Osimhen ba zai halarci bikin karrama gwarzon ɗan ƙwallon Afirka na bana ba

[ad_1]



Fitaccen ɗan wasan gaba na Najeriya da ke taka leda a ƙungiyar Galatasaray ta Turkiyya, Victor Osimhen, ba zai halarci bikin karrama gwarazan ‘yan wasan Afirka na 2025 ba.

Osimhen, wanda ya lashe kyautar gwarzon ɗan wasan Afirka a 2023, ya bayyana cewa ya koma Turkiyya ne domin duba lafiyarsa, bayan raunin da ya samu a wasan da Jamhuriyar Dimokuraɗiyyar Kongo ta doke Najeriya.

A yau Laraba ne Hukumar Ƙwallon Ƙafa ta Afirka (CAF) za ta sanar da sunayen gwarazan ‘yan wasan nahiyar na shekarar 2025, a yayin babban bikin da za a gudanar a Morocco.

Za a bayyana gwarazan a rukuni-rukuni daban-daban: maza da mata, masu horarwa, ƙungiyoyi, tawagar ƙasashe, da kuma matasan ‘yan wasa masu tasowa.

Za a fara bikin ne da misalin ƙarfe 7:00 na yamma agogon Morocco da Najeriya, a jami’ar Mohammed VI Polytechnic University (UM6P) da ke Rabat, babban birnin ƙasar.


[ad_2]

Source link

Similar Posts

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *