Kano ta yanke masa hukuncin ɗaurin shekaru 15 bisa samunsa da laifin mallakar tabar wiwi ba bisa ƙa’ida ba.

    A wata sanarwa da kakakin hukumar a Kano, Sadiq Muhammad Maigatari, ya fitar, ya ce Mai shari’a M.N. Yunusa ne ya yanke hukuncin a ranar 17 ga Maris, 2026, inda ya yankewa mutumin mai shekaru 45 ɗan asalin Jihar Filato hukuncin.

    • NDLEA Ta Kama Tsoho Da Yunƙurin Safarar Hodar Iblis A Filin Jirgin Sama Na Abuja
    • Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 9 A Wurin Shaƙatawa A Filato

    Sanarwar ta ce jami’an NDLEA sun kama Jonathan ne a ranar 20 ga Yuli, 2023, a kusa da gadar Wudil a ƙaramar hukumar Wudil ta Jihar Kano, inda aka same shi da buhuna 116 na tabar wiwi.

    An gurfanar da shi a gaban kotu, kuma bayan shari’a da bincike na tsawon shekaru uku, kotun ta same shi da laifi tare da yanke masa hukuncin ɗaurin shekaru 15 a gidan yari.

    Hukumar ta kuma bayyana cewa Jonathan Nuhu ya taɓa samun irin wannan hukunci a Jihar Jigawa a shekarar 2021 kan laifi makamancin wannan, duk da cewa yana kan beli kafin a sake kama shi, inda ta jaddada ƙudirinta na ci gaba da cafke wa da gurfanar da masu aikata irin waɗannan laifuka.

    [ad_2]

    Source link

  • An kashe manyan Kwamandojin Boko Haram 3 a Borno

    [ad_1]



    Dakaru na rundunar sojojinhaɗin gwiwa na Arewa maso Gabas, Operation HADIN KAI, sun kashe wasu manyan kwamandojin Boko Haram/ISWAP uku a lokacin wani harin ta’addanci da bai yi nasara ba a Mallam Fatori.

    Kamar yadda majiyar tsaro ke cewa, wannan farmaki ya faru ne a safiyar ranar Laraba lokacin da ‘yan ta’adda suka yi yunƙurin kai hari kan sansanonin sojoji.

    Sojojin sun ce, an kashe ‘yan ta’adda sama da 80 a lokacin fafatawar.

    Daga cikin waɗanda aka kashe akwai manyan kwamandoji uku da aka bayyana sunayen su Mallam Abdulrahman Gobara da Mallam Ba Yuram da Abou Ayyuba.

    Sojojin sun ce kwamandojin sun taka muhimmiyar rawa wajen tsarawa da kuma jagorantar harin.

    An kuma kashe wasu sanannun mayaƙa da dama a lokacin samamen da aka ɗauki lokaci ana fafatawa.

    Majiyar na cigaba da cewar, cikin sanannun mayaƙan da aka halaka Sun haɗa da: Zarkawi, Ba Bunu da Rawa Fannami da Abowor Suwurti da Bulama Mil da Abu Aisha da Suleimana da Abu Rijal da Abu Ali da Abba Gana Kawiyya da kuma Ahmodu Hirasama da sauran su.

    Dakarun sojojin sun fafata da maharan da ƙarfin bindiga da kuma goyon baya da suka samu daga dakarun sama na rundunar sojan ta OPHK.

    Sojojin sun ce ‘yan tawayen sun ci gaba da tafiya a ƙafa kuma sun tura jiragen sama marasa matuƙa don su karya kariyar da dakarun sojan ke da shi.

    Majiyar tsaron na cewa, tunda ma dakarun sojan sun yi tsammanin harin kuma sun mayar da martani da dabarun kariya da aka shirya.

    Haka nan an ƙarfafa aikin ta hanyar tallafin jiragen saman yaƙi na jumhuriyar Nijar.

    A cewar majiyar an ƙwato makamai da harsasai daga wurin bayan fafatawar.


    [ad_2]

    Source link

  • EFCC ta kama mutum uku da ake zargi da haƙar zinare a Borno

    [ad_1]



    Jami’an Hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa ta Najeriya EFCC reshen jihar Borno a Maiduguri sun kama mutane uku da ake zargi da haƙar zinare ba bisa ƙa’ida ba a jihar.

    Hukumar EFCC ta bayyana hakan a cikin wata sanarwa a ranar Talata, 17 ga Maris, 2026, inda ta bayyana cewa an kama mutanen ne a garin Malam Jakwa, cikin ƙaramar hukumar Hawul, bayan samun sahihan bayanai kan ayyukansu.

    An gano waɗanda ake zargin da suka haɗa da: Umar Muhammad da Modu Bamai Umar da Sani Samaila.

    A cewar hukumar EFCC, zargin da ake yi musu na haƙar zinare ba bisa ƙa’ida ba yana haifar da rashin tsaro da lalata muhalli a jihar.

    Sanarwar ta ce, “An kama waɗanda ake zargin ne bayan samun sahihan bayanai kan ayyukan haƙar zinare da suka aikata ba bisa ƙa’ida ba.”

    Kayayyakin da aka samu daga gare su sun haɗa da: ƙaramin injin auna zinare da adadin zinare da aka haƙo.

    EFCC ta ce za a gurfanar da waɗanda ake zargin a gaban kotu bayan kammala bincike don ya zama izina ga wasu masu ƙudirin irin na su.


    [ad_2]

    Source link

  • APC Ta Musanta Zargin Aikata Cin Hanci, Ta Bai Wa NNPP Sa’o’i 72 Ta Ba Da Haƙuri

    [ad_1]

    Jam’iyyar APC ta yi watsi da zargin da tsagin Kwankwasiyya na NNPP ya yi cewa gwamnatin Jihar Kano na tsoma baki a harkokin kotu.

    A wata sanarwa da kakakin jam’iyyar, Auwalu Soja Gwale, ya fitar, APC ta ce zargin ba gaskiya ba ne kuma babu hujja a kansa.

    • ADC Ta Buƙaci Gwamnatin Tarayya Ta Saki El-Rufai Ko Ta Gurfanar Da Shi A Kotu
    • Adadin Mayaƙan ISWAP Da Aka Kashe A Borno Ya Kai 75

    Jam’iyyar ta kuma musanta rahotannin cewa an biya kuɗi domin yin tasiri a wata kotu da ke Abuja.

    APC ta bai wa NNPP da kakakinta, Ibrahim Karaye, wa’adin awanni 72 su janye zargin tare da neman afuwa, ko kuma su fuskanci matakin shari’a.

    APC ta ce an yi hakan ne domin ɓata sunan ɓangaren shari’a.

    Ta jaddada cewa gwamnatin Jihar Kano ba ta taɓa tsoma baki a harkokin kotu ba.

    Jam’iyyar ta kuma zargi ɓangaren NNPP da yawan yin irin waɗannan kalamai a duk lokacin da abubuwa ba su tafi yadda suke so ba.

    Ta buƙace su da su mayar da hankali wajen magance rikice-rikicen cikin gida maimakon yin zarge-zarge marasa tushe.

    [ad_2]

    Source link

  • Malami da mabiyansa sun yi sallar Idi a Sakkwato

    [ad_1]



    Wani malamin addinin Musulunci mazaunin Sakkwato, Sheikh Musa Lukuwa a ranar Alhamis ya jagoranci mabiyansa wajen gudanar da Sallar Idul-Fitr, a matsayin ƙalubale ga umarnin da Sarkin Musulmi ya bayar, wanda ya ayyana ranar Juma’a a matsayin ranar Sallah a hukumance.

    Malamin ya gudanar da Sallar Idi raƙa’a biyu a masallatinsa da ke Mabera da misalin ƙarfe 9:10 na safe, bayan da rahotanni suka bayyana cewa ya yi wa mabiyansa jawabi sa’o’i kaɗan bayan sanarwar da Sarkin Musulmi ya yi na cewa ba a ga jinjirin watan Shawwal ba a ko’ina a Najeriya.

    A wani saƙo da ya karaɗe kafafen sada zumunta na zamani , Lukuwa ya bayyana dalilinsa na yin hakan da cewa akwai ingantattun rahotannin ganin wata a maƙwabciyar ƙasar, Jamhuriyar Nijar.

    A cewarsa, wasu mutane da ya amince da su a ƙasar sun tabbatar da ganin watan, wanda hakan ya sa ƙungiyarsa ta ci gaba da gudanar da bikin Sallah.

    “Jamhuriyar Nijar tana kusa da mu sosai—kimanin kilomita 100 ne tsakaninmu,” in ji shi. “Idan muna karɓar rahotanni daga birane kamar Kano ko ma Legas, waɗanda suke da nisa sosai, babu dalilin da zai sa mu ƙi amincewa da tabbacin ganin wata daga maƙwabciyar ƙasa.”

    Ya jaddada cewa wannan mataki ba na nuna rashin mutunta hukuncin Sarkin Musulmi ba ne, ko ƙin bin koyarwar addini ne.

    “Yawancin lokaci muna bin umarnin Sarkin Musulmi wajen fara azumi da ƙare shi. Sai dai idan ya fito fili cewa an ga wata, dole ne mu yi aiki da koyarwar Manzo (SAW), koda kuwa hakan ya saɓa wa sanarwar Sarkin Musulmi,” in ji shi.

    Lukuwa ya kuma ya yi misali da irin rawar da marigayi Abubakar Mahmoud Gumi ya taka a baya wajen sanar da ganin wata kafin a tattara wannan alhaki a hannun Sarkin Musulmi domin haɗin kan al’ummar Musulmi.

    Ya bayyana cewa shawarar da Sarkin Musulmi ya yanke a wannan karon ba daidai ba ce, kuma ya dage kan cewa mabiyansa ba za su bi wannan umarni ba.


    [ad_2]

    Source link

  • ADC Ta Buƙaci Gwamnatin Tarayya Ta Saki El-Rufai Ko Ta Gurfanar Da Shi A Kotu

    [ad_1]

    Jam’iyyar ADC ta buƙaci gwamnatin Nijeriya da ta saki Nasir El-Rufai nan take ko kuma ta gurfanar da shi a gaban kotu ba tare da ɓata lokaci ba.

    A wata sanarwa da kakakin jam’iyyar, Bolaji Abdullahi, ya fitar, jam’iyyar ta ce tsare shi ba tare da shari’a ba ya saɓa wa doka kuma yana barazana ga dimokuraɗiyya.

    • Ministan Harkokin Wajen Sin: Babakere Ba Ya Samar Da Mafita
    • CAF Ta Soke Nasarar Senegal, Ta Ayyaṇa Morocco A Matsayin Zakarar AFCON Ta 2025

    ADC ta kuma soki gwamnatin Bola Tinubu, tana mai cewa lamarin na haifar da tambayoyi kan mutunta haƙƙin ɗan Adam da bin doka.

    Jam’iyyar ta jaddada cewa ‘yanci haƙƙi ne da kundin tsarin mulki ya tanada, ba wani abu ba ne da gwamnati ke bayarwa ko karɓa yadda ta ga dama ba.

    Haka kuma ta buƙaci gwamnati da jami’an da abin ya shafa, ciki har da Nuhu Ribadu, da su bi doka tare da mutunta haƙƙin ‘yan ƙasa.

    [ad_2]

    Source link

  • Mahaifi ya rasa ’ya’yansa 4 a fashewar bama-bamai a Maiduguri

    [ad_1]



    Wani mutum ya rasa ’ya’yansa maza huɗu a jerin fashewar bama-bamai da suka girgiza Maiduguri, babban birnin Jihar Borno a ranar Litinin, kamar yadda jaridar Aminiya ta gano.

    Fashewar, waɗanda suka afku a ƙofar shiga Asibitin Koyarwa na Jami’ar Maiduguri (UMTH), da yankin Monday Market da kuma yankin Post Office, sun yi sanadin mutuwar mutane kusan 27 yayin da wasu da dama suka jikkata.

    Wani ɗan kasuwa, Usman Lawan ya bayyana yadda maƙwabcinsa, Ba Musa, wanda ke zaune a Gwange Sabon Layi, ya rasa ‘ya’yansa huɗu a lamarin.

    Ya ce yaran sun faɗa cikin hatsarin ne sa’ilin da suka je sayen tabarau na bikin Sallah.

    Yayin da yake magana da wakilinmu lokacin ziyarar Mataimakin Shugaban Kasa Kashim Shettima ya ziyarci a asibitin UMTH, ya ce:

    “Muna gama buɗa baki, ina tura kurar itace sai fashewar ta auku, na tsinci kaina kawai a asibiti. Na rasa komai nawa a wannan harin.”

    “Ya saya musu sabbin kaya da takalma, sai suka zo wurinmu don sayen tabarau na bikin Sallah. Fashewar ta kashe su duka. An binne su jiya,” in ji shi.

    Wani mai gadi a asibitin, wanda ya samu raunuka a hannunsa da kafafunsa, ya shaida wa BBC yadda lamarin ya faru:

    “Ina zaune a wajen asibitin sai mutane uku suka zo kan babur. Na lura da wani abu da ban amince masa ba, sai na ce su tafi. Sun dawo karo na biyu, sa’ad da na ƙi barinsu su shiga, sai suka jefa mini wani kwanon abinci. Ya buge ni a hannu ya faɗi ƙasa, yana barazanar fashewa. Na kwanta sai na ji ƙara mai ƙarfi. Yayin da nake ƙoƙarin guduwa ciki, wani kwanon ya sake fashewa ya buge ni a kafa,” in ji shi.

    Wata matar da ta tsira, wadda ta rasa ɗiyarta a fashewar, ta ce: “Muna isowa asibitin sai bam ɗin ya tashi. Na faɗi, ita kuma ɗiyata ta faɗi matacciya. Kanta ya fashe. Suka kai ni ciki suka faɗa mini ta rasu. Na yi addu’a ga Allah domin Shi ne ya ɗauki abarsa. Mahaifinta ya rasu tun tana jaririya ’yar wata biyar.”


    [ad_2]

    Source link

  • Adadin Mayaƙan ISWAP Da Aka Kashe A Borno Ya Kai 75

    [ad_1]

    Adadin mayaƙan ISWAP da aka kashe yayin wani hari a Jihar Borno ya ƙaru zuwa 75.

    ‘Yan ta’addan sun yi yunƙurin kai hari kan sojojin Nijeriya a Malam Fatori, ƙaramar hukumar Abadam, da safiyar ranar Laraba, amma sojojin sun daƙile harin.

    • Rawar Da Sashen Ayyukan Hidimomi Da Biyan Bukatu Ke Kara Takawa A Kasar Sin
    • Ramadan: Lokutan Buda-Baki Da Sahur Na Azumi Na 29

    Da farko an ce an kashe mutum 61, amma daga baya an tabbatar da cewa aƙalla mayaƙa 75 aka kashe, yayin da wasu suka tsere da munanan raunuka.

    Sojojin tare da haɗin gwiwar rundunar sojin saman Nijeriya sun gano harin da wuri tare da mayar da martani cikin gaggawa.

    An kuma kai hare-hare ta sama kan waɗanda suka gudu, wanda ya ƙara jawo musu asara.

    Haka kuma, rundunar sojin saman Jamhuriyar Nijar ta taimaka wajen kai hare-hare kan ‘yan ta’addan da ke tserewa.

    Jami’an tsaro sun kuma ƙwato makamai da alburusai da dama daga wajen, wanda ya ƙara rage ƙarfin ƙungiyar a yankin.

    A ɓangaren sojoji, an jikkata sojoji huɗu amma ana kula da su kuma suna cikin ƙoshin lafiya.

    [ad_2]

    Source link