2027: ADC Na Duba Yiwuwar Fitar Da Dan Takarar Shugaban Kasa Ta Hanyar Yarjejeniya — Kakakin Jam’iyya

[ad_1]

Jam’iyyar ADC ta ce tana la’akari da karbar hanyar da kowa zai amince da ita wajen zaben dan takararta na shugaban kasa a 2027.

Sakataren yada labarai na jam’iyyar, Bolaji Abdullahi, ya bayyana hakan a wani shiri na gidan talabijin na Arise TB, a ranar Asabar.

  • Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan PDP A Kaduna, Ashiru, Zai Koma ADC A Ranar Lahadi
  • CBN Ya Ɗage Tsarin Dijital, Zai Biya Mahajjata Kuɗin Guzurinsu A Hannu

Ya ce jam’iyyar na da zabin yin zaben fitar da gwai kai tsaye ko bin hanyar yarjejeniya wajen zaben wanda zai tsaya mata takara a zaben shugaban kasa. Ya kara da cewa zabukan fid da gwani ba su kasance ‘a tebur’ ba bisa ga dokar zabe da aka gyara.

A cewarsa, zabin yin yarjejeniya ita ce kadai hanyar zabin da aka fi so, saboda tana da sauki wajen kashe kudade.

“Muna kokarin gwadawa gwargwadon ikomu ta rungumar hanyar yarjejeiya, saboda wannan shi ne mafi karancin kudi a garemu. A bangarenmu kuma, mafi kyawun yanayi shi ne samun damar tsara yarjejeiyar, kuma wannan ne abin da muke aiki a kai,” in ji shi.

Abdullahi ya kuma soki jam’iyyar APC mai mulki, yana jayayya cewa hadin kan jam’iyyar tana da alaka da shugabancinta a yanzu.

“Idan ka cire iko daga APC, APC ba komai ba ne a zahiri. Na san jam’iyyar sosai.

“Bayan Bola Tinubu, za su rushe cikin sauri, har ma da kansu za su yi mamaki. Shi ne kadai mai rike jam’iyyar gaba daya,” in ji shi.

Ya bayyana APC a matsayin mota ta musamman da aka kirkira don kawo shugabancin, Marigayi Muhammadu Buhari da Tinubu, yana kara da cewa jam’iyyar ta cika wannan manufa gaba daya.

Mai magana da yawun ADC ya kara zargin cewa jam’iyyar mai mulki tana nuna alamun damuwa gabanin zaben da ke tafe.

“A kowace sahihin zabe mai cike da adalci a Nijeriya a yau, babu yadda APC za ta ci zabe.

“Me ya sa jam’iyya mai gwamnonin 31 da kusan kashi 90 cikin dari na ‘yan majalisar kasa ke ci gaba da firgita? Me ya sa har yanzu suke kokarin Sanya wa sauran jam’iyyu masu adawa cikin tashin hankali?

“Ya kamata su kasance suna shirin nasarar Tinubu, la’akari da iko mai yawa da suke da shi. Amma ba su kwantar da hankalinsu ba saboda sun san a zaben da ya kasance mai kyauta kuma mai adalci, ba za su iya samun nasara ba. ‘Yan Nijeriya sun gaji da su,” in ji shi.

Wannan mataki ya zo ne yayin da ADC, wacce ta sanya kanta a matsayin babban jam’iyyar adawa da ta hada fitattun ‘yan siyasa.

Cikin masu neman tikiti takarar shugaba kasa a zaben 2027, akwai tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar da tsohon gwamnan Anambra, Peter Obi, da tsohon ministan sufuri, Rotimi Amaechi, da sauransu.

Sai dai kuma babu sanarwa a hukumance game da takamaiman ‘yan takara.

TATTALIN ARZIKI

[ad_2]

Source link

Similar Posts

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *