Amurka Ta Yi Watsi Da Nadin Mojtaba Khamenei’ Sabon Shugaban Iran
[ad_1]
Kamfanin dillancin labaran Reuters, ya ba da rahoton cewa; a ranar Litinin da ta gabata ne, kasar Iran ta nada Mojtaba Khamenei, a matsayin wanda zai gaji mahaifinsa, Ali Khamenei, a matsayin shugaban koli.
Hakan na nuni da cewa, masu tsattsauran ra’ayi za su ci gaba da rike madafun iko a Tehran, a rikicin da suke yi da Amurka da Isra’ila.
- Za a Gudanar Da Tattaunawa Kan Batun Tattalin Arziki Da Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka a Faransa Daga Ranar 14 Zuwa 17 Ga Watan Maris
- Arsenal Na Tattaunawa Da Declan Rice Kan Tsawaita Kwantiraginsa A Ƙungiyar
Mojtaba, malami ne mai matsakaicin matsayi tare da tasiri a cikin jami’an tsaron kasar Iran da kuma manyan hanyoyin kasuwanci a karkashin mahaifinsa, ana kallonsa a matsayin wanda ke kan gaba a zaben da majalisar ta yi, kungiyar malamai 88 da suka aiwatar da zaben sabon shugaban, bayan Ali Khamenei.
A cikin wata sanarwa da majalisar ta fitar bayan tsakar daren ranar Litinin a birnin Tehran na kasar Iran ta ce; ta hanyar kuri’ar da aka kada, majalisar kwararru ta nada Ayatollah Sayyid Mojtaba Hosseini Khamenei a matsayin shugaban tsarin Jamhuriyar Musulunci ta Iran na uku.
Matsayin ya bai wa Mojtaba matsayi na koli a dukkan lamurran da suka shafi tsarin Jamhuriyar Musulunci.
Nadin na Mojtaba, zai iya jawo fushin shugaban Amurka Donald Trump, wanda a ranar Lahadin da ta gabata ya bayyana cewa; ya kamata Washington ta sanya baki a zaben. “Idan bai samu amincewa daga gare mu ba, ba za mu bari zaben ya je ko’ina ba,” kamar yadda ya fada wa kafar yada labarai ta ABC.
Kafin wannan mataki, Isra’ila ta yi barazanar kashe mahaifin Mojtaba, Jagoran Addini Ali Khamenei, a daya daga cikin hare-haren farko da aka kaddamar kan Iran fiye da mako guda da ya gabata.
Rundunar sojin Amurka a ranar Lahadin da ta gabata ta ba da rahoton cewa, wani Ba’amurke wanda shi ne na bakwai, ya mutu sakamakon raunukan da ya samu a harin farko na Iran mako guda da ya wuce, kwana guda bayan da Trump ya jagoranci komawa da gawarwakin wasu shida da suka mutu Amurka.
Hare-haren na Amurka da Isra’ila, sun yi sanadiyyar kashe fararen hula akalla 1,332 na Iran tare da raunata dubban wadanda ba su ji ba, ba su gani ba, a cewar jakadan Iran na Majalisar Dinkin Duniya.
Yayin da Trump ya matsa lamba kan mika wuya ba tare da wani sharadi ba, Mohammad Bagher Kalibaf, kakakin majalisar dokokin Iran, ya ce; Tehran ba ta neman tsagaita bude wuta a yakin, sannan kuma za ta hukunta masu tada kayar baya.
Isra’ila ta ci gaba da kai hare-hare kan wasu manyan jami’an Iran, ciki har da Abolkasem Babaian, wanda aka nada kwanan nan a ofishin soji na babban jagoran, yana mai cewa; an kashe shi ne a wani harin da ta kai ranar Asabar. (Reuters)
Wasu sabbin hare-hare guda biyu da Isra’ila ta kai cikin dare, sun shafi wuraren da ake jibge man fetur a ciki da wajen Tehran da kuma wani harin da aka kai a wani otal da ke tsakiyar Beirut babban birnin kasar Lebanon, wanda aka kai kan wasu da ake zargin kwamandojin Iran ne.
Jiragen saman yakin, sun kai harin ne kan wasu cibiyoyin man fetur guda biyar a ciki da wajen babban birnin Iran, inda suka kashe akalla mutum hudu, a cewar wani jami’in mai na kasar.
Gwamnan Tehran, ya shaida wa kamfanin dillancin labarai na IRNA cewa; “an dakatar da rarraba mai na dan wani lokaci” a babban birnin kasar.
Wani duhu ne ya mamaye birnin mai dauke da mutane kimanin miliyan 10, wanda ya toshe rana, kuma warin man fetur ya jima yana bin iska.
Har ila yau, hukumomin kasar sun yi gargadin cewa; hayakin na iya kasancewa mai dauke da guba tare da yin kira ga ‘yan kasar da su kasance sun zauna a gida, amma duk da haka, karfin fashe-fashen ya fasa tare da lalata tagogi da dama.
“Fiye da sa’o’i 12 da gobarar ta ci gaba da ci, iskar ta ci gaba da gurbata da ta kai har ba ma iya yin numfashi ba. Kazalika, babu mai iya fita don yin sayayya ta yau da kullum,” in ji wani dan shekara 35 daga Tehran.
“Da farko, na goyi bayan wannan yakin, bayan mutuwar Khamenei, inda muka yi biki tare da abokaina, muka sha ruwan inabi, muka kuma yi rawa.
“Amma tun jiya mutane suke cewa, babu ko da dan kadan na man fetur da ya rage a gidajen mai,” in ji ta a cikin sakon tes zuwa Turai.
Yayin da yakin ya tsawaita a kwana na tara, dakarun kare juyin juya halin Musulunci na Iran sun ce; suna da isassun kayayyakin da za su ci gaba da yakin da suke yi da makamai masu linzami a Gabas ta Tsakiya, har na tsawon wata shida.
An ji karar fashewar wasu abubuwa a cibiyar kasuwanci ta Isra’ila, Tel Abib, bayan da sojojin Isra’ila suka ce; sun gano wani makami mai linzami daga Iran. Hukumar bayar da agajin gaggawa ta Magen Dabid Adom ta ce, mutum shida sun jikkata a tsakiyar birnin Isra’ila.
[ad_2]
Source link