Mahaifi ya rasa ’ya’yansa 4 a fashewar bama-bamai a Maiduguri
[ad_1]
Wani mutum ya rasa ’ya’yansa maza huɗu a jerin fashewar bama-bamai da suka girgiza Maiduguri, babban birnin Jihar Borno a ranar Litinin, kamar yadda jaridar Aminiya ta gano.
Fashewar, waɗanda suka afku a ƙofar shiga Asibitin Koyarwa na Jami’ar Maiduguri (UMTH), da yankin Monday Market da kuma yankin Post Office, sun yi sanadin mutuwar mutane kusan 27 yayin da wasu da dama suka jikkata.
Wani ɗan kasuwa, Usman Lawan ya bayyana yadda maƙwabcinsa, Ba Musa, wanda ke zaune a Gwange Sabon Layi, ya rasa ‘ya’yansa huɗu a lamarin.
Ya ce yaran sun faɗa cikin hatsarin ne sa’ilin da suka je sayen tabarau na bikin Sallah.
Yayin da yake magana da wakilinmu lokacin ziyarar Mataimakin Shugaban Kasa Kashim Shettima ya ziyarci a asibitin UMTH, ya ce:
“Muna gama buɗa baki, ina tura kurar itace sai fashewar ta auku, na tsinci kaina kawai a asibiti. Na rasa komai nawa a wannan harin.”
“Ya saya musu sabbin kaya da takalma, sai suka zo wurinmu don sayen tabarau na bikin Sallah. Fashewar ta kashe su duka. An binne su jiya,” in ji shi.
Wani mai gadi a asibitin, wanda ya samu raunuka a hannunsa da kafafunsa, ya shaida wa BBC yadda lamarin ya faru:
“Ina zaune a wajen asibitin sai mutane uku suka zo kan babur. Na lura da wani abu da ban amince masa ba, sai na ce su tafi. Sun dawo karo na biyu, sa’ad da na ƙi barinsu su shiga, sai suka jefa mini wani kwanon abinci. Ya buge ni a hannu ya faɗi ƙasa, yana barazanar fashewa. Na kwanta sai na ji ƙara mai ƙarfi. Yayin da nake ƙoƙarin guduwa ciki, wani kwanon ya sake fashewa ya buge ni a kafa,” in ji shi.
Wata matar da ta tsira, wadda ta rasa ɗiyarta a fashewar, ta ce: “Muna isowa asibitin sai bam ɗin ya tashi. Na faɗi, ita kuma ɗiyata ta faɗi matacciya. Kanta ya fashe. Suka kai ni ciki suka faɗa mini ta rasu. Na yi addu’a ga Allah domin Shi ne ya ɗauki abarsa. Mahaifinta ya rasu tun tana jaririya ’yar wata biyar.”
Masu alaƙa
[ad_2]
Source link