An kashe manyan Kwamandojin Boko Haram 3 a Borno

[ad_1]



Dakaru na rundunar sojojinhaɗin gwiwa na Arewa maso Gabas, Operation HADIN KAI, sun kashe wasu manyan kwamandojin Boko Haram/ISWAP uku a lokacin wani harin ta’addanci da bai yi nasara ba a Mallam Fatori.

Kamar yadda majiyar tsaro ke cewa, wannan farmaki ya faru ne a safiyar ranar Laraba lokacin da ‘yan ta’adda suka yi yunƙurin kai hari kan sansanonin sojoji.

Sojojin sun ce, an kashe ‘yan ta’adda sama da 80 a lokacin fafatawar.

Daga cikin waɗanda aka kashe akwai manyan kwamandoji uku da aka bayyana sunayen su Mallam Abdulrahman Gobara da Mallam Ba Yuram da Abou Ayyuba.

Sojojin sun ce kwamandojin sun taka muhimmiyar rawa wajen tsarawa da kuma jagorantar harin.

An kuma kashe wasu sanannun mayaƙa da dama a lokacin samamen da aka ɗauki lokaci ana fafatawa.

Majiyar na cigaba da cewar, cikin sanannun mayaƙan da aka halaka Sun haɗa da: Zarkawi, Ba Bunu da Rawa Fannami da Abowor Suwurti da Bulama Mil da Abu Aisha da Suleimana da Abu Rijal da Abu Ali da Abba Gana Kawiyya da kuma Ahmodu Hirasama da sauran su.

Dakarun sojojin sun fafata da maharan da ƙarfin bindiga da kuma goyon baya da suka samu daga dakarun sama na rundunar sojan ta OPHK.

Sojojin sun ce ‘yan tawayen sun ci gaba da tafiya a ƙafa kuma sun tura jiragen sama marasa matuƙa don su karya kariyar da dakarun sojan ke da shi.

Majiyar tsaron na cewa, tunda ma dakarun sojan sun yi tsammanin harin kuma sun mayar da martani da dabarun kariya da aka shirya.

Haka nan an ƙarfafa aikin ta hanyar tallafin jiragen saman yaƙi na jumhuriyar Nijar.

A cewar majiyar an ƙwato makamai da harsasai daga wurin bayan fafatawar.


[ad_2]

Source link

Similar Posts

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *