An Maka Gwamnatin Tarayya A Kotu Kan Aiwatar Da Dokar Haraji
[ad_1]
An kai Gwamnatin Tarayya gaban Babbar Kotun Babban Birnin Tarayya (FCT) kan shirinta na fara aiwatar da sabbin dokokin haraji daga ranar 1 ga Janairu, 2026. Masu shigar da ƙarar su ne ƙungiyar amintattu masu rajin bincikar masu riƙe da madafun iko (Ƙaddamar da Amintattu na Ƙaddamarwar Afirka don Zaluntar Jama’a).
Masu ƙarar sun roƙi kotu ta bayar da umarnin dakatar da aiwatar da dokokin harajin har sai an saurari ƙarar gaba ɗaya kuma an yanke hukunci a kai. Waɗanda ake ƙara sun haɗa da gwamnatin tarayya, da Shugaban Ƙasa, da Antoni Janar na Tarayya, da Shugaban Majalisar Dattawa, da Kakakin Majalisar Wakilai da Hukumar Gudanarwar Majalisar Tarayya.
- ‘Yan Majalisar Wakilai Sun Nemi A Dakatar Da Aiwatar Da Dokokin Haraji
- Lambobin NIN Da CAC Za Su Zama Lambobin Biyan Haraji Daga 2026— FIRS
A wata buƙata ta gaggawa (Motion Exparte), masu ƙarar sun nemi umarnin wucin gadi na hana gwamnati ci gaba da aiwatar da dokokin, tare da buƙatar a hanzarta sauraro da yanke hukunci kan ƙarar.
Sai dai kotun ta ɗage yanke hukunci kan buƙatar gaggawar zuwa ranar 5 ga Janairu, 2026.
[ad_2]
Source link