AFCON 2026: Nijeriya Ta Ƙare A Matsayi Na Ɗaya A Rukunin C
[ad_1]
Daga Rabilu Sanusi Bena
Tawagar Super Eagles ta Nijeriya ta zama kasa ta farko a gasar nahiyar kasashen Afirika ta bana da ta samu nasara a dukkan wasanni 3 da ta buga a matakin rukuni bayan lallasa kasar Uganda da ci 3-1 a wasansu na yau Talata.
Nijeriya ta hada maki 9 da kwallo 4 a wasanni 3 da ta buga, hakan yasa ta kare a matsayi na 1 a rukunin C na gasar, kasar Tunisia ce ke matsayi na 2 da maki 4 sai Tanzania da ta samu maki 2 a matsayi na 3 sannan kasar Uganda da ta kare a matsayi na 4 kuma na karshe da maki 1 kacal.
Paul Onuachu ne ya zurawa Nijeriya kwallonta ta farko a minti na 28 da fara wasa, bayan dawowa daga hutun rabin lokaci ne Raphael Onyedika ya zura kwallaye 2 rigis, wanda yayi sanadiyar samun nasarar Super Eagles din.
Yanzu Nijeriya za ta jira a kammala wasannin rukuni kafin ta san kasar da zata hadu da ita a zagayen 16 na sili daya kwale, Super Eagles na fatan lashe wannan gasar ta bana domin huce haushin rashin nasarar da sukayi a hannun Ivory Coast a wasan karshe na gasar na shekarar 2023.
[ad_2]
Source link