Ɗan Majalisar NNPP Ɗaya Tilo A Bauchi Ya Sauya Sheƙa Zuwa APC


Ɗan Majalisar Dokokin Jihar Bauchi mai wakiltar Ƙaramar Hukumar Jama’are, Mubarak Haruna Mai Raƙumi, ya sauya sheƙa daga jam’iyyar NNPP zuwa jam’iyyar APC.

An sanar da sauyin sheƙar ne a yayin wani taron da aka gudanar a ranar Lahadi, 1 ga watan Fabrairu, 2026, inda Mai Rakumi ya zama ɗan majalisa ɗaya tilo daga NNPP a Majalisar Dokokin Jihar Bauchi da ya koma APC, lamarin da ya jawo hankalin manyan ƴan siyasa da magoya bayan jam’iyyun a jihar.

  • Gwamnatin Bauchi Za Ta Haramta Haihuwa Ba A Asibiti Ba
  • Hotuna: Babbar Mota Ta Hallaka Wata Bafulatana A Bauchi

A jawabinsa, ɗan majalisar ya gode wa Gwamnan Jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, bisa goyon baya da gudummawar da ya ce ya samu daga wajensa a tsawon lokacin da ya shafe a siyasa. Ya bayyana cewa sauyin shekar da ya yi ya biyo bayan nazari da shawara da manyan jiga-jigan mazaɓarsa, domin inganta walwalar al’ummarsa da kuma ci gaban jihar Bauchi gaba ɗaya.

Masu sharhi kan harkokin siyasa na ganin cewa wannan mataki na Mai Rakumi na zuwa ne a daidai lokacin da ake samun sauye-sauyen siyasa a faɗin ƙasar nan, musamman yayin da jam’iyyun ke ƙoƙarin ƙarfafa kansu gabanin babban zaɓen shekarar 2027.



Source link

Similar Posts

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *