Zulum Ya Raba Motocin Sintiri 63 Don Yaki da Laifuffuka A Maiduguri

[ad_1]



Zulum Ya Raba Motocin Sintiri 63 Don Yaki da Laifuffuka A Maiduguri

Gwamnan Jihar Borno, Babagana Umara Zulum,  ya mika motocin sintiri 63 ga hukumomin tsaro da kuma Rundunar Hadin Gwiwa ta Farar Hula (CJTF) da ke aiki a Maiduguri da kewaye.

Daga cikin motocin 63, an ba da motocin 30 ga sassa daban-daban na Sibiliyan JTF, 16 ga Jami’an tsaron kai daukin gaggawa don dakile masu aikata laifukan cin Zarafi, 10 ga kungiyoyin tsaro, 6 ga mafarauta da kuma daya ga jami’an Hukumar Kula da Fataucin Mutane (NAPTIP).

Rarraba motocin yana da nufin inganta karfin yin sintiri da mayar da martanin gaggawa musamman ga ‘yan sanda, sauran jami’an tsaro, da rundunar hadin gwiwa ta farar hula wajen magance barazanar tsaro kamar kungiyoyin ‘yan daba da sauran nau’ikan laifuka a cikin babban birnin jihar da kewaye.

Wannan gudummawar na daya daga cikin rarraba motocin da gwamnatin Zulum ta yi tun 2019, wadanda duk an yi niyya ne don karfafa tsarin tsaro da kare rayuka da dukiyoyin al’umma.

Yayin da yake gabatar da motocin, Gwamna Zulum ya sake nanata kudirin gwamnatinsa na samar da ci gaba da tallafawa jami’an tsaro.

Ya jaddada cewa tsaro wani vangare ne na muhimman abubuwan da gwamnatinsa ta sa a gaba.

Ya ce, “muna nan a ci gaba da kokarinmu na tallafa wa jami’an tsaro a Jihar Borno da kayan aikin da ake bukata domin su yi aiki yadda ya kamata.

“Ina so in tabbatar muku da cewa gwamnatin Borno a karkashin jagorancina za ta ci gaba da tallafa muku da nufin cimma kyawawan manufofi na tabbatar da cewa jihar ta kawar da ta’addanci,” in ji gwamnan.

Zulum ya kuma yaba wa Shugaban Qasa Bola Ahmed Tinubu da jami’an tsaro kan kokarinsu na dawo da zaman lafiya a Borno.

Ya ce, “bari in yi amfani da wannan damar don mika godiyata ga Shugaban Kasa kuma Babban Kwamandan Sojojin Nijeriya, Shugaba Bola Ahmed Tunibu da shugabannin ayyuka da Kwamandan Rundunar OPHK da kwamandojin sashe da dukkan jami’ai da ma’aikatan rundunar sojin Nijeriya da ke aiki don hada kan al’umma da kuma dukkan kungiyoyin ‘yan sanda a Jihar Borno saboda manyan ayyukan da suke yi a jihar.”

Taron ya samu halartar Mataimakin Gwamnan Jihar Borno, Dakta Umar Usman Kadafur da Sakataren Gwamnatin Jihar Borno, Bukar Tijani da Kwamishinan ‘Yan Sanda na Jihar Borno, Naziru Abdulmajid da Daraktan Hukumar Tsaro ta Jiha, Adamu Umar da Kwamandan Rundunar Tsaron Farar Hula ta Nijeriya, Abdulrazak Haroon da sauran sassan Jami’an tsaro.


[ad_2]

Source link

Similar Posts

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *